< 2 Tarihi 22 >
1 Mutanen Urushalima suka mai da Ahaziya, autan Yehoram, sarki a madadinsa, da yake’yan hari, waɗanda suka zo tare da Larabawa cikin sansani, sun kashe dukan manyan’ya’yansa. Saboda haka Ahaziya ɗan Yeroham sarkin Yahuda ya fara mulki.
Och de i Jerusalem gjorde till Konung Ahasia hans yngsta son, i hans stad; förty krigsfolket, som utaf de Araber med här kommo, hade de första alla ihjälslagit; derföre vardt Ahasia Konung, Jorams son, Juda Konungs.
2 Ahaziya yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara guda. Sunan mahaifiyarsa Ataliya ce, jikanyar Omri.
Tu och fyratio år gammal var Ahasia, då han Konung vardt, och regerade ett år i Jerusalem. Hans moder het Athalja, Amri dotter.
3 Shi ma ya yi tafiya a hanyoyin gidan Ahab, gama mahaifiyarsa ta ƙarfafa shi yă yi abin da ba shi da kyau.
Han vandrade ock uti Achabs hus vägar; ty hans moder höll honom dertill, att han skulle göra det ondt var.
4 Ya aikata mugayen ayyuka a gaban Ubangiji, yadda gidan Ahab ta yi, gama bayan mutuwar mahaifinsa, sai gidan Ahab ta zama masu ba shi shawara, shawarar da ta kai shi ga lalacewa.
Derföre gjorde han det Herranom icke behagade, såsom Achabs hus; ty de voro hans rådgifvare efter hans faders död, så att de förderfvade honom.
5 Ya kuma bi shawararsu sa’ad da ya tafi tare da Yoram ɗan Ahab sarkin Isra’ila don yă yaƙi Hazayel sarkin Aram a Ramot Gileyad. Sai Arameyawa suka yi wa Yoram rauni;
Och han vandrade efter deras råd, och han drog bort med Joram, Achabs son, Israels Konung, i strid, till Ramoth i Gilead, emot Hasael, Konungen i Syrien. Men de i Rama slogo Joram;
6 saboda haka ya dawo Yezireyel don yă yi jinyar raunin da suka yi masa a Rama cikin yaƙinsa da Hazayel sarkin Aram. Sa’an nan Azariya ɗan Yehoram sarkin Yahuda ya gangara zuwa Yezireyel don yă ga Yoram ɗan Ahab domin ya ji rauni.
Så att han omvände, till att låta läka sig i Jisreel; förty han hade sår, som han fått hade i Rama, då han stridde med Hasael, Konungen i Syrien. Och Asaria, Jorams son, Juda Konungs, for ned till att bese Joram, Achabs son, i Jisreel, som krank låg.
7 Ta wurin ziyarar Yoram, Allah ya kawo fāɗuwar Ahaziya. Sa’ad da Ahaziya ya iso, ya tafi tare da Yoram domin yă sadu da Yehu ɗan Nimshi, wanda Ubangiji ya shafe don yă hallaka gidan Ahab.
Ty den ofärden var så af Gudi Ahasia tillfogad, att han skulle komma till Joram, och så med Joram utdraga emot Jehu, Nimsi son, hvilken Herren smort hade, till att utrota Achabs hus.
8 Yayinda Yehu yake hukunta wa gidan Ahab, sai ya sami fadawan Yahuda da kuma’ya’yan dangin Ahaziya maza, waɗanda suke yi wa Ahaziya hidima, sai ya kashe su.
Då nu Jehu höll uppå att straffa Achabs hus, fann han några öfverstar af Juda, och Ahasia bröders barn, som tjente, och drap dem.
9 Ya kuma sa aka nemi Ahaziya. Aka kamo shi sa’ad da ya ɓuya a Samariya, suka kawo shi wurin Yehu, suka kashe shi, suka binne shi, gama sun ce, “Shi jikan Yehoshafat ne, wanda ya nemi Ubangiji da dukan zuciyarsa.” Ta haka babu wani a gidan Ahaziya da yake da ƙarfin cin gaba da mulkin.
Och han sökte Ahasia, och fick honom fatt, der han sig undstungit hade i Samarien; och han vardt hafder fram för Jehu. Han drap honom, och man begrof honom; ty de sade: Han är Josaphats son, hvilken efter Herran sökte af allt hjerta. Och var sedan ingen qvar utaf Ahasia huse, som Konung kunde varda.
10 Sa’ad da Ataliya mahaifiyar Ahaziya ta ga cewa ɗanta ya mutu, sai ta tashi ta hallaka dukan’yan gidan sarautar Yahuda.
Då nu Athalja, Ahasia moder, såg att hennes son död var, stod hon upp, och förgjorde all Konungslig säd i Juda hus.
11 Amma Yehosheba,’yar Sarki Yehoram, ta ɗauki Yowash ɗan Ahaziya ta sace shi daga cikin’ya’yan gidan sarauta waɗanda ake shiri a kashe, ta sa shi tare da mai renonsa a ɗakin kwana. Haka fa, Yehosheba’yar sarki Yoram, matar Yehohiyada firist, ta yi, gama ita’yar’uwar Ahaziya ce, ta ɓoye Yowash don kada Ataliya tă kashe shi.
Men Josabeath, Konungens dotter, tog Johas, Ahasia son, och stal honom undan ibland Konungsbarnen, som dräpne vordo, och lät honom med hans ammo uti en sängakammar. Alltså fördolde honom för Athalja Josabeath, Konung Jorams dotter, Prestens Jojada hustru; ty hon var Ahasia syster; att han icke dräpen vardt.
12 Ya kasance a ɓoye tare da su a haikalin Allah shekara shida, yayinda Ataliya take mulkin ƙasar.
Och han var med dem i Guds hus fördold i sex år, medan Athalja regerade i landena.