< 2 Tarihi 25 >

1 Amaziya yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ashirin da tara. Sunan mahaifiyarsa Yehoyaddin ce; ita daga Urushalima ne.
C'est à vingt-cinq ans que Amatsia devint roi, et il régna vingt-neuf ans à Jérusalem. Or le nom de sa mère était Joadan de Jérusalem.
2 Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, amma ba da dukan zuciyarsa ba.
Et il fit ce qui est bien aux yeux de l'Éternel, seulement pas d'un cœur non partagé.
3 Bayan sarauta ta kahu a ƙarƙashinsa, sai ya kashe hafsoshin da suka kashe mahaifinsa sarki.
Et lorsque la royauté lui fut assurée, il fit périr ses serviteurs, meurtriers du roi son père.
4 Duk da haka bai kashe’ya’yansu maza ba amma ya yi bisa ga abin da yake a rubuce a cikin Doka, a cikin Littafin Musa, inda Ubangiji ya umarta, “Ba za a kashe iyaye saboda’ya’yansu ba; ba kuwa za a kashe’ya’ya saboda iyayensu ba; kowa zai mutu saboda zunubansa ne.”
Mais il ne mit pas à mort leurs fils, se conformant à ce qui est écrit dans la Loi, dans le Livre de Moïse, d'après l'ordre de l'Éternel, portant: Les pères ne subiront pas la mort à cause de leurs fils, et les fils ne subiront pas la mort à cause de leurs pères, mais chacun subira la mort pour son péché.
5 Amaziya ya tattara mutanen Yahuda ya kuma ba su aiki bisa ga iyalansu, ya ba da aiki ga shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, a dukan Yahuda da Benyamin. Ya kuma tattara waɗanda suke’yan shekara ashirin da haihuwa ko fiye ya sami mutane dubu ɗari uku da suke a shirye don aikin soja, da suka isa riƙe māshi da garkuwa.
Et Amatsia assembla les hommes de Juda et les rangea par maisons patriarcales, par chefs de milliers et par chefs de centaines, pour la totalité de Juda et de Benjamin, et il les dénombra dès l'âge de vingt ans et au-dessus, et il en trouva trois cent mille d'élite, aptes à la guerre, maniant la lance et le bouclier.
6 Ya kuma ɗauko sojan haya jarumawa dubu ɗari ɗaya daga Isra’ila a kan talenti ɗari na azurfa.
Et il prit à sa solde d'Israël cent mille hommes forts dans la guerre, pour le prix de cent talents d'argent.
7 Amma mutumin Allah ya zo wurinsa ya ce, “Ya sarki, waɗannan runduna daga Isra’ila ba za su tafi tare da kai ba, gama Ubangiji ba ya tare da Isra’ila, ba ya nan da wani cikin mutanen Efraim.
Cependant un homme de Dieu vint le trouver et lui dit: O roi, ne te fais pas accompagner par des troupes d'Israël, car l'Éternel n'est pas avec Israël, avec tous les enfants d'Éphraïm!
8 Ko da ma ya tafi ya yi faɗa da ƙwazo a cikin yaƙi, Allah zai tumɓuke shi a gaban abokan gāba, gama Allah yana da iko yă taimaka ko yă tumɓuke.”
va plutôt seul, agis et tiens ferme au combat! Dieu pourrait te faire tomber devant l'ennemi, car à Dieu est le pouvoir de soutenir ou de faire tomber.
9 Amaziya ya tambayi mutumin Allah ya ce, “Amma game da talenti ɗarin da na biya saboda waɗannan rundunonin Isra’ila fa?” Mutumin Allah ya amsa, “Ubangiji zai ba ka fiye da wannan.”
Et Amatsia dit à l'homme de Dieu: Mais que faire à l'égard des cent talents que j'ai délivrés à la troupe d'Israël? Et l'homme de Dieu dit: Dieu peut te rendre plus que cela.
10 Saboda haka Amaziya ya sallame rundunonin da suka zo daga Efraim, ya kuma mayar da su gida. Suka husata da Yahuda suka koma gida da fushi sosai.
