< 2 Tarihi 25 >

1 Amaziya yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ashirin da tara. Sunan mahaifiyarsa Yehoyaddin ce; ita daga Urushalima ne.
Amacīja bija divdesmit piecus gadus vecs, kad palika par ķēniņu, un valdīja Jeruzālemē divdesmit deviņus gadus, un viņa mātei vārds bija Joadana, no Jeruzālemes.
2 Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, amma ba da dukan zuciyarsa ba.
Un viņš darīja, kas Tam Kungam labi patika, tomēr ne no visas sirds.
3 Bayan sarauta ta kahu a ƙarƙashinsa, sai ya kashe hafsoshin da suka kashe mahaifinsa sarki.
Kad nu viņš bija stiprinājies savā valstībā, tad viņš nokāva savus kalpus, kas bija kāvuši viņa tēvu, to ķēniņu.
4 Duk da haka bai kashe’ya’yansu maza ba amma ya yi bisa ga abin da yake a rubuce a cikin Doka, a cikin Littafin Musa, inda Ubangiji ya umarta, “Ba za a kashe iyaye saboda’ya’yansu ba; ba kuwa za a kashe’ya’ya saboda iyayensu ba; kowa zai mutu saboda zunubansa ne.”
Bet viņu bērnus viņš nenokāva, kā ir rakstīts Mozus bauslības grāmatā, kur Tas Kungs pavēlējis sacīdams: tēviem nebūs mirt par bērniem, un bērniem nebūs mirt par tēviem, bet ikviens lai mirst savu paša grēku dēļ.
5 Amaziya ya tattara mutanen Yahuda ya kuma ba su aiki bisa ga iyalansu, ya ba da aiki ga shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, a dukan Yahuda da Benyamin. Ya kuma tattara waɗanda suke’yan shekara ashirin da haihuwa ko fiye ya sami mutane dubu ɗari uku da suke a shirye don aikin soja, da suka isa riƙe māshi da garkuwa.
Un Amacīja salpulcināja Jūdu un tos šķīra pēc tēvu namiem, pēc tūkstošniekiem un pēc simtniekiem pa visu Jūdu un Benjaminu, un skaitīja no tiem tos, kas divdesmit un vairāk gadus bija veci, un atrada no tiem trīs simt reizi tūkstoš izlasītus, kas varēja iet karā un nesa šķēpus un priekšturamās bruņas.
6 Ya kuma ɗauko sojan haya jarumawa dubu ɗari ɗaya daga Isra’ila a kan talenti ɗari na azurfa.
Un viņš saderēja no Israēla simt tūkstoš stiprus karavīrus par simts talentiem sudraba.
7 Amma mutumin Allah ya zo wurinsa ya ce, “Ya sarki, waɗannan runduna daga Isra’ila ba za su tafi tare da kai ba, gama Ubangiji ba ya tare da Isra’ila, ba ya nan da wani cikin mutanen Efraim.
Bet viens Dieva vīrs nāca pie viņa un sacīja: ķēniņ! Israēla spēks lai tev neiet līdz, jo Tas Kungs nav ar Israēli, ar nevienu no Efraīma bērniem.
8 Ko da ma ya tafi ya yi faɗa da ƙwazo a cikin yaƙi, Allah zai tumɓuke shi a gaban abokan gāba, gama Allah yana da iko yă taimaka ko yă tumɓuke.”
Bet ja tu iesi un (to) darīsi un būsi drošs uz karu, tad Dievs tev liks krist ienaidnieka priekšā; jo Dievam ir spēks palīdzēt un nogāzt,
9 Amaziya ya tambayi mutumin Allah ya ce, “Amma game da talenti ɗarin da na biya saboda waɗannan rundunonin Isra’ila fa?” Mutumin Allah ya amsa, “Ubangiji zai ba ka fiye da wannan.”
Un Amacīja sacīja uz to Dieva vīru: bet ko tad es darīšu ar tiem simts talentiem, ko esmu devis Israēla karavīriem? Bet tas Dieva vīrs sacīja: Tam Kungam ir vairāk tev ko dot nekā tik daudz.
10 Saboda haka Amaziya ya sallame rundunonin da suka zo daga Efraim, ya kuma mayar da su gida. Suka husata da Yahuda suka koma gida da fushi sosai.
