< 2 Tarihi 23 >

1 A shekara ta bakwai Yehohiyada ya nuna ƙarfinsa. Ya yi alkawari da shugabanni na ɗari-ɗari, Azariya ɗan Yeroham, Ishmayel ɗan Yehohanan, Azariya ɗan Obed, Ma’asehiya ɗan Adahiya, da Elishafat ɗan Zikri.
Mais en la septième année Jéhojadah se fortifia, et prit avec soi des centeniers; [savoir] Hazaria fils de Jéroham, Ismahël fils de Jéhohanan, Hazaria fils de Hobed, Mahaséja fils de Hadaja, Elisaphat fils de Zicri, et traita alliance avec eux.
2 Suka ratsa cikin Yahuda suka tattara Lawiyawa da shugabannin iyalan Isra’ilawa daga dukan garuruwa. Sa’ad da suka zo Urushalima,
Et ils firent le tour de Juda, et assemblèrent de toutes les villes de Juda les Lévites, et les Chefs des pères d'Israël, et vinrent à Jérusalem.
3 dukan taron suka yi alkawari da sarki a haikalin Allah. Yehohiyada ya ce musu, “Ɗan sarki zai yi mulki yadda Ubangiji ya yi alkawari game da zuriyar Dawuda.
Et toute cette assemblée traita alliance avec le Roi dans la maison de Dieu, et [Jéhojadah] leur dit: Voici, le fils du Roi régnera selon que l'Eternel en a parlé touchant les fils de David.
4 Yanzu ga abin da za ku yi, shi ne, kashi ɗaya bisa uku na firistoci da Lawiyawa waɗanda za su yi aiki a Asabbaci su yi tsaro a ƙofofi,
C'est ici [donc] ce que vous ferez: La troisième partie de ceux d'entre vous qui entrerez en semaine, tant des Sacrificateurs, que des Lévites, sera à la porte de Sippim.
5 kashi ɗaya bisa ukunku a fadan sarki, kashi ɗaya bisa uku kuma, a Ƙofar Harsashi, sai kuma dukan sauran mutane su kasance a filayen haikalin Ubangiji.
Et la troisième partie se tiendra vers la maison du Roi; et la troisième partie à la porte du fondement; et que tout le peuple soit dans les parvis de la maison de l'Eternel.
6 Babu wanda zai shiga haikalin Ubangiji sai firistoci da Lawiyawan da suke a aiki; za su iya shiga domin su tsarkaku ne, amma sauran mutane za su kiyaye abin da Ubangiji ya sa su yi.
Que nul n'entre dans la maison de l'Eternel, que les Sacrificateurs et les Lévites servants; ceux-ci y entreront, parce qu'ils sont sanctifiés; et le reste du peuple fera la garde de l'Eternel.
7 Lawiyawa za su tsaya kewaye da sarki, kowane mutum da makamansa a hannunsa. Duk wanda ya shiga haikali sai a kashe shi. Ku tsaya kusa da sarki a duk inda ya tafi.”
Et ces Lévites-là environneront le Roi tout autour, ayant chacun ses armes en sa main; mais que celui qui entrera dans la maison, soit mis à mort; et tenez-vous auprès du Roi quand il sortira et quand il entrera.
8 Lawiyawa da dukan mutanen Yahuda suka yi yadda Yehohiyada firist ya umarta. Kowanne ya ɗauki mutanensa, waɗanda suke aiki a Asabbaci da waɗanda suka gama aiki, gama Yehohiyada firist bai bar waɗansu ɓangarori ba.
Les Lévites donc et tous ceux de Juda firent tout ce que Jéhojadah le Sacrificateur avait commandé, et prirent chacun ses gens, tant ceux qui entraient en semaine que ceux qui sortaient de semaine; car Jéhojadah le Sacrificateur n'avait point donné congé aux départements.
9 Sa’an nan ya ba shugabannin māsu da garkuwoyi manya da ƙanana na sarki Dawuda, waɗanda suke cikin haikalin Allah.
Et Jéhojadah le sacrificateur donna aux centeniers des hallebardes, des boucliers, et des rondelles, qui avaient été au Roi David, et qui étaient dans la maison de Dieu.
10 Ya kuma sa dukan mutane, kowanne da makaminsa a hannunsa, kewaye da sarki, kusa da bagade da kuma haikali, daga gefen kudu zuwa gefen arewa na haikali.
Et il rangea tout le peuple, tout autour du Roi; chacun tenant ses armes en sa main, depuis le côté droit du Temple jusqu'au côté gauche du Temple, tant pour l'autel, que pour le Temple.
11 Yehohiyada da’ya’yansa maza suka fitar da ɗan sarki suka sa rawani a kansa; suka miƙa masa alkawarin, suka kuma yi shelarsa a matsayin sarki. Suka shafe shi suka kuma tā da murya suna cewa, “Ran sarki yă daɗe!”
