< 2 Tarihi 22 >

1 Mutanen Urushalima suka mai da Ahaziya, autan Yehoram, sarki a madadinsa, da yake’yan hari, waɗanda suka zo tare da Larabawa cikin sansani, sun kashe dukan manyan’ya’yansa. Saboda haka Ahaziya ɗan Yeroham sarkin Yahuda ya fara mulki.
Potem mieszkańcy Jerozolimy ustanowili Achazjasza, jego najmłodszego syna, królem na jego miejscu, gdyż wszystkich starszych [jego braci] wymordowała zgraja, która razem z Arabami wtargnęła do obozu. Tak więc [zaczął] królować Achazjasz, syn Jorama, króla Judy.
2 Ahaziya yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara guda. Sunan mahaifiyarsa Ataliya ce, jikanyar Omri.
Achazjasz [miał] czterdzieści dwa lata, kiedy [zaczął] królować, i królował jeden rok w Jerozolimie. Jego matka [miała] na imię Atalia [i była] córką Omriego.
3 Shi ma ya yi tafiya a hanyoyin gidan Ahab, gama mahaifiyarsa ta ƙarfafa shi yă yi abin da ba shi da kyau.
On również kroczył drogami domu Achaba, bo jego matka radziła mu, aby postępował niegodziwie.
4 Ya aikata mugayen ayyuka a gaban Ubangiji, yadda gidan Ahab ta yi, gama bayan mutuwar mahaifinsa, sai gidan Ahab ta zama masu ba shi shawara, shawarar da ta kai shi ga lalacewa.
Czynił więc to, co złe w oczach PANA, tak jak dom Achaba. Oni bowiem na jego zgubę byli jego doradcami po śmierci ojca.
5 Ya kuma bi shawararsu sa’ad da ya tafi tare da Yoram ɗan Ahab sarkin Isra’ila don yă yaƙi Hazayel sarkin Aram a Ramot Gileyad. Sai Arameyawa suka yi wa Yoram rauni;
Chodził za ich radą i wyruszył z Joramem, synem Achaba, królem Izraela, na wojnę przeciw Chazaelowi, królowi Syrii, do Ramot-Gilead. Tam Syryjczycy zranili Jorama.
6 saboda haka ya dawo Yezireyel don yă yi jinyar raunin da suka yi masa a Rama cikin yaƙinsa da Hazayel sarkin Aram. Sa’an nan Azariya ɗan Yehoram sarkin Yahuda ya gangara zuwa Yezireyel don yă ga Yoram ɗan Ahab domin ya ji rauni.
Wrócił więc, aby się leczyć w Jizreel z ran, które zadano mu w Rama, gdy walczył z Chazaelem, królem Syrii. Wtedy Azariasz, syn Jorama, króla Judy, przybył do Jizreel, aby odwiedzić Jorama, syna Achaba, bo był chory.
7 Ta wurin ziyarar Yoram, Allah ya kawo fāɗuwar Ahaziya. Sa’ad da Ahaziya ya iso, ya tafi tare da Yoram domin yă sadu da Yehu ɗan Nimshi, wanda Ubangiji ya shafe don yă hallaka gidan Ahab.
A to, że przybył do Jorama, było od Boga na zgubę Achazjasza. Kiedy bowiem przybył, wyjechał z Joramem przeciw Jehu, synowi Nimsziego, którego PAN namaścił, aby wytracić dom Achaba.
8 Yayinda Yehu yake hukunta wa gidan Ahab, sai ya sami fadawan Yahuda da kuma’ya’yan dangin Ahaziya maza, waɗanda suke yi wa Ahaziya hidima, sai ya kashe su.
I kiedy Jehu dokonywał sądu nad domem Achaba, znalazł [niektórych] książąt Judy i synów braci Achazjasza, którzy służyli Achazjaszowi, i zabił ich.
9 Ya kuma sa aka nemi Ahaziya. Aka kamo shi sa’ad da ya ɓuya a Samariya, suka kawo shi wurin Yehu, suka kashe shi, suka binne shi, gama sun ce, “Shi jikan Yehoshafat ne, wanda ya nemi Ubangiji da dukan zuciyarsa.” Ta haka babu wani a gidan Ahaziya da yake da ƙarfin cin gaba da mulkin.
Potem szukał Achazjasza i pojmano go, gdy ukrywał się w Samarii. Przyprowadzili go do Jehu i zabili. Potem pogrzebali go, bo mówili: To jest syn Jehoszafata, który szukał PANA całym swoim sercem. I tak już nie było [nikogo] w domu Achazjasza, kto by mógł przejąć królestwo.
10 Sa’ad da Ataliya mahaifiyar Ahaziya ta ga cewa ɗanta ya mutu, sai ta tashi ta hallaka dukan’yan gidan sarautar Yahuda.
Kiedy Atalia, matka Achazjasza, zobaczyła, że jej syn umarł, wstała i zgładziła całe potomstwo królewskie z domu Judy.
11 Amma Yehosheba,’yar Sarki Yehoram, ta ɗauki Yowash ɗan Ahaziya ta sace shi daga cikin’ya’yan gidan sarauta waɗanda ake shiri a kashe, ta sa shi tare da mai renonsa a ɗakin kwana. Haka fa, Yehosheba’yar sarki Yoram, matar Yehohiyada firist, ta yi, gama ita’yar’uwar Ahaziya ce, ta ɓoye Yowash don kada Ataliya tă kashe shi.
Ale Jehoszaba, córka króla, wzięła Joasza, syna Achazjasza, wykradła go spośród synów króla, których [potem] zabito, i ukryła go wraz z jego mamką w pokoju sypialnym. Tak to ukryła go Jehoszaba, córka króla Jorama, żona kapłana Jehojady i siostra Achazjasza, przed Atalią, aby ta go nie zabiła.
12 Ya kasance a ɓoye tare da su a haikalin Allah shekara shida, yayinda Ataliya take mulkin ƙasar.
I przebywał z nimi ukryty w domu Bożym przez sześć lat, podczas gdy Atalia królowała nad ziemią.

< 2 Tarihi 22 >