< 2 Tarihi 22 >

1 Mutanen Urushalima suka mai da Ahaziya, autan Yehoram, sarki a madadinsa, da yake’yan hari, waɗanda suka zo tare da Larabawa cikin sansani, sun kashe dukan manyan’ya’yansa. Saboda haka Ahaziya ɗan Yeroham sarkin Yahuda ya fara mulki.
Og Indbyggerne i Jerusalem gjorde Ahasia, hans yngste Søn, til Konge i hans Sted; thi den Trop, som kom med Araberne til Lejren, havde ihjelslaaet alle de første; og Ahasia, Jorams Søn, regerede søm Konge i Juda.
2 Ahaziya yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara guda. Sunan mahaifiyarsa Ataliya ce, jikanyar Omri.
Ahasia var to og fyrretyve Aar gammel, der han blev Konge, og regerede et Aar i Jerusalem, og hans Moders Navn var Athalia, Omris (Søns) Datter.
3 Shi ma ya yi tafiya a hanyoyin gidan Ahab, gama mahaifiyarsa ta ƙarfafa shi yă yi abin da ba shi da kyau.
Og han vandrede i Akabs Hus's Veje; thi hans Moder var hans Raadgiver til at handle ugudeligt.
4 Ya aikata mugayen ayyuka a gaban Ubangiji, yadda gidan Ahab ta yi, gama bayan mutuwar mahaifinsa, sai gidan Ahab ta zama masu ba shi shawara, shawarar da ta kai shi ga lalacewa.
Og han gjorde det, som var ondt for Herrens Øjne ligesom Akabs Hus; thi de vare hans Raadgivere efter hans Faders Død til Fordærvelse for ham.
5 Ya kuma bi shawararsu sa’ad da ya tafi tare da Yoram ɗan Ahab sarkin Isra’ila don yă yaƙi Hazayel sarkin Aram a Ramot Gileyad. Sai Arameyawa suka yi wa Yoram rauni;
Han vandrede ogsaa efter deres Raad og drog med Joram, Israels Konge, Akabs Søn, i Krig imod Hasael, Kongen af Syrien, imod Ramoth i Gilead; men Syrerne sloge Joram.
6 saboda haka ya dawo Yezireyel don yă yi jinyar raunin da suka yi masa a Rama cikin yaƙinsa da Hazayel sarkin Aram. Sa’an nan Azariya ɗan Yehoram sarkin Yahuda ya gangara zuwa Yezireyel don yă ga Yoram ɗan Ahab domin ya ji rauni.
Og han vendte tilbage for at lade sig læge i Jisreel af de Saar, som de havde slaget ham ved Rama, der han stred med Hasael, Kongen af Syrien; og Asaria, Jorams Søn, Judas Konge, drog ned at besøge Joram, Akabs Søn, i Jisreel, thi han laa syg.
7 Ta wurin ziyarar Yoram, Allah ya kawo fāɗuwar Ahaziya. Sa’ad da Ahaziya ya iso, ya tafi tare da Yoram domin yă sadu da Yehu ɗan Nimshi, wanda Ubangiji ya shafe don yă hallaka gidan Ahab.
Og af Gud var Ahasias Undergang, saa at han kom til Joram; thi der han kom, da drog han ud med Joram imod Jehu, Nimsis Søn, som Herren havde salvet til at udrydde Akabs Hus.
8 Yayinda Yehu yake hukunta wa gidan Ahab, sai ya sami fadawan Yahuda da kuma’ya’yan dangin Ahaziya maza, waɗanda suke yi wa Ahaziya hidima, sai ya kashe su.
Og det skete, da Dommen udførtes af Jehu imod Akabs Hus, da traf han de Øverste af Juda og Ahasias Brodersønner, som tjente Ahasia, og slog dem ihjel.
9 Ya kuma sa aka nemi Ahaziya. Aka kamo shi sa’ad da ya ɓuya a Samariya, suka kawo shi wurin Yehu, suka kashe shi, suka binne shi, gama sun ce, “Shi jikan Yehoshafat ne, wanda ya nemi Ubangiji da dukan zuciyarsa.” Ta haka babu wani a gidan Ahaziya da yake da ƙarfin cin gaba da mulkin.
Siden ledte han efter Ahasia, og de grebe ham, da han havde skjult sig i Samaria, og de førte ham til Jehu og dræbte ham og begrove ham; thi de sagde: Han er en Søn af Josafat, som søgte Herren af sit ganske Hjerte; og der var ingen af Ahasias Hus, som formaaede at overtage Riget.
10 Sa’ad da Ataliya mahaifiyar Ahaziya ta ga cewa ɗanta ya mutu, sai ta tashi ta hallaka dukan’yan gidan sarautar Yahuda.
Der Athalia, Ahasias Moder, saa, at hendes Søn var død, da gjorde hun sig rede og udryddede hele den kongelige Slægt i Judas Hus.
11 Amma Yehosheba,’yar Sarki Yehoram, ta ɗauki Yowash ɗan Ahaziya ta sace shi daga cikin’ya’yan gidan sarauta waɗanda ake shiri a kashe, ta sa shi tare da mai renonsa a ɗakin kwana. Haka fa, Yehosheba’yar sarki Yoram, matar Yehohiyada firist, ta yi, gama ita’yar’uwar Ahaziya ce, ta ɓoye Yowash don kada Ataliya tă kashe shi.
Men Josabeath, Kongens Datter, tog Joas, Ahasias Søn, og stjal ham midt ud fra Kongens Sønner, som bleve dræbte, og satte ham med sin Amme i Sengekammeret; og Josabeath, Kong Jorams Datter, Præsten Jojadas Hustru, skjulte ham (thi hun var Ahasias Søster) for Athalias Ansigt, saa at hun ikke fik ham dræbt.
12 Ya kasance a ɓoye tare da su a haikalin Allah shekara shida, yayinda Ataliya take mulkin ƙasar.
Og han var skjult hos dem i Guds Hus seks Aar; men Athalia var Dronning i Landet.

< 2 Tarihi 22 >