< 2 Tarihi 26 >

1 Sai dukan mutanen Yahuda suka ɗauki Uzziya wanda yake da shekara goma sha shida da haihuwa, suka naɗa shi sarki a madadin mahaifinsa Amaziya.
Alt Folket i Juda tog så Uzzija, der da var seksten År gammel, og gjorde ham til Konge i hans Fader Amazjas Sted.
2 Shi ne wanda ya sāke gina Elot ya kuma mai da shi ga Yahuda bayan Amaziya ya huta tare da kakanninsa.
Det var ham, der befæstede Elot og atter forenede det med Juda efter at Kongen havde lagt sig til Hvile hos sine Fædre.
3 Uzziya yana da shekara goma sha shida sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara hamsin da biyu. Sunan mahaifiyarsa Yekoliya ce; ita daga Urushalima ce.
Uzzija var seksten År gammel da han blev Konge, og han herskede to og halvtredsindstyve År i Jerusalem. Hans Moder hed Jekolja og var fra Jerusalem.
4 Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar dai yadda mahaifinsa Amaziya ya yi.
Han gjorde, hvad der var ret i HERRENs Øjne, ganske som hans Fader Amazja;
5 Ya nemi Allah a kwanakin Zakariya, wanda ya koyar da shi a tsoron Allah. Muddin ya nemi Ubangiji, Allah ya ba shi nasara.
og han blev ved med at søge Gud, så længe Zekarja, der havde undervist ham i Gudsfrygt, levede. Og så længe han søgte HERREN, gav Gud ham Lykke.
6 Ya yi yaƙi da Filistiyawa ya kuma rushe katangar Gat, Yabne da kuma Ashdod. Sa’an nan ya sāke gina garuruwa kusa da Ashdod da sauran wurare a cikin Filistiyawa.
Han gjorde et Krigstog mod Filisterne og nedrev Bymurene i Gat, Jabne og Asdod og byggede Byer i Asdods Område og Filisterlandet.
7 Allah ya taimake shi a kan Filistiyawa da kuma a kan Larabawa waɗanda suke zama a Gur-Ba’al da kuma a kan Meyunawa.
Gud hjalp ham mod Filisterne og Araberne, der boede i Gur-Ba'al og mod Me'uniterne.
8 Ammonawa suka kawo haraji wa Uzziya, sunan da ya yi kuwa ya bazu har iyakar Masar, domin ya zama mai iko sosai.
Atnmoniterne svarede Uzzija Skat, og hans Ry nåede til Ægypten, thi han blev overmåde mægtig.
9 Uzziya ya gina hasumiyoyi a Urushalima a Ƙofar Kusurwa, a Ƙofar Kwari da kuma a kusurwar katanga, ya kuma yi musu katanga.
Og Uzzija byggede Tårne i Jerusalem ved Hjørneporten, Dalporten og Murhjørnet og befæstede
10 Ya gina hasumiyoyi a hamada ya kuma haƙa rijiyoyi masu yawa, gama yana da dabbobi masu yawa a gindin duwatsu da kuma a kwari. Yana da mutane masu yin masa aiki a gonakinsa da gonakin inabinsa a tuddai da kuma a ƙasashe masu dausayi, gama yana son noma.
Fremdeles byggede han Tårne i Ørkenen og lod mange Cisterner udhugge, thi han havde store Hjorde både i Lavlandet og på Højsletten, der hos Agerdyrkere og Vingårdsmænd på Bjergene og i Frugtlandet, thi han var ivrig Landmand.
11 Uzziya ya kasance da gogaggun mayaƙa, a shirye su fito ɓangarori-ɓangarori bisa ga yawansu yadda Yehiyel magatakarda, da Ma’asehiya jarumi, suka karkasa su bisa ga umarnin Hananiya, ɗaya daga cikin fadawa.
Og Uzzija havde en øvet Krigshær, der drog i Krig Deling for Deling i det Tal, der fremgik af Mønstringen, som Statsskriveren Je'uel og Retsskriveren Ma'aseja foretog under Tilsyn af Hananja, en at Kongens Øverster.
12 Yawan shugabannin iyali a bisa jarumawa sun kai 2,600.
Det fulde Tal på de dygtige Krigere, som var Overhoveder for Fædrenehusene, var 2600.
13 A ƙarƙashin shugabancinsu akwai mayaƙa 307,500 horarru don yaƙi, mayaƙa masu ƙarfi don su taimaki sarki a kan abokan gābansa.
Under deres Befaling stod en Hærstyrke på 307500 krigsvante Folk i deres fulde Kraft til at hjælpe Kongen mod Fjenden.
