< 2 Tarihi 26 >

1 Sai dukan mutanen Yahuda suka ɗauki Uzziya wanda yake da shekara goma sha shida da haihuwa, suka naɗa shi sarki a madadin mahaifinsa Amaziya.
Tout le peuple de Juda prit Ozias, qui avait seize ans, et le fit roi à la place de son père Amatsia.
2 Shi ne wanda ya sāke gina Elot ya kuma mai da shi ga Yahuda bayan Amaziya ya huta tare da kakanninsa.
Il bâtit Eloth et la rendit à Juda. Après cela, le roi se coucha avec ses pères.
3 Uzziya yana da shekara goma sha shida sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara hamsin da biyu. Sunan mahaifiyarsa Yekoliya ce; ita daga Urushalima ce.
Ozias avait seize ans lorsqu'il devint roi, et il régna cinquante-deux ans à Jérusalem. Le nom de sa mère était Jechilia, de Jérusalem.
4 Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar dai yadda mahaifinsa Amaziya ya yi.
Il fit ce qui est droit aux yeux de l'Éternel, selon tout ce qu'avait fait son père Amatsia.
5 Ya nemi Allah a kwanakin Zakariya, wanda ya koyar da shi a tsoron Allah. Muddin ya nemi Ubangiji, Allah ya ba shi nasara.
Il se mit à chercher Dieu du temps de Zacharie, qui avait l'intelligence de la vision de Dieu; et tant qu'il chercha Yahvé, Dieu le fit prospérer.
6 Ya yi yaƙi da Filistiyawa ya kuma rushe katangar Gat, Yabne da kuma Ashdod. Sa’an nan ya sāke gina garuruwa kusa da Ashdod da sauran wurare a cikin Filistiyawa.
Il sortit et combattit les Philistins, et il abattit la muraille de Gath, la muraille de Jabné et la muraille d'Asdod; il bâtit des villes dans le pays d'Asdod et chez les Philistins.
7 Allah ya taimake shi a kan Filistiyawa da kuma a kan Larabawa waɗanda suke zama a Gur-Ba’al da kuma a kan Meyunawa.
Dieu le secourut contre les Philistins, contre les Arabes qui habitaient à Gur Baal, et contre les Meunim.
8 Ammonawa suka kawo haraji wa Uzziya, sunan da ya yi kuwa ya bazu har iyakar Masar, domin ya zama mai iko sosai.
Les Ammonites rendirent hommage à Ozias. Son nom se répandit jusqu'à l'entrée de l'Égypte, car il devint extrêmement fort.
9 Uzziya ya gina hasumiyoyi a Urushalima a Ƙofar Kusurwa, a Ƙofar Kwari da kuma a kusurwar katanga, ya kuma yi musu katanga.
Ozias bâtit à Jérusalem des tours à la porte de l'angle, à la porte de la vallée et au tournant de la muraille, et il les fortifia.
10 Ya gina hasumiyoyi a hamada ya kuma haƙa rijiyoyi masu yawa, gama yana da dabbobi masu yawa a gindin duwatsu da kuma a kwari. Yana da mutane masu yin masa aiki a gonakinsa da gonakin inabinsa a tuddai da kuma a ƙasashe masu dausayi, gama yana son noma.
Il construisit des tours dans le désert et creusa de nombreuses citernes, car il avait beaucoup de bétail, tant dans les plaines que dans les vallées. Il avait des fermiers et des vignerons dans les montagnes et dans les champs fertiles, car il aimait l'agriculture.
11 Uzziya ya kasance da gogaggun mayaƙa, a shirye su fito ɓangarori-ɓangarori bisa ga yawansu yadda Yehiyel magatakarda, da Ma’asehiya jarumi, suka karkasa su bisa ga umarnin Hananiya, ɗaya daga cikin fadawa.
Ozias avait aussi une armée de combattants qui allaient à la guerre par bandes, selon le dénombrement fait par le scribe Jeiel et l'officier Maaséja, sous la direction de Hanania, l'un des chefs du roi.
12 Yawan shugabannin iyali a bisa jarumawa sun kai 2,600.
Le nombre total des chefs de famille, des vaillants hommes, était de deux mille six cents.
13 A ƙarƙashin shugabancinsu akwai mayaƙa 307,500 horarru don yaƙi, mayaƙa masu ƙarfi don su taimaki sarki a kan abokan gābansa.
Ils avaient sous leurs ordres une armée de trois cent sept mille cinq cents hommes, qui faisaient la guerre avec une grande puissance, pour aider le roi contre l'ennemi.
