< 2 Tarihi 25 >

1 Amaziya yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ashirin da tara. Sunan mahaifiyarsa Yehoyaddin ce; ita daga Urushalima ne.
A son of twenty and five years hath Amaziah reigned, and twenty and nine years he hath reigned in Jerusalem, and the name of his mother [is] Jehoaddan of Jerusalem,
2 Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, amma ba da dukan zuciyarsa ba.
and he doth that which is right in the eyes of Jehovah — only, not with a perfect heart.
3 Bayan sarauta ta kahu a ƙarƙashinsa, sai ya kashe hafsoshin da suka kashe mahaifinsa sarki.
And it cometh to pass, when the kingdom hath been strong upon him, that he slayeth his servants, those smiting the king his father,
4 Duk da haka bai kashe’ya’yansu maza ba amma ya yi bisa ga abin da yake a rubuce a cikin Doka, a cikin Littafin Musa, inda Ubangiji ya umarta, “Ba za a kashe iyaye saboda’ya’yansu ba; ba kuwa za a kashe’ya’ya saboda iyayensu ba; kowa zai mutu saboda zunubansa ne.”
and their sons he hath not put to death, but [did] as is written in the law, in the book of Moses, whom Jehovah commanded, saying, 'Fathers do not die for sons, and sons die not for fathers, but each for his own sin they die.'
5 Amaziya ya tattara mutanen Yahuda ya kuma ba su aiki bisa ga iyalansu, ya ba da aiki ga shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, a dukan Yahuda da Benyamin. Ya kuma tattara waɗanda suke’yan shekara ashirin da haihuwa ko fiye ya sami mutane dubu ɗari uku da suke a shirye don aikin soja, da suka isa riƙe māshi da garkuwa.
And Amaziah gathereth Judah, and appointeth them, according to the house of the fathers, for heads of the thousands, and for heads of the hundreds, for all Judah and Benjamin; and he inspecteth them from a son of twenty years and upward, and findeth them three hundred thousand chosen ones, going forth to the host, holding spear and target.
6 Ya kuma ɗauko sojan haya jarumawa dubu ɗari ɗaya daga Isra’ila a kan talenti ɗari na azurfa.
And he hireth out of Israel a hundred thousand mighty ones of valour, with a hundred talents of silver;
7 Amma mutumin Allah ya zo wurinsa ya ce, “Ya sarki, waɗannan runduna daga Isra’ila ba za su tafi tare da kai ba, gama Ubangiji ba ya tare da Isra’ila, ba ya nan da wani cikin mutanen Efraim.
and a man of God hath come in unto him, saying, 'O king, the host of Israel doth not go with thee; for Jehovah is not with Israel — all the sons of Ephraim;
8 Ko da ma ya tafi ya yi faɗa da ƙwazo a cikin yaƙi, Allah zai tumɓuke shi a gaban abokan gāba, gama Allah yana da iko yă taimaka ko yă tumɓuke.”
but if thou art going — do [it], be strong for battle, God doth cause thee to stumble before an enemy, for there is power in God to help, and to cause to stumble.'
9 Amaziya ya tambayi mutumin Allah ya ce, “Amma game da talenti ɗarin da na biya saboda waɗannan rundunonin Isra’ila fa?” Mutumin Allah ya amsa, “Ubangiji zai ba ka fiye da wannan.”
And Amaziah saith to the man of God, 'And what — to do for the hundred talents that I have given to the troop of Israel?' And the man of God saith, 'Jehovah hath more to give to thee than this.'
10 Saboda haka Amaziya ya sallame rundunonin da suka zo daga Efraim, ya kuma mayar da su gida. Suka husata da Yahuda suka koma gida da fushi sosai.
And Amaziah separateth them — for the troop that hath come in unto him from Ephraim to go to their own place, and their anger doth burn mightily against Judah, and they turn back to their place in the heat of anger.
11 Sa’an nan Amaziya ya yi ƙarfin hali ya jagoranci mayaƙansa zuwa Kwarin Gishiri, inda ya kashe mutanen Seyir dubu goma.
And Amaziah hath strengthened himself, and leadeth his people, and goeth to the Valley of Salt, and smiteth the sons of Seir — ten thousand.
12 Mayaƙan Yahuda suka kuma kama mutane dubu goma da rai, suka ɗauke su zuwa ƙwanƙolin dutsen, suka yi ta tunkuɗa su ƙasa suka yi kaca-kaca.
And ten thousand alive have the sons of Judah taken captive, and they bring them to the top of the rock, and cast them from the top of the rock, and all of them have been broken.
13 Ana cikin haka, sai rundunar da Amaziya ya mai da su gida, waɗanda ba a bari suka tafi yaƙin ba, suka kai wa garuruwan Yahuda daga Samariya zuwa Bet-Horon hari. Suka kashe mutane dubu uku suka kwashe ganima mai yawan gaske.
And the sons of the troop that Amaziah hath sent back from going with him to battle — they rush against cities of Judah, from Samaria even unto Beth-Horon, and smite of them three thousand, and seize much prey.
14 Da Amaziya ya dawo daga kisan mutanen Edom, sai ya dawo da allolin mutanen Seyir. Ya kafa su a matsayin allolinsa, ya rusuna musu, ya kuma miƙa musu hadayun ƙonawa.
And it cometh to pass, after the coming in of Amaziah from smiting the Edomites, that he bringeth in the gods of the sons of Seir, and establisheth them to him for gods, and before them doth bow himself, and to them he maketh perfume.
15 Fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kan Amaziya, sai ya aiki wani annabi wurinsa wanda ya ce, “Me ya sa ka nemi shawarar allolin mutanen nan, waɗanda ba za su cece mutanensu daga hannunka ba?”