Alors on amena le fils du Roi, et on mit sur lui la couronne et le témoignage, et ils l'établirent Roi; et Jéhojadah et ses fils l'oignirent, et dirent: Vive le Roi!
12 Sa’ad da Ataliya ta ji surutun mutane suna gudu suna yabon sarki, sai ta tafi wurinsu a haikalin Ubangiji.
Et Hathalie entendant le bruit du peuple qui courait, et qui chantait les louanges [de Dieu] autour du Roi, vint vers le peuple en la maison de l'Eternel.
13 Ta duba, a can kuwa ga sarki, tsaye kusa da ginshiƙinsa a mashigi. Manyan sojoji da masu bushe-bushe suna kusa da sarki, dukan mutanen ƙasar kuwa suna farin ciki suna busa ƙahoni, mawaƙa kuma da kayan kiɗi suna bi da yabo. Sai Ataliya ta yage rigunanta ta yi ihu tana cewa, “Cin amanar ƙasa! Cin amanar ƙasa!”
Et elle regarda, et voilà, le Roi était près de sa colonne à l'entrée, et les capitaines, et les trompettes étaient près du Roi, et tout le peuple du pays était en joie, et on sonnait des trompettes; les chantres aussi [chantaient] avec des instruments de musique, et montraient comment il fallait chanter les louanges [de Dieu]; et sur cela Hathalie déchira ses vêtements, et dit: Conjuration! conjuration!
14 Yehohiyada firist ya fito da shugabanni waɗanda suke shugabancin rundunar sojoji, ya ce musu, “Ku fitar da ita tsakanin sojoji ku kuma kashe duk wanda ya bi ta da takobi.” Gama firist ya ce, “Kada ku kashe ta a haikalin Ubangiji.”
Alors le Sacrificateur Jéhojadah fit sortir les centeniers, qui avaient la charge de l'armée, et leur dit: Menez-la hors des rangs; et que celui qui la suivra, soit mis à mort par l'épée; car le Sacrificateur avait dit: Ne la mettez point à mort dans la maison de l'Eternel.
15 Saboda haka suka kama ta yayinda take kaiwa mashigin Ƙofar Doki a filin fada, a can suka kashe ta.
Ils lui firent donc place; et elle s'en retourna en la maison du Roi par l'entrée de la porte des chevaux, et ils la firent mourir là.
16 Sa’an nan Yehohiyada ya yi alkawari cewa shi da mutane da kuma sarki za su zama mutanen Ubangiji.
Et Jéhojadah, tout le peuple, et le Roi traitèrent cette alliance, qu'ils seraient le peuple de l'Eternel.
17 Dukan mutane suka tafi haikalin Ba’al suka rurrushe shi. Suka farfashe bagadan da gumakan, suka kuma kashe Mattan firist na Ba’al a gaban bagadan.
Alors tout le peuple entra dans la maison de Bahal, et ils la démolirent; ils brisèrent ses autels et ses images, et tuèrent Mattan Sacrificateur de Bahal, devant les autels.
18 Sa’an nan Yehohiyada ya sa aikin lura da haikalin Ubangiji a hannuwan firistoci, waɗanda suke Lawiyawan da Dawuda ya ba su aikin haikali don su miƙa hadayun ƙonawa na Ubangiji kamar yadda yake a rubuce a Dokar Musa, da farin ciki da kuma rerawa, kamar yadda Dawuda ya umarta.
Jéhojadah rétablit aussi les charges de la maison de l'Eternel, entre les mains des Sacrificateurs Lévites, que David avait distribués pour la maison de l'Eternel, afin qu'ils offrissent les holocaustes à l'Eternel, ainsi qu'il est écrit dans la Loi de Moïse, avec joie et avec des cantiques, selon la disposition qui en avait été faite par David.
19 Ya kuma sa matsaran ƙofofi a ƙofofin haikalin Ubangiji don kada wani da ba shi da tsarki yă shiga.
Il établit aussi des portiers aux portes de la maison de l'Eternel; afin qu'aucune personne souillée, pour quelque chose que ce fût, n'y entrât.
20 Ya ɗauki shugabannin ɗari-ɗari, manyan gari, shugabannin mutane da dukan mutanen ƙasar tare da shi ya saukar da sarki daga haikalin Ubangiji. Suka shiga fada ta Ƙofar Bisa suka kuma zaunar da sarki a kujerar sarauta,
Il prit [ensuite] les centeniers, les hommes les plus considérables, ceux qui étaient établis en autorité sur le peuple, et tout le peuple du pays; et il fit descendre le Roi de la maison de l'Eternel, et ils entrèrent par le milieu de la haute porte dans la maison du Roi; puis ils firent asseoir le Roi sur le trône Royal.
21 sai dukan mutanen ƙasar suka yi farin ciki. Birnin kuwa ya samu zaman lafiya domin an kashe Ataliya da takobi.
Et tout le peuple du pays fut en joie, et la ville demeura tranquille, bien qu'on eût mis à mort Hathalie par l'épée.

< 2 Tarihi 23 >