< 2 Tarihi 26 >

1 Sai dukan mutanen Yahuda suka ɗauki Uzziya wanda yake da shekara goma sha shida da haihuwa, suka naɗa shi sarki a madadin mahaifinsa Amaziya.
Yahuda halkı Amatsya'nın yerine on altı yaşındaki oğlu Uzziya'yı kral yaptı.
2 Shi ne wanda ya sāke gina Elot ya kuma mai da shi ga Yahuda bayan Amaziya ya huta tare da kakanninsa.
Babası Amatsya ölüp atalarına kavuştuktan sonra Uzziya Eylat Kenti'ni onarıp Yahuda topraklarına kattı.
3 Uzziya yana da shekara goma sha shida sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara hamsin da biyu. Sunan mahaifiyarsa Yekoliya ce; ita daga Urushalima ce.
Uzziya on altı yaşında kral oldu ve Yeruşalim'de elli iki yıl krallık yaptı. Annesi Yeruşalimli Yekolya'ydı.
4 Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar dai yadda mahaifinsa Amaziya ya yi.
Babası Amatsya gibi, Uzziya da RAB'bin gözünde doğru olanı yaptı.
5 Ya nemi Allah a kwanakin Zakariya, wanda ya koyar da shi a tsoron Allah. Muddin ya nemi Ubangiji, Allah ya ba shi nasara.
Kendisine Tanrı korkusunu öğreten Zekeriya'nın günlerinde Tanrı'ya yöneldi. RAB'be yöneldiği sürece Tanrı onu başarılı kıldı.
6 Ya yi yaƙi da Filistiyawa ya kuma rushe katangar Gat, Yabne da kuma Ashdod. Sa’an nan ya sāke gina garuruwa kusa da Ashdod da sauran wurare a cikin Filistiyawa.
Uzziya Filistliler'e savaş açtı. Gat, Yavne ve Aşdot'un surlarını yıktırdı. Sonra Aşdot yakınlarında ve Filist bölgesinde kentler kurdu.
7 Allah ya taimake shi a kan Filistiyawa da kuma a kan Larabawa waɗanda suke zama a Gur-Ba’al da kuma a kan Meyunawa.
Filistliler'e, Gur-Baal'da yaşayan Araplar'a ve Meunlular'a karşı Tanrı ona yardım etti.
8 Ammonawa suka kawo haraji wa Uzziya, sunan da ya yi kuwa ya bazu har iyakar Masar, domin ya zama mai iko sosai.
Ammonlular Uzziya'ya haraç vermeye başladılar. Gitgide güçlenen Uzziya'nın ünü Mısır sınırına dek ulaştı.
9 Uzziya ya gina hasumiyoyi a Urushalima a Ƙofar Kusurwa, a Ƙofar Kwari da kuma a kusurwar katanga, ya kuma yi musu katanga.
Uzziya Yeruşalim'de Köşe Kapısı, Dere Kapısı ve surun köşesi üzerinde kuleler kurup bunları sağlamlaştırdı.
10 Ya gina hasumiyoyi a hamada ya kuma haƙa rijiyoyi masu yawa, gama yana da dabbobi masu yawa a gindin duwatsu da kuma a kwari. Yana da mutane masu yin masa aiki a gonakinsa da gonakin inabinsa a tuddai da kuma a ƙasashe masu dausayi, gama yana son noma.
Şefela'da ve ovada çok sayıda hayvanı olduğundan, kırda gözetleme kuleleri yaptırarak birçok sarnıç açtırdı. Dağlık bölgelerde, verimli topraklarda da ırgatları, bağcıları vardı; çünkü toprağı severdi.
11 Uzziya ya kasance da gogaggun mayaƙa, a shirye su fito ɓangarori-ɓangarori bisa ga yawansu yadda Yehiyel magatakarda, da Ma’asehiya jarumi, suka karkasa su bisa ga umarnin Hananiya, ɗaya daga cikin fadawa.
Uzziya'nın savaşa hazır bir ordusu vardı. Kralın komutanlarından Hananya'nın denetiminde Yazman Yeiel'le görevli Maaseya'nın yaptığı sayımın sonuçlarına göre, bu ordu bölük bölük savaşa girerdi.
12 Yawan shugabannin iyali a bisa jarumawa sun kai 2,600.
Yiğit savaşçıları yöneten boy başlarının sayısı 2 600'dü.
13 A ƙarƙashin shugabancinsu akwai mayaƙa 307,500 horarru don yaƙi, mayaƙa masu ƙarfi don su taimaki sarki a kan abokan gābansa.
Bunların komutası altında krala yardım etmek için düşmanla yiğitçe savaşacak 307 500 askerden oluşan bir ordu vardı.
