< 2 Tarihi 22 >

1 Mutanen Urushalima suka mai da Ahaziya, autan Yehoram, sarki a madadinsa, da yake’yan hari, waɗanda suka zo tare da Larabawa cikin sansani, sun kashe dukan manyan’ya’yansa. Saboda haka Ahaziya ɗan Yeroham sarkin Yahuda ya fara mulki.
Et les habitants de Jérusalem firent Achazia, son fils cadet, roi en sa place; car tous les aînés avaient été tués par la horde venue avec les Arabes au camp. Ainsi devint roi Achazia, fils de Joram, roi de Juda.
2 Ahaziya yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara guda. Sunan mahaifiyarsa Ataliya ce, jikanyar Omri.
Achazia avait quarante-deux ans à son avènement, et il régna un an à Jérusalem. Or le nom de sa mère était Athalie, fille d'Omri.
3 Shi ma ya yi tafiya a hanyoyin gidan Ahab, gama mahaifiyarsa ta ƙarfafa shi yă yi abin da ba shi da kyau.
Lui aussi marcha sur les errements de la maison d'Achab, car sa mère était sa conseillère d'impiété.
4 Ya aikata mugayen ayyuka a gaban Ubangiji, yadda gidan Ahab ta yi, gama bayan mutuwar mahaifinsa, sai gidan Ahab ta zama masu ba shi shawara, shawarar da ta kai shi ga lalacewa.
Et il fit ce qui est mal aux yeux de l'Éternel, comme la maison d'Achab, car là furent ses conseillers après la mort de son père, pour sa perte.
5 Ya kuma bi shawararsu sa’ad da ya tafi tare da Yoram ɗan Ahab sarkin Isra’ila don yă yaƙi Hazayel sarkin Aram a Ramot Gileyad. Sai Arameyawa suka yi wa Yoram rauni;
Ce fut aussi d'après leur conseil qu'il se conduisit, et qu'il marcha avec Joram, fils d'Achab, roi d'Israël, à l'attaque de Hazaël, roi de Syrie, à Ramoth en Galaad. Et les Syriens blessèrent Joram,
6 saboda haka ya dawo Yezireyel don yă yi jinyar raunin da suka yi masa a Rama cikin yaƙinsa da Hazayel sarkin Aram. Sa’an nan Azariya ɗan Yehoram sarkin Yahuda ya gangara zuwa Yezireyel don yă ga Yoram ɗan Ahab domin ya ji rauni.
qui alors rebroussa pour se faire traiter à Jizréel des blessures qu'il avait reçues à Rama, lorsqu'il se battait contre Hazaël, roi de Syrie. Et Azaria, fils de Joram, roi de Juda, descendit pour visiter Joram, fils d'Achab, à Jizréel, parce qu'il était malade.
7 Ta wurin ziyarar Yoram, Allah ya kawo fāɗuwar Ahaziya. Sa’ad da Ahaziya ya iso, ya tafi tare da Yoram domin yă sadu da Yehu ɗan Nimshi, wanda Ubangiji ya shafe don yă hallaka gidan Ahab.
Et c'est par la volonté de Dieu qu'Achazia se perdit en venant auprès de Joram; et à son arrivée il s'achemina avec Joram, au-devant de Jéhu, fils de Nimsi, que l'Éternel avait oint pour extirper la maison d'Achab.
8 Yayinda Yehu yake hukunta wa gidan Ahab, sai ya sami fadawan Yahuda da kuma’ya’yan dangin Ahaziya maza, waɗanda suke yi wa Ahaziya hidima, sai ya kashe su.
Et comme Jéhu faisait justice de la maison d'Achab, il atteignit les chefs de Juda et les fils des frères d'Achab, qui étaient au service d'Achazia, et les massacra.
9 Ya kuma sa aka nemi Ahaziya. Aka kamo shi sa’ad da ya ɓuya a Samariya, suka kawo shi wurin Yehu, suka kashe shi, suka binne shi, gama sun ce, “Shi jikan Yehoshafat ne, wanda ya nemi Ubangiji da dukan zuciyarsa.” Ta haka babu wani a gidan Ahaziya da yake da ƙarfin cin gaba da mulkin.
Et il chercha Achazia, qui fut pris comme il se cachait dans Samarie, et on l'emmena à Jéhu, et on le fit mourir, et on lui donna la sépulture; car ils disaient: C'est le fils de Josaphat qui cherchait l'Éternel de tout son cœur. Et dans la maison d'Achazia il n'y avait personne d'apte à régner.
10 Sa’ad da Ataliya mahaifiyar Ahaziya ta ga cewa ɗanta ya mutu, sai ta tashi ta hallaka dukan’yan gidan sarautar Yahuda.
Mais Athalie, mère d'Achazia, voyant son fils mort, se mit en devoir de détruire toute la race royale de la maison de Juda.
11 Amma Yehosheba,’yar Sarki Yehoram, ta ɗauki Yowash ɗan Ahaziya ta sace shi daga cikin’ya’yan gidan sarauta waɗanda ake shiri a kashe, ta sa shi tare da mai renonsa a ɗakin kwana. Haka fa, Yehosheba’yar sarki Yoram, matar Yehohiyada firist, ta yi, gama ita’yar’uwar Ahaziya ce, ta ɓoye Yowash don kada Ataliya tă kashe shi.
Alors Josabeath, fille de roi, prit Joas, fils d'Achazia, et parvint à le soustraire du milieu des fils du roi qu'on mettait à mort, et le logea lui et sa nourrice dans la salle des lits; ainsi le cacha Josabeath, fille du roi Joram, femme de Joiada, le Prêtre (car elle était sœur d'Achazia) aux regards d'Athalie, afin que celle-ci ne le fît pas mourir;
12 Ya kasance a ɓoye tare da su a haikalin Allah shekara shida, yayinda Ataliya take mulkin ƙasar.
et il fut avec eux dans la maison de Dieu, caché pendant six ans. Cependant Athalie régissait le pays.

< 2 Tarihi 22 >