< 2 Tarihi 23 >

1 A shekara ta bakwai Yehohiyada ya nuna ƙarfinsa. Ya yi alkawari da shugabanni na ɗari-ɗari, Azariya ɗan Yeroham, Ishmayel ɗan Yehohanan, Azariya ɗan Obed, Ma’asehiya ɗan Adahiya, da Elishafat ɗan Zikri.
And in the seventh year hath Jehoiada strengthened himself, and taketh the heads of the hundreds, even Azariah son of Jeroham, and Ishmael son of Jehohanan, and Azariah son of Obed, and Maaseiah son of Adaiah, and Elishaphat son of Zichri, with him into covenant.
2 Suka ratsa cikin Yahuda suka tattara Lawiyawa da shugabannin iyalan Isra’ilawa daga dukan garuruwa. Sa’ad da suka zo Urushalima,
And they go round about in Judah, and gather the Levites out of all the cities of Judah, and heads of the fathers of Israel, and come in unto Jerusalem,
3 dukan taron suka yi alkawari da sarki a haikalin Allah. Yehohiyada ya ce musu, “Ɗan sarki zai yi mulki yadda Ubangiji ya yi alkawari game da zuriyar Dawuda.
and all the assembly make a covenant in the house of God with the king, and he saith to them, 'Lo, the son of the king doth reign, as Jehovah spake concerning the sons of David.
4 Yanzu ga abin da za ku yi, shi ne, kashi ɗaya bisa uku na firistoci da Lawiyawa waɗanda za su yi aiki a Asabbaci su yi tsaro a ƙofofi,
'This [is] the thing that ye do: The third of you, going in on the sabbath, of the priests, and of the Levites, [are] for gatekeepers of the thresholds,
5 kashi ɗaya bisa ukunku a fadan sarki, kashi ɗaya bisa uku kuma, a Ƙofar Harsashi, sai kuma dukan sauran mutane su kasance a filayen haikalin Ubangiji.
and the third [are] at the house of the king, and the third at the gate of the foundation, and all the people [are] in the courts of the house of Jehovah.
6 Babu wanda zai shiga haikalin Ubangiji sai firistoci da Lawiyawan da suke a aiki; za su iya shiga domin su tsarkaku ne, amma sauran mutane za su kiyaye abin da Ubangiji ya sa su yi.
'And none doth enter the house of Jehovah except the priests, and those ministering of the Levites (they go in for they [are] holy), and all the people keep the watch of Jehovah:
7 Lawiyawa za su tsaya kewaye da sarki, kowane mutum da makamansa a hannunsa. Duk wanda ya shiga haikali sai a kashe shi. Ku tsaya kusa da sarki a duk inda ya tafi.”
and the Levites have compassed the king round about, each with his weapon in his hand, and he who hath gone in unto the house is put to death; and be ye with the king in his coming in and in his going out.'
8 Lawiyawa da dukan mutanen Yahuda suka yi yadda Yehohiyada firist ya umarta. Kowanne ya ɗauki mutanensa, waɗanda suke aiki a Asabbaci da waɗanda suka gama aiki, gama Yehohiyada firist bai bar waɗansu ɓangarori ba.
And the Levites and all Judah do according to all that Jehoiada the priest hath commanded, and take each his men going in on the sabbath, with those going out on the sabbath, for Jehoiada the priest hath not let away the courses.
9 Sa’an nan ya ba shugabannin māsu da garkuwoyi manya da ƙanana na sarki Dawuda, waɗanda suke cikin haikalin Allah.
And Jehoiada the priest giveth to the heads of the hundreds the spears, and the shields, and the bucklers that [are] king David's, that [are] in the house of God;
10 Ya kuma sa dukan mutane, kowanne da makaminsa a hannunsa, kewaye da sarki, kusa da bagade da kuma haikali, daga gefen kudu zuwa gefen arewa na haikali.
and he stationeth the whole of the people, and each his dart in his hand, from the right shoulder of the house unto the left shoulder of the house, at the altar, and at the house, by the king, round about.
11 Yehohiyada da’ya’yansa maza suka fitar da ɗan sarki suka sa rawani a kansa; suka miƙa masa alkawarin, suka kuma yi shelarsa a matsayin sarki. Suka shafe shi suka kuma tā da murya suna cewa, “Ran sarki yă daɗe!”