14 Uzziya ya tanada garkuwoyi, māsu, hulunan kwano, kayan sulke, baka da majajjawa don mayaƙan gaba ɗaya.
Uzziya bütün ordu için kalkan, mızrak, miğfer, zırh, yay, sapan taşı sağladı.
15 A Urushalima ya yi na’urori da gwanaye suka sarrafa don amfani a hasumiyoyi da kuma a kusurwar kāriya don harbin kibiyoyi da jefan manyan duwatsu. Sunansa ya bazu ko’ina, gama ya sami taimako sosai har ya zama mai iko.
Yeruşalim'de becerikli adamlarca tasarlanmış gereçler yaptırdı. Okları, büyük taşları fırlatmak için bu gereçleri kulelere ve köşelere yerleştirdi. Uzziya'nın ünü uzaklara kadar yayıldı; çünkü gördüğü olağanüstü yardım sayesinde büyük güce kavuşmuştu.
16 Amma bayan Uzziya ya zama mai iko, sai ɗaga kai ya kai shi ga fāɗuwa. Bai yi aminci ga Ubangiji Allahnsa ba, ya kuma shiga haikalin Ubangiji don yă ƙone turare a bagaden turare.
Ne var ki, güçlenince kendisini yıkıma sürükleyecek bir gurura kapıldı. Tanrısı RAB'be ihanet etti. Buhur sunağı üzerinde buhur yakmak için RAB'bin Tapınağı'na girdi.
17 Azariya firist tare da waɗansu firistoci tamanin na Ubangiji masu ƙarfin hali suka bi shi ciki.
Kâhin Azarya ile RAB'bin yürekli seksen kâhini de ardısıra tapınağa girdiler.
18 Suka kalubalance shi suka ce, “Ba daidai ba ne, Uzziya, ka ƙone turare ga Ubangiji. Wannan aikin firistoci zuriyar Haruna ne, waɗanda aka tsarkake don ƙone turare. Ka bar wuri mai tsarki, gama ka kasance marar aminci; kuma Ubangiji Allah ba zai girmama ka ba.”
Kral Uzziya'ya karşı durarak, “Ey Uzziya, RAB'be buhur yakmaya hakkın yok!” dediler, “Ancak Harun soyundan kutsanmış kâhinler buhur yakabilir. Tapınaktan çık! Çünkü sen RAB'be ihanet ettin; RAB Tanrı da seni onurlandırmayacak!”
19 Uzziya wanda yake da farantin wuta a hannunsa a shirye don ƙone turare, ya husata. Yayinda yake fushi da firistocin a gabansu a gaban bagaden turare a haikalin Ubangiji, sai kuturta ta faso a goshinsa.
Buhur yakmak için elinde buhurdan tutan Uzziya kâhinlere öfkelendi. Öfkelenir öfkelenmez de kâhinlerin önünde, RAB'bin Tapınağı'ndaki buhur sunağının yanında duran Uzziya'nın alnında deri hastalığı belirdi.
20 Sa’ad da Azariya babban firist da dukan sauran firistoci suka dube shi, sai suka ga cewa yana da kuturta a goshinsa, saboda haka suka gaggauta tunkuɗa shi waje nan da nan. Tabbatacce, shi kansa ma ya yi marmari yă bar wurin domin Ubangiji ya buge shi.
Başkâhin Azarya ile öbür kâhinler ona bakınca alnında deri hastalığı belirdiğini gördüler. Onu çabucak oradan çıkardılar. Uzziya da çıkmaya istekliydi, çünkü RAB onu cezalandırmıştı.
21 Sarki Uzziya ya kasance da kuturta har ranar mutuwarsa. Ya zauna a gidan da aka ware, da kuturci, aka kuma ware shi daga haikalin Ubangiji. Yotam ɗansa ya lura da fadan ya kuma yi mulkin mutanen ƙasar.
Kral Uzziya ölünceye kadar deri hastalığından kurtulamadı. Bu yüzden ayrı bir evde yaşadı ve RAB'bin Tapınağı'na sokulmadı. Sarayı ve ülke halkını oğlu Yotam yönetti.
22 Sauran ayyukan mulkin Uzziya daga farko zuwa ƙarshe, suna a rubuce ta hannun annabi Ishaya ɗan Amoz.
Uzziya'nın yaptığı öbür işleri, başından sonuna dek, Amots oğlu Peygamber Yeşaya yazmıştır.
23 Uzziya ya huta da kakanninsa aka kuma binne shi kusa da su a fili don binnewar da take ta sarakuna, domin mutane sun ce, “Yana da kuturta.” Sai Yotam ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Uzziya ölüp atalarına kavuşunca, deri hastalığına yakalandığı için onu atalarının yanına, kral mezarlığının ayrı bir yerine gömdüler. Yerine oğlu Yotam kral oldu.

< 2 Tarihi 26 >