< 2 Tarihi 21 >
1 Yehoshafat ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda. Sai Yehoram ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Y Josafat murió y lo enterraron en la ciudad de David. Y Joram su hijo se hizo rey en su lugar.
2 ’Yan’uwan Yehoram,’ya’yan Yehoshafat maza su ne, Azariya, Yehiyel, Zakariya, Azariyahu, Mika’ilu da Shefatiya. Dukan waɗannan su ne’ya’yan Yehoshafat sarkin Isra’ila maza.
Y tuvo hermanos, hijos de Josafat, Azarías, Jehiel, Zacarías, Azarías, Micael y Sefatías; todos estos fueron hijos de Josafat, rey de Israel.
3 Mahaifinsu ya ba su kyautai masu yawa na azurfa da zinariya da kayayyaki masu daraja, tare da birane masu katanga a Yahuda, amma ya ba da mulki ga Yehoram domin shi ne ɗan farinsa.
Y su padre les dio mucha plata, oro y cosas de gran valor, así como ciudades amuralladas en Judá; pero el reino se lo dio a Joram, porque era el hijo mayor.
4 Sa’ad da Yehoram ya kafa kansa sosai a bisa mulkin mahaifinsa, sai ya kashe dukan’yan’uwansa da takobi tare da waɗansu sarakunan Isra’ila.
Cuando Joram tomó su lugar sobre el reino de su padre y salvó su posición, mató a filo de espada a sus hermanos, así como a algunos de los príncipes de Israel.
5 Yehoram yana da shekara talatin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara takwas.
Joram tenía treinta y dos años cuando llegó a ser rey; y estuvo gobernando en Jerusalén por ocho años.
6 Ya yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila, kamar yadda gidan Ahab ta yi, gama ya auri’yar Ahab. Ya aikata mugayen ayyuka a idon Ubangiji.
Siguió los caminos de los reyes de Israel e hizo lo que la familia de Acab hizo, porque la hija de Acab era su esposa; E hizo lo malo ante los ojos de Señor.
7 Duk da haka, domin alkawarin da Ubangiji ya yi wa Dawuda, Ubangiji bai so yă hallaka gidan Dawuda ba. Ubangiji ya riga ya yi alkawari zai ci gaba da riƙe fitila domin Dawuda da zuriyarsa har abada.
Pero no era el propósito del Señor enviar destrucción a la familia de David, debido al acuerdo que había hecho con David, cuando dijo que le daría a él y a sus hijos una luz para siempre.
8 A zamanin Yehoram, Edom ya tayar wa Yahuda ya kuma naɗa sarkinsa.
En su tiempo, Edom se rebeló del gobierno de Judá y tomó un rey para ellos.
9 Saboda haka Yehoram ya tafi can tare da shugabannin sojojinsa da kuma dukan keken yaƙinsa. Mutanen Edom suka kewaye shi da shugabannin keken yaƙinsa, amma ya tashi ya fatattaki su da dare.
Entonces Joram se acercó con sus capitanes y todos sus carros de guerra, atacó de noche a los edomitas, cuyas fuerzas lo rodeaban.
10 Har yă zuwa yau Edom na tawaye a kan Yahuda. Libna ya yi tawaye a lokaci guda, domin Yehoram ya yashe Ubangiji Allah na kakanninsa.
Hasta el día de hoy, Edom se rebeló ante el gobierno de Judá: y al mismo tiempo Libna se rebeló ante su gobierno; porque Joram abandonó al Señor, el Dios de sus antepasados.
11 Ya gina masujadan kan tudu a tuddan Yahuda, ya kuma sa mutanen Urushalima suka yi karuwanci, ya sa Yahuda suka kauce.
Y más que esto, hizo lugares altos en las montañas de Judá, enseñando a la gente de Jerusalén a perseguir a dioses falsos, y guiando a Judá lejos del camino verdadero.
12 Yehoram ya sami wasiƙa daga Iliya annabi, wadda ta ce, “Ga abin da Ubangiji Allah na kakanka Dawuda ya ce, ‘Ba ka yi tafiya a hanyoyin mahaifinka Yehoshafat ko Asa sarkin Yahuda ba.
Y le llegó una carta del profeta Elías, diciendo: El Señor, el Dios de tu padre David, dice: Porque no has guardado los caminos de tu padre Josafat ni los caminos de Asa, rey de Judá,
13 Amma ka yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila, ka sa Yahuda ya kauce, ka kuma sa mutanen Urushalima suka yi karuwanci, kamar yadda gidan Ahab ta yi. Ka kuma kashe’yan’uwanka, membobi gidan mahaifinka, mutanen da suka fi ka kirki.
Pero has andado en los caminos de los reyes de Israel, y has hecho que Judá y el pueblo de Jerusalén se hayan prostituido, como se prostituyó la familia de Acab y porque has matado a los hijos de tu padre, tus hermanos, que fueron mejores que tú.
14 Saboda haka a yanzu Ubangiji yana shirin ya bugi mutanenka,’ya’yanka maza, matanka da kuma kome da yake naka, da bugu mai ƙarfi.
Ahora, verdaderamente, el Señor enviará una gran destrucción a tu pueblo, a tus hijos, a tus esposas y a todo lo que es tuyo:
15 Kai kuma za ka kamu da ciwon hanji wanda zai yi ta cinka kowace rana sai har hanjinka sun fito.’”
Y tú mismo sufrirás los dolores crueles de una enfermedad en tú estómago, de modo que día a día tus intestinos se te saldrán debido a la enfermedad.
16 Ubangiji ya sa Filistiyawa da Larabawa waɗanda suke zama kusa da Kushawa su yi gāba da Yehoram
Entonces los filisteos y los árabes, que viven en Etiopía, fueron movidos por el Señor para hacer la guerra a Joram;
17 Suka yaƙi Yahuda, suka kai masa hari, suka kwashe dukan abubuwa masu kyau da suka samu a fadan sarki, tare da’ya’yansa maza da kuma matansa. Ba wanda aka bari, sai dai Ahaziya autansa.
Y subieron contra Judá, forzándose a entrar, y se llevaron todos los bienes de la casa del rey, así como a sus hijos y sus esposas; de modo que no tuvo más hijo que solo Joacaz, el más joven.
18 Bayan dukan wannan, sai Ubangiji ya sa wa Yehoram cuta marar warkarwa ta ciki.
Y después de todo esto, el Señor le envió una enfermedad del estómago de la cual era imposible que se curara.
19 Cikin lokaci, a ƙarshen shekara ta biyu, sai hanjin cikinsa suka fito saboda cutar, ya kuma mutu cikin tsananin zafi. Mutanensa suka hura wuta don girmama shi, kamar yadda suka yi wa kakanninsa.
Y el tiempo continuó, y después de dos años, sus intestinos se le salieron debido a la enfermedad, y murió de dolor cruel. Y su pueblo no hizo fuego para él en su honra como el fuego hecho para sus antepasados.
20 Yehoram yana da shekara talatin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara takwas. Ya mutu, ba ma wanda ya kula, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda, amma ba a makabartan sarakuna ba.
Tenía treinta y dos años cuando comenzó a reinar, y estuvo gobernando en Jerusalén durante ocho años. Y su muerte nadie la lamento, Ellos lo enterraron en la ciudad de David, pero no en el panteón de los reyes.