And the anger of Jehovah burneth against Amaziah, and He sendeth unto him a prophet, and he saith unto him, 'Why hast thou sought the gods of the people that have not delivered their people out of thy hand?'
16 Tun yana cikin magana, sai sarki ya ce masa, “Yaushe muka naɗa ka mai ba sarki shawara? Rufe mana baki! Me zai hana a kashe ka?” Sai annabin ya yi shiru, amma ya ce, “Na dai sani Allah ya riga ya shirya zai hallaka ka, saboda ka aikata wannan, ba ka kuma saurari shawarata ba.”
And it cometh to pass, in his speaking unto him, that he saith to him, 'For a counsellor to the king have we appointed thee? cease for thee; why do they smite thee?' And the prophet ceaseth, and saith, 'I have known that God hath counselled to destroy thee, because thou hast done this, and hast not hearkened to my counsel.'
17 Bayan Amaziya sarkin Yahuda ya nemi shawara mashawartansa, sai ya kalubalanci Yowash ɗan Yehoyahaz, ɗan Yehu, sarkin Isra’ila, “Zo mu gamu fuska da fuska.”
And Amaziah king of Judah taketh counsel, and sendeth unto Joash son of Jehoahaz, son of Jehu, king of Israel, saying,
18 Amma Yowash sarkin Isra’ila ya amsa wa Amaziya sarkin Yahuda ya ce, “Wata ƙaya ce a Lebanon, ta aika da saƙo wa itacen al’ul na Lebanon cewa, ‘Ka ba ɗana’yarka aure.’ Sai wani naman jeji na Lebanon ya zo ya tattake ƙayar.
'Come, we look one another in the face.' And Joash king of Israel sendeth unto Amaziah king of Judah, saying, 'The thorn that [is] in Lebanon hath sent unto the cedar that [is] in Lebanon, saying, Give thy daughter to my son for a wife; and pass by doth a beast of the field that [is] in Lebanon, and treadeth down the thorn.
19 Ka ce wa kanka cewa ka ci Edom da yaƙi, yanzu kuwa kana fariya da ɗaga kai. Amma tsaya dai a gida! Me ya sa kake neman faɗa kana neman fāɗuwarka da ta Yahuda?”
Thou hast said, Lo, I have smitten Edom; and thy heart hath lifted thee up to boast; now, abide in thy house, why dost thou stir thyself up in evil, that thou hast fallen, thou, and Judah with thee?'
20 Amma Amaziya bai saurara ba gama Allah ya yi haka domin yă miƙa su ga Yehowash, domin sun nemi shawarar allolin Edom.
And Amaziah hath not hearkened, for from God it [is] in order to give them into hand, because they have sought the gods of Edom;
21 Saboda haka Yowash sarkin Isra’ila ya kai yaƙi. Shi da Amaziya sarkin Yahuda suka fuskanci juna a Bet-Shemesh a Yahuda.
and go up doth Joash king of Israel, and they look one another in the face, he and Amaziah king of Judah, in Beth-Shemesh, that [is] Judah's,
22 Isra’ila ta fatattaki Yahuda, sai kowane mutum ya gudu zuwa gidansa.
and Judah is smitten before Israel, and they flee — each to his tents.
23 Yehowash sarkin Isra’ila ya kama Amaziya sarkin Yahuda, ɗan Yowash, ɗan Ahaziya a Bet-Shemesh. Sa’an nan Yehowash ya kawo shi Urushalima ya farfasa katangar Urushalima daga Ƙofar Efraim har zuwa Ƙofar Kusurwa, wani sashe mai tsawon ƙafa ɗari shida.
And Amaziah king of Judah, son of Joash, son of Jehoahaz, hath Joash king of Israel caught in Beth-Shemesh, and bringeth him in to Jerusalem, and breaketh down in the wall of Jerusalem from the gate of Ephraim unto the gate of the corner, four hundred cubits,
24 Ya kwashe dukan zinariya da azurfa da dukan kayayyakin da aka samu a haikalin Allah waɗanda suke a ƙarƙashin kulawar Obed-Edom, da kaya masu daraja na gidan sarki, da waɗanda aka kamo cikin yaƙi, ya kawo Samariya.
and [taketh] all the gold, and the silver, and all the vessels that are found in the house of God with Obed-Edom, and the treasures of the house of the king, and the sons of the pledges, and turneth back to Samaria.
25 Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda ya rayu shekara goma sha biyar bayan mutuwar Yehowash ɗan Yehoyahaz sarkin Isra’ila.
And Amaziah son of Joash, king of Judah, liveth after the death of Joash son of Jehoahaz, king of Israel, fifteen years;
26 Game da sauran ayyukan mulkin Amaziya, daga farko zuwa ƙarshe, an rubuta su a littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
and the rest of the matters of Amaziah, the first and the last, lo, are they not written on the books of the kings of Judah and Israel?
27 Sa’ad da Amaziya ya bar bin Ubangiji, aka shirya masa maƙarƙashiya a Urushalima, sai ya gudu zuwa Lakish, amma suka aiki mutane suka bi shi zuwa Lakish, a can suka kashe shi.
And from the time that Amaziah hath turned aside from after Jehovah — they make a conspiracy against him in Jerusalem, and he fleeth to Lachish, and they send after him to Lachish, and put him to death there,
28 Aka dawo da shi a kan doki, aka binne shi tare da kakanninsa a Birnin Yahuda.
and lift him up on the horses, and bury him with his fathers in the city of Judah.

< 2 Tarihi 25 >