< 2 Tarihi 21 >

1 Yehoshafat ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda. Sai Yehoram ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Josafat durmió con sus padres, y fue enterrado con ellos en la ciudad de David; y su hijo Joram reinó en su lugar.
2 ’Yan’uwan Yehoram,’ya’yan Yehoshafat maza su ne, Azariya, Yehiyel, Zakariya, Azariyahu, Mika’ilu da Shefatiya. Dukan waɗannan su ne’ya’yan Yehoshafat sarkin Isra’ila maza.
Tuvo hermanos, los hijos de Josafat: Azarías, Jehiel, Zacarías, Azarías, Miguel y Sefatías. Todos ellos eran hijos de Josafat, rey de Israel.
3 Mahaifinsu ya ba su kyautai masu yawa na azurfa da zinariya da kayayyaki masu daraja, tare da birane masu katanga a Yahuda, amma ya ba da mulki ga Yehoram domin shi ne ɗan farinsa.
Su padre les dio grandes regalos de plata, de oro y de cosas preciosas, con ciudades fortificadas en Judá; pero le dio el reino a Joram, porque era el primogénito.
4 Sa’ad da Yehoram ya kafa kansa sosai a bisa mulkin mahaifinsa, sai ya kashe dukan’yan’uwansa da takobi tare da waɗansu sarakunan Isra’ila.
Cuando Joram se alzó sobre el reino de su padre, y se fortaleció, mató a espada a todos sus hermanos, y también a algunos de los príncipes de Israel.
5 Yehoram yana da shekara talatin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara takwas.
Joram tenía treinta y dos años cuando comenzó a reinar, y reinó ocho años en Jerusalén.
6 Ya yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila, kamar yadda gidan Ahab ta yi, gama ya auri’yar Ahab. Ya aikata mugayen ayyuka a idon Ubangiji.
Siguió el camino de los reyes de Israel, al igual que la casa de Ajab, pues tuvo como esposa a la hija de Ajab. Hizo lo que era malo a los ojos del Señor.
7 Duk da haka, domin alkawarin da Ubangiji ya yi wa Dawuda, Ubangiji bai so yă hallaka gidan Dawuda ba. Ubangiji ya riga ya yi alkawari zai ci gaba da riƙe fitila domin Dawuda da zuriyarsa har abada.
Sin embargo, Yahvé no quiso destruir la casa de David, a causa de la alianza que había hecho con él, y porque había prometido darle siempre una lámpara a él y a sus hijos.
8 A zamanin Yehoram, Edom ya tayar wa Yahuda ya kuma naɗa sarkinsa.
En sus días Edom se rebeló de la mano de Judá y se hizo un rey sobre ellos.
9 Saboda haka Yehoram ya tafi can tare da shugabannin sojojinsa da kuma dukan keken yaƙinsa. Mutanen Edom suka kewaye shi da shugabannin keken yaƙinsa, amma ya tashi ya fatattaki su da dare.
Entonces Joram fue allí con sus capitanes y todos sus carros con él. Se levantó de noche e hirió a los edomitas que lo rodeaban, junto con los capitanes de los carros.
10 Har yă zuwa yau Edom na tawaye a kan Yahuda. Libna ya yi tawaye a lokaci guda, domin Yehoram ya yashe Ubangiji Allah na kakanninsa.
Así se rebeló Edom bajo la mano de Judá hasta el día de hoy. También Libna se rebeló al mismo tiempo de debajo de su mano, porque había abandonado a Yahvé, el Dios de sus padres.
11 Ya gina masujadan kan tudu a tuddan Yahuda, ya kuma sa mutanen Urushalima suka yi karuwanci, ya sa Yahuda suka kauce.
Además, hizo lugares altos en los montes de Judá, e hizo que los habitantes de Jerusalén se prostituyeran, y desvió a Judá.
12 Yehoram ya sami wasiƙa daga Iliya annabi, wadda ta ce, “Ga abin da Ubangiji Allah na kakanka Dawuda ya ce, ‘Ba ka yi tafiya a hanyoyin mahaifinka Yehoshafat ko Asa sarkin Yahuda ba.
Le llegó una carta del profeta Elías que decía: “Yahvé, el Dios de David, tu padre, dice: ‘Porque no has seguido los caminos de Josafat, tu padre, ni los de Asá, rey de Judá,
13 Amma ka yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila, ka sa Yahuda ya kauce, ka kuma sa mutanen Urushalima suka yi karuwanci, kamar yadda gidan Ahab ta yi. Ka kuma kashe’yan’uwanka, membobi gidan mahaifinka, mutanen da suka fi ka kirki.
sino que has seguido el camino de los reyes de Israel y has hecho que Judá y los habitantes de Jerusalén se prostituyan como lo hizo la casa de Ajab, y también has matado a tus hermanos de la casa de tu padre, que eran mejores que tú,
14 Saboda haka a yanzu Ubangiji yana shirin ya bugi mutanenka,’ya’yanka maza, matanka da kuma kome da yake naka, da bugu mai ƙarfi.
he aquí que el Señor golpeará a tu pueblo con una gran plaga, incluyendo a tus hijos, a tus esposas y a todas tus posesiones;
15 Kai kuma za ka kamu da ciwon hanji wanda zai yi ta cinka kowace rana sai har hanjinka sun fito.’”
y tendréis una gran enfermedad de las entrañas, hasta que se os caigan las entrañas a causa de la enfermedad, día tras día.’”
16 Ubangiji ya sa Filistiyawa da Larabawa waɗanda suke zama kusa da Kushawa su yi gāba da Yehoram
Yahvé despertó contra Joram el espíritu de los filisteos y de los árabes que están junto a los etíopes;
17 Suka yaƙi Yahuda, suka kai masa hari, suka kwashe dukan abubuwa masu kyau da suka samu a fadan sarki, tare da’ya’yansa maza da kuma matansa. Ba wanda aka bari, sai dai Ahaziya autansa.
y subieron contra Judá, la asaltaron y se llevaron todos los bienes que se encontraban en la casa del rey, incluidos sus hijos y sus mujeres, de modo que no le quedó ningún hijo, excepto Joacaz, el menor de sus hijos.
18 Bayan dukan wannan, sai Ubangiji ya sa wa Yehoram cuta marar warkarwa ta ciki.
Después de todo esto, Yahvé lo hirió en sus entrañas con una enfermedad incurable.
19 Cikin lokaci, a ƙarshen shekara ta biyu, sai hanjin cikinsa suka fito saboda cutar, ya kuma mutu cikin tsananin zafi. Mutanensa suka hura wuta don girmama shi, kamar yadda suka yi wa kakanninsa.
Con el tiempo, al cabo de dos años, se le cayeron los intestinos a causa de su enfermedad, y murió de graves enfermedades. Su pueblo no le hizo ninguna quema, como la de sus padres.
20 Yehoram yana da shekara talatin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara takwas. Ya mutu, ba ma wanda ya kula, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda, amma ba a makabartan sarakuna ba.
Tenía treinta y dos años cuando comenzó a reinar, y reinó en Jerusalén ocho años. Partió sin que nadie lo lamentara. Lo enterraron en la ciudad de David, pero no en las tumbas de los reyes.

< 2 Tarihi 21 >