14 Uzziya ya tanada garkuwoyi, māsu, hulunan kwano, kayan sulke, baka da majajjawa don mayaƙan gaba ɗaya.
Uzzija udrustede hele Hæren med Skjolde, Spyd, Hjelme, Brynjer, Buer og Slyngesten.
15 A Urushalima ya yi na’urori da gwanaye suka sarrafa don amfani a hasumiyoyi da kuma a kusurwar kāriya don harbin kibiyoyi da jefan manyan duwatsu. Sunansa ya bazu ko’ina, gama ya sami taimako sosai har ya zama mai iko.
Ligeledes lod han i Jerusalem lave snildt udtænkte Krigsmaskiner, der opstilledes på Tårnene og Murtinderne til at udslynge Pile og store Sten. Og hans Ry nåede viden om, thi på underfuld Måde blev han hjulpet til stor Magt.
16 Amma bayan Uzziya ya zama mai iko, sai ɗaga kai ya kai shi ga fāɗuwa. Bai yi aminci ga Ubangiji Allahnsa ba, ya kuma shiga haikalin Ubangiji don yă ƙone turare a bagaden turare.
Men da han var blevet mægtig, blev hans Hjerte overmodigt, så han gjorde, hvad fordærveligt var; han handlede troløst mod HERREN sin Gud, idet han gik ind i HERRENs Helligdom for at brænde Røgelse på Røgelsealteret.
17 Azariya firist tare da waɗansu firistoci tamanin na Ubangiji masu ƙarfin hali suka bi shi ciki.
Præsten Azarja fulgte efter ham, ledsaget af firsindstyve af HERRENs Præster, modige Mænd;
18 Suka kalubalance shi suka ce, “Ba daidai ba ne, Uzziya, ka ƙone turare ga Ubangiji. Wannan aikin firistoci zuriyar Haruna ne, waɗanda aka tsarkake don ƙone turare. Ka bar wuri mai tsarki, gama ka kasance marar aminci; kuma Ubangiji Allah ba zai girmama ka ba.”
og de trådte frem for Kong Uzzija og sagde til ham: "At ofre HERREN Røgelse tilkommer ikke dig, Uzzija, men Arons Sønner, Præsterne, som er helliget til at ofre Røgelse; gå ud af Helligdommen, thi du har handlet troløst, og det tjener dig ikke til Ære for HERREN din Gud!"
19 Uzziya wanda yake da farantin wuta a hannunsa a shirye don ƙone turare, ya husata. Yayinda yake fushi da firistocin a gabansu a gaban bagaden turare a haikalin Ubangiji, sai kuturta ta faso a goshinsa.
Uzzija, der holdt Røgelsekarret i Hånden for at brænde Røgelse, blev rasende; men som han rasede mod Præsterne, slog Spedalskhed ud på hans Pande, medens han stod der over for Præsterne foran Røgelsealteret i HERRENs Hus;
20 Sa’ad da Azariya babban firist da dukan sauran firistoci suka dube shi, sai suka ga cewa yana da kuturta a goshinsa, saboda haka suka gaggauta tunkuɗa shi waje nan da nan. Tabbatacce, shi kansa ma ya yi marmari yă bar wurin domin Ubangiji ya buge shi.
og da Ypperstepræsten Azarja og alle Præsterne vendte sig imod ham, se, da var han spedalsk i Panden. Så førte de ham hastigt bort derfra, og selv fik han travlt med at komme ud, fordi HERREN havde ramt ham.
21 Sarki Uzziya ya kasance da kuturta har ranar mutuwarsa. Ya zauna a gidan da aka ware, da kuturci, aka kuma ware shi daga haikalin Ubangiji. Yotam ɗansa ya lura da fadan ya kuma yi mulkin mutanen ƙasar.
Så var Kong Uzzija spedalsk til sin Dødedag; og skønt spedalsk fik han Lov at blive boende i sit Hus, men var udelukket fra HERRENs Hus, medens hans Søn Jotam rådede i Kongens Palads og dømte Folket i Landet.
22 Sauran ayyukan mulkin Uzziya daga farko zuwa ƙarshe, suna a rubuce ta hannun annabi Ishaya ɗan Amoz.
Hvad der ellers er at fortælle om Uzzija fra først til sidst, har Profeten Esajas, Amoz's Søn, optegnet.
23 Uzziya ya huta da kakanninsa aka kuma binne shi kusa da su a fili don binnewar da take ta sarakuna, domin mutane sun ce, “Yana da kuturta.” Sai Yotam ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Så lagde han sig til Hvile hos sine Fædre, og man jordede ham hos hans Fædre på den Mark, hor Kongegravene var, under Hensyn til at han havde været spedalsk; og hans Søn Jotam blev Konge i hans Sted.

< 2 Tarihi 26 >