Tad Amacīja atšķīra tos karavīrus, kas no Efraīma bija nākuši pie viņa, lai tie ietu uz savām mājām. Bet tie ļoti apskaitās pret Jūdu un ar lielām dusmām griezās atkal atpakaļ uz savām mājām.
11 Sa’an nan Amaziya ya yi ƙarfin hali ya jagoranci mayaƙansa zuwa Kwarin Gishiri, inda ya kashe mutanen Seyir dubu goma.
Un Amacīja ņēmās drošu prātu un izveda savus ļaudis un nogāja sāls ielejā un kāva desmit tūkstošus no Seīra bērniem.
12 Mayaƙan Yahuda suka kuma kama mutane dubu goma da rai, suka ɗauke su zuwa ƙwanƙolin dutsen, suka yi ta tunkuɗa su ƙasa suka yi kaca-kaca.
Un Jūda bērni sagūstīja no tiem desmit tūkstošus dzīvus un tos veda klints galā un tos nogāza no paša klints gala, ka tie visi tapa sašķelti.
13 Ana cikin haka, sai rundunar da Amaziya ya mai da su gida, waɗanda ba a bari suka tafi yaƙin ba, suka kai wa garuruwan Yahuda daga Samariya zuwa Bet-Horon hari. Suka kashe mutane dubu uku suka kwashe ganima mai yawan gaske.
Bet tie karavīri, kam Amacīja bija licis iet atpakaļ, lai tie ar viņu karā neietu, tie ielauzās Jūda pilsētās no Samarijas līdz BetOronai un kāva no tiem trīs tūkstošus un aiznesa lielu laupījumu.
14 Da Amaziya ya dawo daga kisan mutanen Edom, sai ya dawo da allolin mutanen Seyir. Ya kafa su a matsayin allolinsa, ya rusuna musu, ya kuma miƙa musu hadayun ƙonawa.
Kad nu Amacīja pārnāca no Edomiešu kaujas un bija atvedis līdz Seīra bērnu dievus, tad viņš tos sev iecēla par dieviem un metās zemē viņu priekšā un tiem kvēpināja.
15 Fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kan Amaziya, sai ya aiki wani annabi wurinsa wanda ya ce, “Me ya sa ka nemi shawarar allolin mutanen nan, waɗanda ba za su cece mutanensu daga hannunka ba?”
Tad Tā Kunga bardzība iedegās pret Amacīju, un Viņš sūtīja pie tā pravieti. Tas uz viņu sacīja: kāpēc tu esi meklējis to ļaužu dievus, kas savus ļaudis nevarēja atpestīt no tavas rokas?
16 Tun yana cikin magana, sai sarki ya ce masa, “Yaushe muka naɗa ka mai ba sarki shawara? Rufe mana baki! Me zai hana a kashe ka?” Sai annabin ya yi shiru, amma ya ce, “Na dai sani Allah ya riga ya shirya zai hallaka ka, saboda ka aikata wannan, ba ka kuma saurari shawarata ba.”
Kad nu viņš uz to tā runāja, tad tas uz viņu sacīja: vai tu esi iecelts par ķēniņa padoma devēju? Esi klusu, kāpēc lai tevi nokauj? Tad tas pravietis apklusa un sacīja: es gan atzīstu, ka Dievs apņēmies tevi samaitāt, tāpēc ka tu to esi darījis un neesi klausījis manam padomam.
17 Bayan Amaziya sarkin Yahuda ya nemi shawara mashawartansa, sai ya kalubalanci Yowash ɗan Yehoyahaz, ɗan Yehu, sarkin Isra’ila, “Zo mu gamu fuska da fuska.”
Un Amacīja, Jūda ķēniņš, aprunājās un sūtīja pie Jehoasa, Joakasa dēla, Jeūs dēla dēla, Israēla ķēniņa, un sacīt: nāc, griezīsim vaigu pret vaigu!
18 Amma Yowash sarkin Isra’ila ya amsa wa Amaziya sarkin Yahuda ya ce, “Wata ƙaya ce a Lebanon, ta aika da saƙo wa itacen al’ul na Lebanon cewa, ‘Ka ba ɗana’yarka aure.’ Sai wani naman jeji na Lebanon ya zo ya tattake ƙayar.
