< 2 Tarihi 28 >

1 Ahaz yana da shekara ashirin sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara goma sha shida. Ba kamar Dawuda kakansa ba, bai yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji ba.
Achaz était âgé de vingt ans quand il devint roi, et il régna seize ans à Jérusalem. Il ne fit point ce qui est droit aux y eux de l'Éternel, comme David, son père.
2 Ya yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila ya kuma yi zubin gumaka domin a bauta wa Ba’al.
Il suivit la voie des rois d'Israël; et il fit même des images de fonte pour les Baals.
3 Ya ƙone hadayu a Kwarin Ben Hinnom, ya kuma miƙa’ya’yansa maza a cikin wuta, yana bin hanyoyi banƙyama na al’umman da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.
Il fit des encensements dans la vallée du fils de Hinnom, et il brûla ses fils au feu, selon les abominations des nations que l'Éternel avait chassées devant les enfants d'Israël.
4 Ya miƙa hadayu, ya kuma ƙone turare a masujadan kan tudu, a bisa tuddai da kuma ƙarƙashin kowane itace mai inuwa.
Il sacrifiait aussi et faisait des encensements dans les hauts lieux, sur les collines, et sous tout arbre verdoyant.
5 Saboda haka Ubangiji Allahnsa ya miƙa shi ga sarkin Aram. Arameyawa suka ci shi a yaƙi, suka kuma kwashe mutanensa da yawa a matsayin’yan kurkuku, suka kawo Damaskus. Ya kuma ba da shi ga sarkin Isra’ila, wanda ya jijji masa a yaƙi.
Et l'Éternel son Dieu le livra entre les mains du roi de Syrie; et les Syriens le battirent et lui prirent un grand nombre de prisonniers, qu'ils emmenèrent à Damas. Il fut aussi livré entre les mains du roi d'Israël, qui lui fit essuyer une grande défaite.
6 A rana ɗaya Feka ɗan Remaliya ya kashe sojoji dubu ɗari da dubu ashirin a Yahuda, domin Yahuda sun yashe Ubangiji Allah na kakanninsu.
Car Pékach, fils de Rémalia, tua en un seul jour, en Juda, cent vingt mille hommes, tous vaillants hommes, parce qu'ils avaient abandonné l'Éternel, le Dieu de leurs pères.
7 Zikri, wani jarumin Efraim, ya kashe Ma’asehiya ɗan sarki, Azrikam hafsa mai lura da fada, da kuma Elkana, mataimakin sarki.
Et Zicri, homme vaillant d'Éphraïm, tua Maaséja, fils du roi, et Azrikam, qui avait la conduite de la maison, et Elkana, le second après le roi.
8 Isra’ilawa suka kame kamammu daga’yan’uwansu mata,’ya’ya maza da kuma’ya’ya mata dubu ɗari biyu. Suka kuma kwashe ganima mai yawan gaske, waɗanda suka kwasa zuwa Samariya.
Et les enfants d'Israël emmenèrent prisonniers, deux cent mille de leurs frères, tant femmes que fils et filles; ils firent aussi sur eux un grand butin, et ils emmenèrent le butin à Samarie.
9 Amma wani annabin Ubangiji mai suna Oded yana a can, sai ya fito don yă sadu da mayaƙa sa’ad da suke komowa zuwa Samariya. Ya ce musu, “Domin Ubangiji Allah na kakanninku yana fushi da Yahuda, ya ba da su cikin hannunku. Sai kuka kashe su cikin fushin da ya kai sama.
Or un prophète de l'Éternel, nommé Oded, était là; il sortit au-devant de cette armée, qui revenait à Samarie, et leur dit: Voici, l'Éternel, le Dieu de vos pères, étant indigné contre Juda, les a livrés entre vos mains, et vous les avez tués avec une fureur qui est parvenue jusqu'aux cieux.
10 Yanzu kuma kuna niyya ku mai da maza da matan Yahuda da Urushalima bayinku. Amma ku ɗin ba ku da laifin zunubi ga Ubangiji Allahnku ne?
Et maintenant, vous prétendez vous assujettir, pour serviteurs et pour servantes, les enfants de Juda et de Jérusalem! Mais n'est-ce pas vous, surtout, qui êtes coupables envers l'Éternel, votre Dieu?
11 To, ku saurare ni! Ku mai da’yan’uwanku da kuka kama a matsayin’yan kurkuku, gama fushin Ubangiji yana a kanku.”
Maintenant écoutez-moi, et remmenez les prisonniers que vous avez faits parmi vos frères; car l'ardeur de la colère de l'Éternel est sur vous.
12 Sai waɗansu shugabanni a Efraim, Azariya ɗan Yehohanan, Berekiya ɗan Meshillemot, Hezekiya ɗan Shallum da Amasa ɗan Hadlai, suka tasar wa waɗanda suke isowa daga yaƙi.
Alors quelques-uns des chefs des enfants d'Éphraïm, Azaria, fils de Jochanan, Bérékia, fils de Meshillémoth, Ézéchias, fils de Shallum, et Amasa, fils de Hadlaï, s'élevèrent contre ceux qui revenaient de l'armée,
13 Suka ce, “Dole ku kawo waɗannan’yan kurkukun a nan, ko kuwa za ku yi laifi a gaban Ubangiji. Kuna niyya ku ƙara ga zunubinmu da kuma laifinmu? Gama laifinmu ya riga ya yi yawa, kuma fushinsa mai tsanani yana a kan Isra’ila.”
Et leur dirent: Vous ne ferez point entrer ici ces prisonniers; car, pour nous rendre coupables devant l'Éternel, vous voulez ajouter à nos péchés et à notre culpabilité; car nous sommes déjà très coupables, et l'ardeur de la colère est sur Israël.
