< 2 Tarihi 26 >
1 Sai dukan mutanen Yahuda suka ɗauki Uzziya wanda yake da shekara goma sha shida da haihuwa, suka naɗa shi sarki a madadin mahaifinsa Amaziya.
Tout le peuple de la terre prit alors Ozias, qui avait seize ans, et ils le proclamèrent roi à la place d'Amasias, son père.
2 Shi ne wanda ya sāke gina Elot ya kuma mai da shi ga Yahuda bayan Amaziya ya huta tare da kakanninsa.
Il rebâtit Elath, et la rendit à Juda lorsque le roi se fut endormi avec ses pères.
3 Uzziya yana da shekara goma sha shida sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara hamsin da biyu. Sunan mahaifiyarsa Yekoliya ce; ita daga Urushalima ce.
Ozias avait seize ans quand il monta sur le trône, et il régna cinquante- deux ans à Jérusalem; sa mère s'appelait Jéchélie de Jérusalem.
4 Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar dai yadda mahaifinsa Amaziya ya yi.
Et il fit ce qui est droit devant le Seigneur, comme avait fait d'abord Amasias, son père.
5 Ya nemi Allah a kwanakin Zakariya, wanda ya koyar da shi a tsoron Allah. Muddin ya nemi Ubangiji, Allah ya ba shi nasara.
Il chercha le Seigneur tant que vécut Zacharie, homme sage et craignant Dieu; tant qu'il vécut, Ozias chercha le Seigneur, et le Seigneur le fit prospérer.
6 Ya yi yaƙi da Filistiyawa ya kuma rushe katangar Gat, Yabne da kuma Ashdod. Sa’an nan ya sāke gina garuruwa kusa da Ashdod da sauran wurare a cikin Filistiyawa.
Il se mit en campagne, combattit les Philistins, renversa les murs de Geth, les murs de Jabner, les murs d'Azot, et bâtit des villes, près d'Azot, sur la terre des étrangers.
7 Allah ya taimake shi a kan Filistiyawa da kuma a kan Larabawa waɗanda suke zama a Gur-Ba’al da kuma a kan Meyunawa.
Et le Seigneur le fortifia contre les Philistins, contre les Arabes qui habitent au milieu des rochers, et contre les Minéens.
8 Ammonawa suka kawo haraji wa Uzziya, sunan da ya yi kuwa ya bazu har iyakar Masar, domin ya zama mai iko sosai.
Alors, les Minéens lui firent des présents, et son nom se répandit jusqu'à l'entrée de l'Égypte; car il se fortifia extrêmement.
9 Uzziya ya gina hasumiyoyi a Urushalima a Ƙofar Kusurwa, a Ƙofar Kwari da kuma a kusurwar katanga, ya kuma yi musu katanga.
Ozias bâtit aussi des tours dans Jérusalem: sur la porte de l'Angle, sur la porte de la Vallée, sur les angles, et il les fortifia.
10 Ya gina hasumiyoyi a hamada ya kuma haƙa rijiyoyi masu yawa, gama yana da dabbobi masu yawa a gindin duwatsu da kuma a kwari. Yana da mutane masu yin masa aiki a gonakinsa da gonakin inabinsa a tuddai da kuma a ƙasashe masu dausayi, gama yana son noma.
Et il bâtit des tours dans le désert, et il fit, en pierres de taille, une multitude de citernes, parce qu'il possédait de nombreux troupeaux dans les basses terres et dans la plaine, et il employait beaucoup de vignerons sur la montagne et sur le Carmel, car il était cultivateur.
11 Uzziya ya kasance da gogaggun mayaƙa, a shirye su fito ɓangarori-ɓangarori bisa ga yawansu yadda Yehiyel magatakarda, da Ma’asehiya jarumi, suka karkasa su bisa ga umarnin Hananiya, ɗaya daga cikin fadawa.
Son armée était aguerrie; au dehors, elle se rangeait en bataille; à l'intérieur, elle se déployait pour qu'on en fit la revue; ceux qui la dénombraient étaient le scribe Jehiel, le juge Maasias, et Ananias le lieutenant du roi.
12 Yawan shugabannin iyali a bisa jarumawa sun kai 2,600.
Le nombre des vaillants, chefs de familles, qui allaient en guerre, s'élevait à deux mille deux cents.
13 A ƙarƙashin shugabancinsu akwai mayaƙa 307,500 horarru don yaƙi, mayaƙa masu ƙarfi don su taimaki sarki a kan abokan gābansa.
Et ils commandaient une armée aguerrie de trois cent soixante-dix mille cinq cents hommes, qui marchaient au combat, pleins de force et de vaillance, pour défendre le roi contre ses ennemis.