Bet Jehoas, Israēla ķēniņš, sūtīja pie Amacījas, Jūda ķēniņa, un lika sacīt: ērkšķu krūms uz Lībanus sūtīja pie ciedra koka uz Lībanus un sacīja: dod savu meitu manam dēlam par sievu; bet tie lauka zvēri, kas uz Lībanus, gāja pāri un samina to ērkšķu krūmu.
19 Ka ce wa kanka cewa ka ci Edom da yaƙi, yanzu kuwa kana fariya da ɗaga kai. Amma tsaya dai a gida! Me ya sa kake neman faɗa kana neman fāɗuwarka da ta Yahuda?”
Redzi, tu domā, tu esi kāvis Edomiešus, un tava sirds lepojās un lielās. Nu tad, paliec mājās, kāpēc tu gribi skriet nelaimē, pats krist un Jūda līdz ar tevi?
20 Amma Amaziya bai saurara ba gama Allah ya yi haka domin yă miƙa su ga Yehowash, domin sun nemi shawarar allolin Edom.
Bet Amacīja neklausīja, jo tas notika no Dieva, lai viņš tos viņiem dotu rokā, tāpēc ka tie bija meklējuši Edomiešu dievus.
21 Saboda haka Yowash sarkin Isra’ila ya kai yaƙi. Shi da Amaziya sarkin Yahuda suka fuskanci juna a Bet-Shemesh a Yahuda.
Un Jehoas, Israēla ķēniņš, cēlās, un tie grieza vaigu pret vaigu, viņš un Amacīja, Jūda ķēniņš, BetŠemē iekš Jūda.
22 Isra’ila ta fatattaki Yahuda, sai kowane mutum ya gudu zuwa gidansa.
Un Jūda tapa kauts Israēla priekšā, un tie bēga ikviens uz savu dzīvokli.
23 Yehowash sarkin Isra’ila ya kama Amaziya sarkin Yahuda, ɗan Yowash, ɗan Ahaziya a Bet-Shemesh. Sa’an nan Yehowash ya kawo shi Urushalima ya farfasa katangar Urushalima daga Ƙofar Efraim har zuwa Ƙofar Kusurwa, wani sashe mai tsawon ƙafa ɗari shida.
Un Jehoas Israēla ķēniņš, sagūstīja Amacīju, Jūda ķēniņu, Joasa dēlu, Joakasa (Ahazijas) dēla dēlu, BetŠemesā un to noveda Jeruzālemē un noplēsa Jeruzālemes mūrus no Efraīma vārtiem līdz Stūra vārtiem četrsimt olektis.
24 Ya kwashe dukan zinariya da azurfa da dukan kayayyakin da aka samu a haikalin Allah waɗanda suke a ƙarƙashin kulawar Obed-Edom, da kaya masu daraja na gidan sarki, da waɗanda aka kamo cikin yaƙi, ya kawo Samariya.
Un viņš ņēma visu zeltu un sudrabu un visus traukus, kas Dieva namā tapa atrasti pie ObedEdoma, un ķēniņa nama mantas līdz ar tiem galviniekiem un griezās atpakaļ uz Samariju.
25 Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda ya rayu shekara goma sha biyar bayan mutuwar Yehowash ɗan Yehoyahaz sarkin Isra’ila.
Un Amacīja, Joasa dēls, Jūda ķēniņš dzīvoja pēc tam, kad Jehoas, Joakasa dēls, Israēla ķēniņš, bija nomiris, piecpadsmit gadus.
26 Game da sauran ayyukan mulkin Amaziya, daga farko zuwa ƙarshe, an rubuta su a littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
Un kas vēl par Amacīju stāstāms, ir par viņa iesākumu, ir par viņa galu, redzi, tas rakstīts Jūda un Israēla ķēniņu grāmatā.
27 Sa’ad da Amaziya ya bar bin Ubangiji, aka shirya masa maƙarƙashiya a Urushalima, sai ya gudu zuwa Lakish, amma suka aiki mutane suka bi shi zuwa Lakish, a can suka kashe shi.
Un no tā laika, kamēr Amacīja no Tā Kunga bija atkāpies, dumpis pret viņu cēlās Jeruzālemē, un viņš bēga uz Laķisu. Bet tie viņam sūtīja pakaļ uz Laķisu un to tur nokāva,
28 Aka dawo da shi a kan doki, aka binne shi tare da kakanninsa a Birnin Yahuda.
Un to atveda uz zirgiem un apraka pie viņa tēviem Jūda pilsētā.

< 2 Tarihi 25 >