< 2 Tarihi 23 >

1 A shekara ta bakwai Yehohiyada ya nuna ƙarfinsa. Ya yi alkawari da shugabanni na ɗari-ɗari, Azariya ɗan Yeroham, Ishmayel ɗan Yehohanan, Azariya ɗan Obed, Ma’asehiya ɗan Adahiya, da Elishafat ɗan Zikri.
Uti sjunde årena tog Jojada dristighet till sig, och tog med sig i förbund de öfversta öfver hundrade, nämliga Asaria, Jerohams son, Ismael, Johanans son, Asaria, Obeds son, Maaseja, Adaja son, och Elisaphat, Sichri son.
2 Suka ratsa cikin Yahuda suka tattara Lawiyawa da shugabannin iyalan Isra’ilawa daga dukan garuruwa. Sa’ad da suka zo Urushalima,
De foro omkring Juda, och hade de Leviter tillhopa utur alla Juda städer, och de öfversta fäderna i Israel; och de kommo till Jerusalem.
3 dukan taron suka yi alkawari da sarki a haikalin Allah. Yehohiyada ya ce musu, “Ɗan sarki zai yi mulki yadda Ubangiji ya yi alkawari game da zuriyar Dawuda.
Och hela menigheten gjorde ett förbund i Guds hus med Konungenom; och han sade till dem: Si, Konungens son skall Konung vara, såsom Herren sagt hafver, öfver Davids barn.
4 Yanzu ga abin da za ku yi, shi ne, kashi ɗaya bisa uku na firistoci da Lawiyawa waɗanda za su yi aiki a Asabbaci su yi tsaro a ƙofofi,
Så skolen I nu alltså göra: tredjedelen af eder, som på Sabbathsdagenom uppå gå, skola vara ibland de Prester och Leviter, som dörravaktare äro vid dörrarna;
5 kashi ɗaya bisa ukunku a fadan sarki, kashi ɗaya bisa uku kuma, a Ƙofar Harsashi, sai kuma dukan sauran mutane su kasance a filayen haikalin Ubangiji.
Tredjedelen i Konungshuset, och tredjedelen vid grundvalsdörrena; men allt folket skall vara i gårdenom till Herrans hus.
6 Babu wanda zai shiga haikalin Ubangiji sai firistoci da Lawiyawan da suke a aiki; za su iya shiga domin su tsarkaku ne, amma sauran mutane za su kiyaye abin da Ubangiji ya sa su yi.
Och att ingen går uti Herrans hus, utan Presterna och Leviterna, som tjena, de skola gå derin; förty de äro helige; och allt folket vakte Herrans vakt.
7 Lawiyawa za su tsaya kewaye da sarki, kowane mutum da makamansa a hannunsa. Duk wanda ya shiga haikali sai a kashe shi. Ku tsaya kusa da sarki a duk inda ya tafi.”
Och Leviterna skola gifva sig omkring Konungen, hvar och en med sine värjo i handene; och hvilken som går in i huset, han dräpes; och de skola vara när Konungenom, då han går ut och in.
8 Lawiyawa da dukan mutanen Yahuda suka yi yadda Yehohiyada firist ya umarta. Kowanne ya ɗauki mutanensa, waɗanda suke aiki a Asabbaci da waɗanda suka gama aiki, gama Yehohiyada firist bai bar waɗansu ɓangarori ba.
Och Leviterna, med hela Juda, gjorde såsom Presten Jojada budit hade. Och hvar och en tog sina män, som på Sabbathen uppå gingo, med dem som på Sabbathen af gingo: ty Presten Jojada lät icke komma de två hoparna ifrå hvarannan.
9 Sa’an nan ya ba shugabannin māsu da garkuwoyi manya da ƙanana na sarki Dawuda, waɗanda suke cikin haikalin Allah.
Och Presten Jojada fick öfverstarna öfver hundrade spetsar och sköldar, och Konung Davids vapen, som i Guds hus voro:
10 Ya kuma sa dukan mutane, kowanne da makaminsa a hannunsa, kewaye da sarki, kusa da bagade da kuma haikali, daga gefen kudu zuwa gefen arewa na haikali.
Och ställde allt folket, hvar och en med sine värjo i handene, ifrå det högra hörnet i husena allt intill det venstra hörnet, till altaret, och till huset omkring Konungen.
11 Yehohiyada da’ya’yansa maza suka fitar da ɗan sarki suka sa rawani a kansa; suka miƙa masa alkawarin, suka kuma yi shelarsa a matsayin sarki. Suka shafe shi suka kuma tā da murya suna cewa, “Ran sarki yă daɗe!”
