< 2 Tarihi 23 >
1 A shekara ta bakwai Yehohiyada ya nuna ƙarfinsa. Ya yi alkawari da shugabanni na ɗari-ɗari, Azariya ɗan Yeroham, Ishmayel ɗan Yehohanan, Azariya ɗan Obed, Ma’asehiya ɗan Adahiya, da Elishafat ɗan Zikri.
Bet septītā gadā Jojada iedrošinājās un cēla derību ar tiem virsniekiem pār simtiem, Azariju, Jeroama dēlu, un Ismaēli, Johanana dēlu, un Azariju, Obeda dēlu, un Maāseju, Adajas dēlu, un Elizavatu, Sihrus dēlu.
2 Suka ratsa cikin Yahuda suka tattara Lawiyawa da shugabannin iyalan Isra’ilawa daga dukan garuruwa. Sa’ad da suka zo Urushalima,
Un tie gāja pa Jūdu apkārt un sapulcināja Levitus no visām Jūda pilsētām un Israēla tēvu namu virsniekus, un tie sanāca Jeruzālemē.
3 dukan taron suka yi alkawari da sarki a haikalin Allah. Yehohiyada ya ce musu, “Ɗan sarki zai yi mulki yadda Ubangiji ya yi alkawari game da zuriyar Dawuda.
Un visa draudze derēja derību Dieva namā ar ķēniņu, un viņš uz tiem sacīja: redzi, ķēniņa dēlam būs būt par ķēniņu, tā kā Tas Kungs runājis par Dāvida dēliem.
4 Yanzu ga abin da za ku yi, shi ne, kashi ɗaya bisa uku na firistoci da Lawiyawa waɗanda za su yi aiki a Asabbaci su yi tsaro a ƙofofi,
To nu jums būs darīt: Trešdaļa no jums, kam svētdienā krīt kārta, no priesteriem un Levitiem, lai vakti tur pie durvīm.
5 kashi ɗaya bisa ukunku a fadan sarki, kashi ɗaya bisa uku kuma, a Ƙofar Harsashi, sai kuma dukan sauran mutane su kasance a filayen haikalin Ubangiji.
Un trešdaļa lai stāv ķēniņa namā, un trešdaļa pie Pamatu vārtiem. Un visi ļaudis lai stāv Tā Kunga nama pagalmā.
6 Babu wanda zai shiga haikalin Ubangiji sai firistoci da Lawiyawan da suke a aiki; za su iya shiga domin su tsarkaku ne, amma sauran mutane za su kiyaye abin da Ubangiji ya sa su yi.
Bet nevienam nebūs Tā Kunga namā ieiet, kā vien priesteriem un Levitiem, kas kalpo; tie var ieiet, jo tie ir svēti, bet visi ļaudis lai tur Tā Kunga vakti.
7 Lawiyawa za su tsaya kewaye da sarki, kowane mutum da makamansa a hannunsa. Duk wanda ya shiga haikali sai a kashe shi. Ku tsaya kusa da sarki a duk inda ya tafi.”
Un Leviti lai stājās visapkārt ap ķēniņu, ikkatrs ar savu ieroci rokā, un kas namā ieiet, tam būs mirt, bet jums būs būt pie ķēniņa, kad tas ieiet un iziet.
8 Lawiyawa da dukan mutanen Yahuda suka yi yadda Yehohiyada firist ya umarta. Kowanne ya ɗauki mutanensa, waɗanda suke aiki a Asabbaci da waɗanda suka gama aiki, gama Yehohiyada firist bai bar waɗansu ɓangarori ba.
Un Leviti un visa Jūda valsts darīja pēc visa, ko priesteris Jojada bija pavēlējis, un ikviens ņēma savus vīrus, kam svētdienā krita kārta un kam svētdienā kārta beidzās. Jo priesteris Jojada tiem kārtniekiem neļāva aiziet.
9 Sa’an nan ya ba shugabannin māsu da garkuwoyi manya da ƙanana na sarki Dawuda, waɗanda suke cikin haikalin Allah.
Un priesteris Jojada deva tiem virsniekiem pār simtniekiem šķēpus un priekšturamās bruņas un tās bruņas, kas ķēniņam Dāvidam bijušas, kas bija Dieva namā.
10 Ya kuma sa dukan mutane, kowanne da makaminsa a hannunsa, kewaye da sarki, kusa da bagade da kuma haikali, daga gefen kudu zuwa gefen arewa na haikali.
Un viņš nostādīja visus ļaudis, ikvienu ar savu ieroci rokā, no nama labās puses līdz nama kreisai pusei, līdz altārim un namam visapkārt ap ķēniņu.
11 Yehohiyada da’ya’yansa maza suka fitar da ɗan sarki suka sa rawani a kansa; suka miƙa masa alkawarin, suka kuma yi shelarsa a matsayin sarki. Suka shafe shi suka kuma tā da murya suna cewa, “Ran sarki yă daɗe!”