14 Uzziya ya tanada garkuwoyi, māsu, hulunan kwano, kayan sulke, baka da majajjawa don mayaƙan gaba ɗaya.
Ozias les avait tous armés de longs boucliers, de javelines, de casques, d'arcs et de frondes.
15 A Urushalima ya yi na’urori da gwanaye suka sarrafa don amfani a hasumiyoyi da kuma a kusurwar kāriya don harbin kibiyoyi da jefan manyan duwatsu. Sunansa ya bazu ko’ina, gama ya sami taimako sosai har ya zama mai iko.
Et il fit exécuter à Jérusalem des machines, œuvres d'un habile calculateur, pour être sur les tours et sur les angles, ou pour lancer des traits ou de grosses pierres; partout, même au loin, on parla beaucoup de ses engins; car il en était merveilleusement secouru, et en tirait une grande force.
16 Amma bayan Uzziya ya zama mai iko, sai ɗaga kai ya kai shi ga fāɗuwa. Bai yi aminci ga Ubangiji Allahnsa ba, ya kuma shiga haikalin Ubangiji don yă ƙone turare a bagaden turare.
Mais, comme il se fortifiait, son cœur s'enorgueillit pour sa perte; et il pécha contre le Seigneur son Dieu, et il entra dans le temple du Seigneur pour brûler de l'encens sur l'autel des parfums.
17 Azariya firist tare da waɗansu firistoci tamanin na Ubangiji masu ƙarfin hali suka bi shi ciki.
Et Azarias le prêtre y entra sur ses pas, accompagné de quatre-vingts prêtres du Seigneur, hommes intrépides.
18 Suka kalubalance shi suka ce, “Ba daidai ba ne, Uzziya, ka ƙone turare ga Ubangiji. Wannan aikin firistoci zuriyar Haruna ne, waɗanda aka tsarkake don ƙone turare. Ka bar wuri mai tsarki, gama ka kasance marar aminci; kuma Ubangiji Allah ba zai girmama ka ba.”
Et ils s'arrêtèrent devant le roi Ozias, et ils lui dirent: Ce n'est pas à toi, Ozias, d'encenser le Seigneur, mais aux prêtres, fils d'Aaron, qui sont consacrés pour faire les sacrifices. Sors du Saint des saints, car tu t'es séparé du Seigneur, et cela ne tournera pas à ta gloire auprès de Dieu.
19 Uzziya wanda yake da farantin wuta a hannunsa a shirye don ƙone turare, ya husata. Yayinda yake fushi da firistocin a gabansu a gaban bagaden turare a haikalin Ubangiji, sai kuturta ta faso a goshinsa.
Mais Ozias s'irrita; or, il avait à la main l'encensoir pour brûler de l'encens dans le temple, et, pendant qu'il s'irritait contre les prêtres, la lèpre parut sur son front, devant les prêtres dans le temple du Seigneur, au pied de l'autel des parfums.
20 Sa’ad da Azariya babban firist da dukan sauran firistoci suka dube shi, sai suka ga cewa yana da kuturta a goshinsa, saboda haka suka gaggauta tunkuɗa shi waje nan da nan. Tabbatacce, shi kansa ma ya yi marmari yă bar wurin domin Ubangiji ya buge shi.
Et le grand prêtre Azarias et les prêtres, en se retournant vers lui, virent la lèpre sur son front; ils eurent hâte de le faire sortir, et lui-même n'était pas moins empressé, car le Seigneur l'avait châtié.
21 Sarki Uzziya ya kasance da kuturta har ranar mutuwarsa. Ya zauna a gidan da aka ware, da kuturci, aka kuma ware shi daga haikalin Ubangiji. Yotam ɗansa ya lura da fadan ya kuma yi mulkin mutanen ƙasar.
Le roi Ozias resta lépreux jusqu'au jour de sa mort; et lépreux, il demeura dans une maison isolée, parce qu'il avait été retranché du temple du Seigneur. Et Joatham, son fils, fut mis à la tête du royaume, jugeant le peuple de la terre.
22 Sauran ayyukan mulkin Uzziya daga farko zuwa ƙarshe, suna a rubuce ta hannun annabi Ishaya ɗan Amoz.
Le reste des actes d'Ozias, les premiers et les derniers, ont été écrits par le prophète Jessé (Isaïe).
23 Uzziya ya huta da kakanninsa aka kuma binne shi kusa da su a fili don binnewar da take ta sarakuna, domin mutane sun ce, “Yana da kuturta.” Sai Yotam ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Et Ozias s'endormit avec ses pères, et on l'ensevelit auprès d'eux, dans le champ où est le sépulcre des rois, parce que, dirent-ils, il était lépreux. Et Joatham, son fils, régna à sa place.