Och de hade fram Konungens son, och satte krono uppå honom, och vittnesbördet, och gjorde honom till Konung. Och Jojada med hans söner smorde honom, och sade: Lycka ske Konungenom.
12 Sa’ad da Ataliya ta ji surutun mutane suna gudu suna yabon sarki, sai ta tafi wurinsu a haikalin Ubangiji.
Då Athalia hörde ropet af folket, som tillopp och lofvade Konungen, gick hon till folket i Herrans hus;
13 Ta duba, a can kuwa ga sarki, tsaye kusa da ginshiƙinsa a mashigi. Manyan sojoji da masu bushe-bushe suna kusa da sarki, dukan mutanen ƙasar kuwa suna farin ciki suna busa ƙahoni, mawaƙa kuma da kayan kiɗi suna bi da yabo. Sai Ataliya ta yage rigunanta ta yi ihu tana cewa, “Cin amanar ƙasa! Cin amanar ƙasa!”
Och hon fick se, och si, Konungen stod i sitt rum i ingångenom, och öfverstarna och trummeterna omkring Konungen; och allt landsfolket var gladt, och blåste med trummeter, och sångarena med allahanda strängaspel skickade till att lofva. Då ref hon sin kläder, och sade: Uppror, uppror.
14 Yehohiyada firist ya fito da shugabanni waɗanda suke shugabancin rundunar sojoji, ya ce musu, “Ku fitar da ita tsakanin sojoji ku kuma kashe duk wanda ya bi ta da takobi.” Gama firist ya ce, “Kada ku kashe ta a haikalin Ubangiji.”
Men Presten Jojada drog sig ut med de öfversta öfver hundrade, som öfver hären voro, och sade till dem: Hafver henne utu huset i gården; och hvilken henne efterföljer, honom skall man dräpa med svärd. Förty Presten hade befallt, att man icke skulle dräpa henne i Herrans hus.
15 Saboda haka suka kama ta yayinda take kaiwa mashigin Ƙofar Doki a filin fada, a can suka kashe ta.
Och de togo fatt på henne. Och då hon kom till hästaportens ingång, vid Konungshuset, dråpo de henne der.
16 Sa’an nan Yehohiyada ya yi alkawari cewa shi da mutane da kuma sarki za su zama mutanen Ubangiji.
Och Jojada gjorde ett förbund emellan sig, och allt folket, och Konungen, att de skulle vara Herrans folk.
17 Dukan mutane suka tafi haikalin Ba’al suka rurrushe shi. Suka farfashe bagadan da gumakan, suka kuma kashe Mattan firist na Ba’al a gaban bagadan.
Då gick allt folket uti Baals hus, och bröto det neder, och slogo sönder hans altare och beläte, och slogo ihjäl Matthan, Baals Prest, inför altaret.
18 Sa’an nan Yehohiyada ya sa aikin lura da haikalin Ubangiji a hannuwan firistoci, waɗanda suke Lawiyawan da Dawuda ya ba su aikin haikali don su miƙa hadayun ƙonawa na Ubangiji kamar yadda yake a rubuce a Dokar Musa, da farin ciki da kuma rerawa, kamar yadda Dawuda ya umarta.
Och Jojada beställde ämbeten i Herrans hus, under Presterna, Leviterna, som David förskickat hade till Herrans hus, till att göra bränneoffer Herranom, såsom skrifvet står i Mose lag, med fröjd och sånger, som David diktat hade;
19 Ya kuma sa matsaran ƙofofi a ƙofofin haikalin Ubangiji don kada wani da ba shi da tsarki yă shiga.
Och ställde dörravaktare vid dörrarna åt Herrans hus, att der skulle intet orent inkomma i någon måtto.
20 Ya ɗauki shugabannin ɗari-ɗari, manyan gari, shugabannin mutane da dukan mutanen ƙasar tare da shi ya saukar da sarki daga haikalin Ubangiji. Suka shiga fada ta Ƙofar Bisa suka kuma zaunar da sarki a kujerar sarauta,
Och han tog de öfversta öfver hundrade, och de mägtiga, och herrarna i folkena, och allt landsfolket, och hade Konungen neder ifrå Herrans hus; och förde honom in genom den höga porten af Konungshuset, och läto Konungen sätta sig på Konungsstolen.
21 sai dukan mutanen ƙasar suka yi farin ciki. Birnin kuwa ya samu zaman lafiya domin an kashe Ataliya da takobi.
Och allt landsfolket, var gladt, och staden var stilla; men Athalja varat dråpen med svärd.

< 2 Tarihi 23 >