14 Saboda haka sojoji suka ba da’yan kurkukun da ganima a gaban hafsoshi da dukan taron.
Alors les soldats abandonnèrent les prisonniers et le butin devant les chefs et devant toute l'assemblée.
15 Sai mutanen da aka kira sunansu suka tashi, suka ɗauki kamammun, da ganimar, suka sa wa dukan waɗanda suke tsirara sutura. Suka sa musu sutura, suka ba su takalma, suka ba su abinci da abin sha, suka shafa musu mai. Suka hawar da dukan raunana a kan jakuna, suka kai su wurin’yan’uwansu a Yeriko, wato, Birnin Itatuwan Dabino, sa’an nan suka koma Samariya.
Et ces hommes, qui ont été désignés par leurs noms, se levèrent, prirent les prisonniers, et vêtirent, au moyen du butin, tous ceux d'entre eux qui étaient nus; ils les vêtirent, ils les chaussèrent; ils leur donnèrent à manger et à boire; ils les oignirent, et ils conduisirent sur des ânes tous ceux qui ne pouvaient pas se soutenir, et les menèrent à Jérico, la ville des palmiers, auprès de leurs frères; puis ils s'en retournèrent à Samarie.
16 A lokacin nan Sarki Ahaz ya aika wurin sarkin Assuriya neman taimako.
En ce temps-là, le roi Achaz envoya vers les rois d'Assyrie, afin qu'ils lui donnassent du secours.
17 Mutanen Edom sun sāke zuwa suka yaƙi Yahuda suka kuma kwashe’yan kurkuku,
Les Édomites étaient encore venus, avaient battu Juda, et emmené des prisonniers.
18 yayinda Filistiyawa suka kai hari wa garuruwa a gindin tuddai da kuma a Negeb na Yahuda. Suka kame su suka kuma zauna a Bet-Shemesh, Aiyalon da Gederot, haka ma Soko, Timna da Gimzo tare da ƙauyuka kewayensu.
Les Philistins s'étaient aussi jetés sur les villes de la plaine et du midi de Juda; et ils avaient pris Beth-Shémèsh, Ajalon, Guédéroth, Soco et les villes de son ressort, Thimna et les villes de son ressort, Guimzo et les villes de son ressort, et ils y habitaient.
19 Ubangiji ya ƙasƙantar da Yahuda saboda Ahaz sarkin Isra’ila, gama ya hadasa mugunta a Yahuda kuma ya kasance marar aminci ga Ubangiji.
Car l'Éternel avait abaissé Juda, à cause d'Achaz, roi d'Israël, parce qu'il avait relâché tout frein en Juda, et qu'il avait grandement péché contre l'Éternel.
20 Tiglat-Fileser sarkin Assuriya ya zo wurinsa, sai ya wahalar da sarki Ahaz maimakon taimakonsa.
Or Thilgath-Pilnéser, roi d'Assyrie, vint vers lui; mais il l'opprima, bien loin de le fortifier.
21 Ahaz ya ɗauki waɗansu abubuwa daga haikalin Ubangiji da kuma daga fadan sarki da kuma daga sarakuna, ya ba da su ga sarkin Assuriya, amma wannan bai taimake shi ba.
Car Achaz dépouilla la maison de l'Éternel, la maison du roi et celle des principaux du peuple, pour faire des présents au roi d'Assyrie, mais sans en retirer secours.
22 Cikin lokacin wahalarsa Sarki Ahaz ya ƙara zama marar aminci ga Ubangiji.
Et dans le temps de sa détresse, il continua à pécher contre l'Éternel. C'était toujours le roi Achaz.
23 Ya miƙa hadayu ga allolin Damaskus, waɗanda suka ci shi a yaƙi; gama ya yi tunani, “Da yake allolin sarakunan Aram sun taimake su, zan miƙa hadayu domin su taimake ni.” Amma suka zama sanadin fāɗuwarsa da kuma fāɗuwar dukan Isra’ila.
Il sacrifia aux dieux de Damas qui l'avaient frappé, et il dit: Puisque les dieux des rois de Syrie leur viennent en aide, je leur sacrifierai, afin qu'ils me soient en aide. Mais ils furent cause de sa chute et de celle de tout Israël.
24 Ahaz ya tattara kayayyaki daga haikalin Allah ya kwashe su. Ya kulle ƙofofin haikalin Ubangiji ya kakkafa bagadai a kowace kusurwa a titin Urushalima.
Or Achaz rassembla les vases de la maison de Dieu, et il mit en pièces les vases de la maison de Dieu. Il ferma les portes de la maison de l'Éternel, et se fit des autels dans tous les coins de Jérusalem.
25 A kowane gari a Yahuda, ya gina masujadan kan tudu don ƙone hadayu ga waɗansu alloli, ya kuma tsokane Ubangiji Allah na kakanninsa ya yi fushi.
Et il fit des hauts lieux dans chaque ville de Juda, pour faire des encensements à d'autres dieux; et il irrita l'Éternel, le Dieu de ses pères.
26 Sauran ayyukan mulkinsa da dukan hanyoyinsa, daga farko zuwa ƙarshe, suna a rubuce a littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
Quant au reste de ses actions, et de toutes ses voies, les premières et les dernières, voici, elles sont écrites dans le livre des rois de Juda et d'Israël.
27 Ahaz ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a birnin Urushalima, amma ba a sa shi a makabartan sarakunan Isra’ila ba. Sai Hezekiya ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Puis Achaz s'endormit avec ses pères, et on l'ensevelit dans la cité, à Jérusalem; car on ne le mit point dans les tombeaux des rois d'Israël; et Ézéchias, son fils, régna à sa place.

< 2 Tarihi 28 >