And they bring out the son of the king, and put upon him the crown, and the testimony, and cause him to reign; and Jehoiada and his sons anoint him, and say, 'Let the king live!'
12 Sa’ad da Ataliya ta ji surutun mutane suna gudu suna yabon sarki, sai ta tafi wurinsu a haikalin Ubangiji.
And Athaliah heareth the voice of the people who are running, and who are praising the king, and she cometh in unto the people in the house of Jehovah,
13 Ta duba, a can kuwa ga sarki, tsaye kusa da ginshiƙinsa a mashigi. Manyan sojoji da masu bushe-bushe suna kusa da sarki, dukan mutanen ƙasar kuwa suna farin ciki suna busa ƙahoni, mawaƙa kuma da kayan kiɗi suna bi da yabo. Sai Ataliya ta yage rigunanta ta yi ihu tana cewa, “Cin amanar ƙasa! Cin amanar ƙasa!”
and seeth, and lo, the king is standing by his pillar in the entrance, and the heads, and the trumpets [are] by the king, and all the people of the land rejoicing and shouting with trumpets, and the singers with instruments of song, and the teachers, to praise, and Athaliah rendeth her garments, and saith, 'Conspiracy, conspiracy.'
14 Yehohiyada firist ya fito da shugabanni waɗanda suke shugabancin rundunar sojoji, ya ce musu, “Ku fitar da ita tsakanin sojoji ku kuma kashe duk wanda ya bi ta da takobi.” Gama firist ya ce, “Kada ku kashe ta a haikalin Ubangiji.”
And Jehoiada the priest bringeth out the heads of the hundreds, inspectors of the force, and saith unto them, 'Take her out from within the rows, and he who hath gone after her is put to death by the sword;' for the priest said, 'Put her not to death [in] the house of Jehovah.'
15 Saboda haka suka kama ta yayinda take kaiwa mashigin Ƙofar Doki a filin fada, a can suka kashe ta.
And they make for her sides, and she cometh in unto the entrance of the gate of the horses at the house of the king, and they put her to death there.
16 Sa’an nan Yehohiyada ya yi alkawari cewa shi da mutane da kuma sarki za su zama mutanen Ubangiji.
And Jehoiada maketh a covenant between him, and between all the people, and between the king, to be for a people to Jehovah;
17 Dukan mutane suka tafi haikalin Ba’al suka rurrushe shi. Suka farfashe bagadan da gumakan, suka kuma kashe Mattan firist na Ba’al a gaban bagadan.
and all the people enter the house of Baal, and break it down, yea, his altars and his images they have broken, and Mattan priest of Baal they have slain before the altars.
18 Sa’an nan Yehohiyada ya sa aikin lura da haikalin Ubangiji a hannuwan firistoci, waɗanda suke Lawiyawan da Dawuda ya ba su aikin haikali don su miƙa hadayun ƙonawa na Ubangiji kamar yadda yake a rubuce a Dokar Musa, da farin ciki da kuma rerawa, kamar yadda Dawuda ya umarta.
And Jehoiada putteth the offices of the house of Jehovah into the hand of the priests the Levites whom David had apportioned over the house of Jehovah, to cause to ascend the burnt-offerings of Jehovah, as written in the law of Moses, with joy, and with singing, by the hands of David;
19 Ya kuma sa matsaran ƙofofi a ƙofofin haikalin Ubangiji don kada wani da ba shi da tsarki yă shiga.
and he stationeth the gatekeepers over the gates of the house of Jehovah, and the unclean in anything doth not go in.
20 Ya ɗauki shugabannin ɗari-ɗari, manyan gari, shugabannin mutane da dukan mutanen ƙasar tare da shi ya saukar da sarki daga haikalin Ubangiji. Suka shiga fada ta Ƙofar Bisa suka kuma zaunar da sarki a kujerar sarauta,
And he taketh the heads of the hundreds, and the honourable ones, and the rulers among the people, and all the people of the land, and bringeth down the king from the house of Jehovah, and they come in through the high gate to the house of the king, and cause the king to sit on the throne of the kingdom.
21 sai dukan mutanen ƙasar suka yi farin ciki. Birnin kuwa ya samu zaman lafiya domin an kashe Ataliya da takobi.
And all the people of the land rejoice, and the city hath been quiet, and Athaliah they have put to death by the sword.

< 2 Tarihi 23 >