< 2 Tarihi 25 >

1 Amaziya yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ashirin da tara. Sunan mahaifiyarsa Yehoyaddin ce; ita daga Urushalima ne.
Amasias avait vingt-cinq ans lorsqu’il commença à régner, et il régna vingt-neuf ans à Jérusalem: le nom de sa mère était Joadan de Jérusalem.
2 Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, amma ba da dukan zuciyarsa ba.
Et il fit le bien en la présence du Seigneur, mais non avec un cœur parfait.
3 Bayan sarauta ta kahu a ƙarƙashinsa, sai ya kashe hafsoshin da suka kashe mahaifinsa sarki.
Et, lorsqu’il vit son empire affermi, il fit égorger les serviteurs qui avaient tué le roi son père;
4 Duk da haka bai kashe’ya’yansu maza ba amma ya yi bisa ga abin da yake a rubuce a cikin Doka, a cikin Littafin Musa, inda Ubangiji ya umarta, “Ba za a kashe iyaye saboda’ya’yansu ba; ba kuwa za a kashe’ya’ya saboda iyayensu ba; kowa zai mutu saboda zunubansa ne.”
Mais leurs enfants, il ne les tua point, comme il est écrit dans le Livre de la loi de Moïse, où le Seigneur a ordonné, disant: Des pères ne seront pas mis à mort pour des enfants, ni des enfants pour des pères; mais chacun mourra pour son péché.
5 Amaziya ya tattara mutanen Yahuda ya kuma ba su aiki bisa ga iyalansu, ya ba da aiki ga shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, a dukan Yahuda da Benyamin. Ya kuma tattara waɗanda suke’yan shekara ashirin da haihuwa ko fiye ya sami mutane dubu ɗari uku da suke a shirye don aikin soja, da suka isa riƙe māshi da garkuwa.
Amasias assembla donc Juda, et il les établit par familles, tribuns et centurions dans tout Juda et Benjamin; et il les recensa depuis vingt ans et au-dessus, et il trouva trois cent mille jeunes hommes qui pouvaient sortir pour les combats, et porter une lance et un bouclier.
6 Ya kuma ɗauko sojan haya jarumawa dubu ɗari ɗaya daga Isra’ila a kan talenti ɗari na azurfa.
Il engagea aussi cent mille hommes robustes d’Israël au prix de cent talents d’argent.
7 Amma mutumin Allah ya zo wurinsa ya ce, “Ya sarki, waɗannan runduna daga Isra’ila ba za su tafi tare da kai ba, gama Ubangiji ba ya tare da Isra’ila, ba ya nan da wani cikin mutanen Efraim.
Or un homme de Dieu vint vers lui, et dit: ô roi, que l’armée d’Israël ne sorte pas avec vous; car Dieu n’est point avec Israël, ni avec les enfants d’Ephraïm.
8 Ko da ma ya tafi ya yi faɗa da ƙwazo a cikin yaƙi, Allah zai tumɓuke shi a gaban abokan gāba, gama Allah yana da iko yă taimaka ko yă tumɓuke.”
Que si vous croyez que la guerre consiste dans la force de l’armée, Dieu fera que vous serez vaincu par vos ennemis; car c’est à Dieu à secourir et à mettre en fuite.
9 Amaziya ya tambayi mutumin Allah ya ce, “Amma game da talenti ɗarin da na biya saboda waɗannan rundunonin Isra’ila fa?” Mutumin Allah ya amsa, “Ubangiji zai ba ka fiye da wannan.”
Et Amasias demanda à l’homme de Dieu: Que sera-t-il donc fait des cent talents que j’ai donnés aux soldats d’Israël? Et l’homme de Dieu lui répondit: Le Seigneur a de quoi pouvoir vous donner beaucoup plus que ces cent talents.
10 Saboda haka Amaziya ya sallame rundunonin da suka zo daga Efraim, ya kuma mayar da su gida. Suka husata da Yahuda suka koma gida da fushi sosai.