Alors Amatsia les sépara, c'est-à-dire la troupe arrivée chez lui d'Éphraïm, afin qu'ils retournassent en leurs lieux. Mais ils furent irrités d'une extrême colère contre Juda, et ils rentrèrent en leurs lieux enflammés de colère.
11 Sa’an nan Amaziya ya yi ƙarfin hali ya jagoranci mayaƙansa zuwa Kwarin Gishiri, inda ya kashe mutanen Seyir dubu goma.
Néanmoins Amatsia s'enhardit et prit son peuple sous sa conduite et gagna la Vallée du sel, et il tua aux enfants de Séïr dix mille hommes.
12 Mayaƙan Yahuda suka kuma kama mutane dubu goma da rai, suka ɗauke su zuwa ƙwanƙolin dutsen, suka yi ta tunkuɗa su ƙasa suka yi kaca-kaca.
Et les enfants de Juda en firent prisonniers dix mille vivants, qu'ils menèrent à la pointe de la roche d'où ils les précipitèrent, de sorte que tous ils furent éventrés.
13 Ana cikin haka, sai rundunar da Amaziya ya mai da su gida, waɗanda ba a bari suka tafi yaƙin ba, suka kai wa garuruwan Yahuda daga Samariya zuwa Bet-Horon hari. Suka kashe mutane dubu uku suka kwashe ganima mai yawan gaske.
Cependant les gens de la troupe qu'Amatsia avait congédiés pour n'en être pas accompagné au combat, se jetèrent dans les villes de Juda, de Samarie à Bethoron, et y tuèrent trois mille hommes et emportèrent un grand butin.
14 Da Amaziya ya dawo daga kisan mutanen Edom, sai ya dawo da allolin mutanen Seyir. Ya kafa su a matsayin allolinsa, ya rusuna musu, ya kuma miƙa musu hadayun ƙonawa.
Et Amatsia, de retour après la défaite des Édomites, fit venir les dieux des enfants de Séïr et se les érigea en dieux, et les adora et leur offrit de l'encens.
15 Fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kan Amaziya, sai ya aiki wani annabi wurinsa wanda ya ce, “Me ya sa ka nemi shawarar allolin mutanen nan, waɗanda ba za su cece mutanensu daga hannunka ba?”
Alors la colère de l'Éternel s'alluma contre Amatsia, et Il lui délégua un prophète, qui lui dit: Pourquoi vas-tu chercher les dieux de ce peuple, qui n'ont pu sauver leur peuple de ta main?
16 Tun yana cikin magana, sai sarki ya ce masa, “Yaushe muka naɗa ka mai ba sarki shawara? Rufe mana baki! Me zai hana a kashe ka?” Sai annabin ya yi shiru, amma ya ce, “Na dai sani Allah ya riga ya shirya zai hallaka ka, saboda ka aikata wannan, ba ka kuma saurari shawarata ba.”
Et comme il lui parlait, [Amatsia] lui dit: T'a-t-on constitué conseiller du roi? Cesse! pourquoi veux-tu être battu? Alors le prophète s'abstint et dit: Je reconnais que Dieu a résolu ta perte, parce que tu agis ainsi et n'écoutes pas mon conseil.
17 Bayan Amaziya sarkin Yahuda ya nemi shawara mashawartansa, sai ya kalubalanci Yowash ɗan Yehoyahaz, ɗan Yehu, sarkin Isra’ila, “Zo mu gamu fuska da fuska.”
Et Amatsia, roi de Juda, se consulta, et il députa vers Joas, fils de Joachaz, fils de Jéhu, roi d'Israël, pour lui dire: Viens! voyons-nous en présence!
18 Amma Yowash sarkin Isra’ila ya amsa wa Amaziya sarkin Yahuda ya ce, “Wata ƙaya ce a Lebanon, ta aika da saƙo wa itacen al’ul na Lebanon cewa, ‘Ka ba ɗana’yarka aure.’ Sai wani naman jeji na Lebanon ya zo ya tattake ƙayar.