Un tie izveda to ķēniņa dēlu un viņam uzlika kroni un tam deva to liecības grāmatu un to cēla par ķēniņu. Un Jojada ar saviem dēliem to svaidīja un sacīja: lai dzīvo ķēniņš!
12 Sa’ad da Ataliya ta ji surutun mutane suna gudu suna yabon sarki, sai ta tafi wurinsu a haikalin Ubangiji.
Kad nu Atalija to ļaužu kliegšanu dzirdēja, kas bija saskrējuši un ķēniņu slavēja, tad viņa nāca pie tiem ļaudīm Tā Kunga namā.
13 Ta duba, a can kuwa ga sarki, tsaye kusa da ginshiƙinsa a mashigi. Manyan sojoji da masu bushe-bushe suna kusa da sarki, dukan mutanen ƙasar kuwa suna farin ciki suna busa ƙahoni, mawaƙa kuma da kayan kiɗi suna bi da yabo. Sai Ataliya ta yage rigunanta ta yi ihu tana cewa, “Cin amanar ƙasa! Cin amanar ƙasa!”
Un tā skatījās, un redzi, ķēniņš stāvēja savā vietā pie durvīm un lielkungi un taurētāji bija pie ķēniņa, un visi zemes ļaudis priecājās un pūta trumetes, un dziedātāji ar saviem rīkiem pavadīja tās slavas dziesmas. Tad Atalija saplēsa savas drēbes un sacīja: dumpis, dumpis!
14 Yehohiyada firist ya fito da shugabanni waɗanda suke shugabancin rundunar sojoji, ya ce musu, “Ku fitar da ita tsakanin sojoji ku kuma kashe duk wanda ya bi ta da takobi.” Gama firist ya ce, “Kada ku kashe ta a haikalin Ubangiji.”
Bet priesteris Jojada lika iziet tiem virsniekiem pār simtiem, tiem kara vadoņiem, un uz tiem sacīja: izvediet to ārā no nama caur rindām, un kas viņai ies pakaļ, to būs ar zobenu nokaut. Jo tas priesteris bija sacījis: nenokaujiet to Tā Kunga namā.
15 Saboda haka suka kama ta yayinda take kaiwa mashigin Ƙofar Doki a filin fada, a can suka kashe ta.
Un tie tai deva ceļu atkāpdamies uz abējām pusēm, un kad tā ieejot pa tiem zirgu vārtiem nāca ķēniņa namā, tad tie viņu tur nokāva.
16 Sa’an nan Yehohiyada ya yi alkawari cewa shi da mutane da kuma sarki za su zama mutanen Ubangiji.
Un Jojada derēja derību starp sevi un visiem ļaudīm un ķēniņu, ka tie būtu Tā Kunga ļaudis.
17 Dukan mutane suka tafi haikalin Ba’al suka rurrushe shi. Suka farfashe bagadan da gumakan, suka kuma kashe Mattan firist na Ba’al a gaban bagadan.
Tad visi ļaudis gāja Baāla namā un to nolauzīja un viņa altārus, un sadauzīja viņa bildes un nokāva Matanu, Baāla priesteri, altāru priekšā.
18 Sa’an nan Yehohiyada ya sa aikin lura da haikalin Ubangiji a hannuwan firistoci, waɗanda suke Lawiyawan da Dawuda ya ba su aikin haikali don su miƙa hadayun ƙonawa na Ubangiji kamar yadda yake a rubuce a Dokar Musa, da farin ciki da kuma rerawa, kamar yadda Dawuda ya umarta.
Un Jojada iecēla atkal par uzraugiem pie Tā Kunga nama priesterus, tos Levitus, ko Dāvids bija atšķīris Tā Kunga namam, upurēt Tam Kungam dedzināmos upurus, kā Mozus bauslībā rakstīts, ar prieku un ar dziesmām pēc Dāvida likuma.
19 Ya kuma sa matsaran ƙofofi a ƙofofin haikalin Ubangiji don kada wani da ba shi da tsarki yă shiga.
Un viņš iecēla vārtu sargus pie Tā Kunga nama vārtiem, ka neviens tur neieietu, kas kaut kādas lietas dēļ nešķīsts.
20 Ya ɗauki shugabannin ɗari-ɗari, manyan gari, shugabannin mutane da dukan mutanen ƙasar tare da shi ya saukar da sarki daga haikalin Ubangiji. Suka shiga fada ta Ƙofar Bisa suka kuma zaunar da sarki a kujerar sarauta,
Un viņš ņēma tos virsniekus pār simtiem un varenos un ļaužu lielkungus, arī visus zemes ļaudis, un noveda ķēniņu no Tā Kunga nama un gāja caur augšējiem vārtiem ķēniņa namā, un sēdināja ķēniņu uz valstības krēslu.
21 sai dukan mutanen ƙasar suka yi farin ciki. Birnin kuwa ya samu zaman lafiya domin an kashe Ataliya da takobi.
Un visi zemes ļaudis priecājās, un pilsēta norima pēc tam, kad Ataliju bija nokāvuši ar zobenu.