C’est pourquoi Amasias sépara l’armée qui lui était venue d’Ephraïm, afin qu’elle retournât en son lieu; mais c’est violemment irritées contre Juda que ces troupes retournèrent dans leur contrée.
11 Sa’an nan Amaziya ya yi ƙarfin hali ya jagoranci mayaƙansa zuwa Kwarin Gishiri, inda ya kashe mutanen Seyir dubu goma.
Or Amasias, conduisit son peuple résolument; il alla dans la vallée des Salines, et il battit les enfants de Séir au nombre de dix mille.
12 Mayaƙan Yahuda suka kuma kama mutane dubu goma da rai, suka ɗauke su zuwa ƙwanƙolin dutsen, suka yi ta tunkuɗa su ƙasa suka yi kaca-kaca.
Et les enfants de Juda prirent dix autres mille hommes; ils les amenèrent sur le pic du rocher, et les précipitèrent du haut en bas, et tous furent brisés.
13 Ana cikin haka, sai rundunar da Amaziya ya mai da su gida, waɗanda ba a bari suka tafi yaƙin ba, suka kai wa garuruwan Yahuda daga Samariya zuwa Bet-Horon hari. Suka kashe mutane dubu uku suka kwashe ganima mai yawan gaske.
Mais l’armée qu’Amasias avait renvoyée, afin qu’elle n’allât pas avec lui au combat, se répandit dans les villes de Juda, depuis Samarie jusqu’à Béthoron, et, trois mille hommes tués, elle enleva un grand butin.
14 Da Amaziya ya dawo daga kisan mutanen Edom, sai ya dawo da allolin mutanen Seyir. Ya kafa su a matsayin allolinsa, ya rusuna musu, ya kuma miƙa musu hadayun ƙonawa.
Or Amasias, après avoir taillé en pièces les Iduméens et avoir emporté les dieux des enfants de Séir, en fit des dieux pour lui-même; il les adorait, et leur brûlait de l’encens.
15 Fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kan Amaziya, sai ya aiki wani annabi wurinsa wanda ya ce, “Me ya sa ka nemi shawarar allolin mutanen nan, waɗanda ba za su cece mutanensu daga hannunka ba?”
C’est pourquoi le Seigneur, irrité contre Amasias, envoya vers lui un prophète pour lui dire: Pourquoi avez-vous adoré les dieux qui n’ont pas délivré leur peuple de votre main?
16 Tun yana cikin magana, sai sarki ya ce masa, “Yaushe muka naɗa ka mai ba sarki shawara? Rufe mana baki! Me zai hana a kashe ka?” Sai annabin ya yi shiru, amma ya ce, “Na dai sani Allah ya riga ya shirya zai hallaka ka, saboda ka aikata wannan, ba ka kuma saurari shawarata ba.”
Comme le prophète disait ces choses, Amasias lui répondit: Est-ce que tu es conseiller du roi? Tais-toi, de peur que je ne te tue. Alors le prophète se retirant: Je sais, dit-il, que Dieu a résolu de vous tuer, parce que vous avez fait ce mal, et que de plus vous n’avez pas voulu acquiescer à mes conseils.
17 Bayan Amaziya sarkin Yahuda ya nemi shawara mashawartansa, sai ya kalubalanci Yowash ɗan Yehoyahaz, ɗan Yehu, sarkin Isra’ila, “Zo mu gamu fuska da fuska.”
Ainsi Amasias, roi de Juda, ayant pris une détestable résolution, envoya vers Joas, fils de Joachaz, fils de Jéhu, roi d’Israël, disant: Venez, et voyons-nous mutuellement.
18 Amma Yowash sarkin Isra’ila ya amsa wa Amaziya sarkin Yahuda ya ce, “Wata ƙaya ce a Lebanon, ta aika da saƙo wa itacen al’ul na Lebanon cewa, ‘Ka ba ɗana’yarka aure.’ Sai wani naman jeji na Lebanon ya zo ya tattake ƙayar.