Alors Joas, roi d'Israël, députa vers Amatsia, roi de Juda, pour lui dire: L'épine du Liban députa vers le cèdre du Liban pour lui dire: Donne ta fille à mon fils pour femme! Alors passèrent les bêtes sauvages du Liban, et elles écrasèrent l'épine.
19 Ka ce wa kanka cewa ka ci Edom da yaƙi, yanzu kuwa kana fariya da ɗaga kai. Amma tsaya dai a gida! Me ya sa kake neman faɗa kana neman fāɗuwarka da ta Yahuda?”
Tu te dis: Voici, tu as battu les Édomites! et ton cœur te donne l'ambition de la gloire; or, reste chez toi! pourquoi veux-tu provoquer un revers pour tomber, toi, et Juda avec toi?
20 Amma Amaziya bai saurara ba gama Allah ya yi haka domin yă miƙa su ga Yehowash, domin sun nemi shawarar allolin Edom.
Mais Amatsia n'écouta point, car c'était une dispensation de Dieu à l'effet de le livrer pour avoir recherché les dieux d'Édom.
21 Saboda haka Yowash sarkin Isra’ila ya kai yaƙi. Shi da Amaziya sarkin Yahuda suka fuskanci juna a Bet-Shemesh a Yahuda.
Joas, roi d'Israël, s'avança donc et ils se virent en présence, lui et Amatsia, roi de Juda, à Bethsémès en Juda.
22 Isra’ila ta fatattaki Yahuda, sai kowane mutum ya gudu zuwa gidansa.
Mais Juda fut battu devant Israël, et ils s'enfuirent chacun dans leurs tentes.
23 Yehowash sarkin Isra’ila ya kama Amaziya sarkin Yahuda, ɗan Yowash, ɗan Ahaziya a Bet-Shemesh. Sa’an nan Yehowash ya kawo shi Urushalima ya farfasa katangar Urushalima daga Ƙofar Efraim har zuwa Ƙofar Kusurwa, wani sashe mai tsawon ƙafa ɗari shida.
Et Amatsia, roi de Juda, fils de Joas, fils d'Achazia, fut fait prisonnier à Bethsémès par Joas, roi d'Israël, qui le mena à Jérusalem, et démolit le mur de Jérusalem, depuis la porte d'Éphraïm jusqu'à la porte de l'angle sur un espace de quatre cents coudées,
24 Ya kwashe dukan zinariya da azurfa da dukan kayayyakin da aka samu a haikalin Allah waɗanda suke a ƙarƙashin kulawar Obed-Edom, da kaya masu daraja na gidan sarki, da waɗanda aka kamo cikin yaƙi, ya kawo Samariya.
et prit tout l'or et l'argent et tous les trésors qui se trouvaient dans la Maison de Dieu chez Obed-Édom, et les trésors du palais royal et les otages, puis revint à Samarie.
25 Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda ya rayu shekara goma sha biyar bayan mutuwar Yehowash ɗan Yehoyahaz sarkin Isra’ila.
Et Amatsia, fils de Joas, roi de Juda, vécut encore quinze ans après la mort de Joas, fils de Joachaz, roi d'Israël.
26 Game da sauran ayyukan mulkin Amaziya, daga farko zuwa ƙarshe, an rubuta su a littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
Le reste des actes d'Amatsia, les premiers et les derniers, est d'ailleurs consigné dans le livre des rois de Juda et d'Israël.
27 Sa’ad da Amaziya ya bar bin Ubangiji, aka shirya masa maƙarƙashiya a Urushalima, sai ya gudu zuwa Lakish, amma suka aiki mutane suka bi shi zuwa Lakish, a can suka kashe shi.
Et à partir du temps où Amatsia s'éloigna de l'Éternel, il se forma contre lui une conjuration à Jérusalem, et il s'enfuit à Lachis, et ils envoyèrent à sa poursuite à Lachis, et là on le fit mourir.
28 Aka dawo da shi a kan doki, aka binne shi tare da kakanninsa a Birnin Yahuda.
Et il fut rapporté à dos de chevaux et reçut la sépulture à côté de ses pères dans la ville de Juda.

< 2 Tarihi 25 >