14 Uzziya ya tanada garkuwoyi, māsu, hulunan kwano, kayan sulke, baka da majajjawa don mayaƙan gaba ɗaya.
Ozias prépara pour eux, pour toute l'armée, des boucliers, des lances, des casques, des cottes de mailles, des arcs et des pierres pour la fronde.
15 A Urushalima ya yi na’urori da gwanaye suka sarrafa don amfani a hasumiyoyi da kuma a kusurwar kāriya don harbin kibiyoyi da jefan manyan duwatsu. Sunansa ya bazu ko’ina, gama ya sami taimako sosai har ya zama mai iko.
A Jérusalem, il fit installer sur les tours et sur les remparts des dispositifs inventés par des hommes habiles, pour lancer des flèches et de grosses pierres. Son nom se répandit au loin, car il fut merveilleusement aidé jusqu'à ce qu'il devienne fort.
16 Amma bayan Uzziya ya zama mai iko, sai ɗaga kai ya kai shi ga fāɗuwa. Bai yi aminci ga Ubangiji Allahnsa ba, ya kuma shiga haikalin Ubangiji don yă ƙone turare a bagaden turare.
Mais lorsqu'il fut fort, son cœur s'éleva, de sorte qu'il se corrompit et pécha contre l'Éternel, son Dieu, car il entra dans le temple de l'Éternel pour brûler des parfums sur l'autel des parfums.
17 Azariya firist tare da waɗansu firistoci tamanin na Ubangiji masu ƙarfin hali suka bi shi ciki.
Le prêtre Azaria entra après lui, et avec lui quatre-vingts prêtres de Yahvé, qui étaient des hommes vaillants.
18 Suka kalubalance shi suka ce, “Ba daidai ba ne, Uzziya, ka ƙone turare ga Ubangiji. Wannan aikin firistoci zuriyar Haruna ne, waɗanda aka tsarkake don ƙone turare. Ka bar wuri mai tsarki, gama ka kasance marar aminci; kuma Ubangiji Allah ba zai girmama ka ba.”
Ils résistèrent au roi Ozias et lui dirent: « Ce n'est pas à toi, Ozias, de brûler des parfums à l'Éternel, mais aux prêtres, fils d'Aaron, qui sont consacrés pour brûler des parfums. Sors du sanctuaire, car tu as commis une faute. Ce ne sera pas pour ton honneur de la part de Yahvé Dieu. »
19 Uzziya wanda yake da farantin wuta a hannunsa a shirye don ƙone turare, ya husata. Yayinda yake fushi da firistocin a gabansu a gaban bagaden turare a haikalin Ubangiji, sai kuturta ta faso a goshinsa.
Ozias se mit en colère. Il avait à la main un encensoir pour brûler des parfums, et comme il était en colère contre les prêtres, la lèpre se déclara sur son front devant les prêtres, dans la maison de l'Éternel, à côté de l'autel des parfums.
20 Sa’ad da Azariya babban firist da dukan sauran firistoci suka dube shi, sai suka ga cewa yana da kuturta a goshinsa, saboda haka suka gaggauta tunkuɗa shi waje nan da nan. Tabbatacce, shi kansa ma ya yi marmari yă bar wurin domin Ubangiji ya buge shi.
Azaria, le grand prêtre, et tous les prêtres le regardèrent, et voici qu'il avait la lèpre au front; et ils le chassèrent rapidement de là. En effet, lui-même se hâtait aussi de sortir, car l'Éternel l'avait frappé.
21 Sarki Uzziya ya kasance da kuturta har ranar mutuwarsa. Ya zauna a gidan da aka ware, da kuturci, aka kuma ware shi daga haikalin Ubangiji. Yotam ɗansa ya lura da fadan ya kuma yi mulkin mutanen ƙasar.
Le roi Ozias fut lépreux jusqu'au jour de sa mort, et il habita dans une maison séparée, étant lépreux, car il avait été retranché de la maison de l'Éternel. Jotham, son fils, était à la tête de la maison du roi, jugeant le peuple du pays.
22 Sauran ayyukan mulkin Uzziya daga farko zuwa ƙarshe, suna a rubuce ta hannun annabi Ishaya ɗan Amoz.
Le reste des actes d'Ozias, les premiers et les derniers, c'est Ésaïe, le prophète, fils d'Amoz, qui les a écrits.
23 Uzziya ya huta da kakanninsa aka kuma binne shi kusa da su a fili don binnewar da take ta sarakuna, domin mutane sun ce, “Yana da kuturta.” Sai Yotam ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Ozias se coucha avec ses pères, et on l'enterra avec ses pères dans le champ d'enterrement qui appartenait aux rois, car on disait: « Il est lépreux. » Jotham, son fils, régna à sa place.

< 2 Tarihi 26 >