Mais Joas renvoya les messagers, disant: Le chardon qui est au Liban envoya vers le cèdre du Liban, disant: Donnez votre fille à mon fils pour femme; et voilà que les bêtes qui étaient dans la forêt du Liban passèrent et foulèrent aux pieds le chardon.
19 Ka ce wa kanka cewa ka ci Edom da yaƙi, yanzu kuwa kana fariya da ɗaga kai. Amma tsaya dai a gida! Me ya sa kake neman faɗa kana neman fāɗuwarka da ta Yahuda?”
Vous avez dit: J’ai battu Edom, et c’est pourquoi votre cœur s’élève jusqu’à l’orgueil. Demeurez en votre maison: pourquoi provoquez-vous un malheur pour que vous tombiez, et vous et Juda avec vous?
20 Amma Amaziya bai saurara ba gama Allah ya yi haka domin yă miƙa su ga Yehowash, domin sun nemi shawarar allolin Edom.
Amasias ne voulut pas l’écouter, parce que la volonté du Seigneur était qu’il fût livré dans les mains des ennemis, à cause des dieux d’Edom.
21 Saboda haka Yowash sarkin Isra’ila ya kai yaƙi. Shi da Amaziya sarkin Yahuda suka fuskanci juna a Bet-Shemesh a Yahuda.
Joas, roi d’Israël, monta donc, et les deux armées se mirent en présence. Or Amasias, roi de Juda, était campé à Bethsamès de Juda;
22 Isra’ila ta fatattaki Yahuda, sai kowane mutum ya gudu zuwa gidansa.
Et Juda tomba devant Israël, et s’enfuit dans ses tabernacles.
23 Yehowash sarkin Isra’ila ya kama Amaziya sarkin Yahuda, ɗan Yowash, ɗan Ahaziya a Bet-Shemesh. Sa’an nan Yehowash ya kawo shi Urushalima ya farfasa katangar Urushalima daga Ƙofar Efraim har zuwa Ƙofar Kusurwa, wani sashe mai tsawon ƙafa ɗari shida.
Pour Amasias, roi de Juda, fils de Joas, fils de Joachaz, Joas, roi d’Israël, le prit dans Bethsamès, et l’emmena à Jérusalem; et il détruisit aussi son mur, depuis la porte d’Ephraïm jusqu’à la porte de l’angle, espace de quatre cents coudées.
24 Ya kwashe dukan zinariya da azurfa da dukan kayayyakin da aka samu a haikalin Allah waɗanda suke a ƙarƙashin kulawar Obed-Edom, da kaya masu daraja na gidan sarki, da waɗanda aka kamo cikin yaƙi, ya kawo Samariya.
Il emporta encore tout l’or et l’argent et tous les vases qu’il avait trouvés dans la maison de Dieu et chez Obédédom, et même dans les trésors de la maison royale; il ramena aussi à Samarie les fils des otages.
25 Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda ya rayu shekara goma sha biyar bayan mutuwar Yehowash ɗan Yehoyahaz sarkin Isra’ila.
Or Amasias, fils de Joas, roi de Juda, vécut quinze ans après que fut mort Joas, fils de Joachaz, roi d’Israël.
26 Game da sauran ayyukan mulkin Amaziya, daga farko zuwa ƙarshe, an rubuta su a littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
Mais le reste des actions d’Amasias, des premières et des dernières, est écrit dans le Livre des rois de Juda et d’Israël.
27 Sa’ad da Amaziya ya bar bin Ubangiji, aka shirya masa maƙarƙashiya a Urushalima, sai ya gudu zuwa Lakish, amma suka aiki mutane suka bi shi zuwa Lakish, a can suka kashe shi.
Après qu’Amasias eut abandonné le Seigneur, on lui tendit des embûches dans Jérusalem; et, comme il se fut enfui à Lachis, on envoya, et on le tua là.
28 Aka dawo da shi a kan doki, aka binne shi tare da kakanninsa a Birnin Yahuda.
Et le rapportant sur les chevaux, on l’ensevelit avec ses pères dans la cité de David.

< 2 Tarihi 25 >