< 2 Tarihi 21 >

1 Yehoshafat ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda. Sai Yehoram ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Jehoshaphat dormiu com seus pais, e foi enterrado com seus pais na cidade de David; e Jehoram seu filho reinou em seu lugar.
2 ’Yan’uwan Yehoram,’ya’yan Yehoshafat maza su ne, Azariya, Yehiyel, Zakariya, Azariyahu, Mika’ilu da Shefatiya. Dukan waɗannan su ne’ya’yan Yehoshafat sarkin Isra’ila maza.
Ele tinha irmãos, os filhos de Jehoshaphat: Azarias, Jehiel, Zacarias, Azarias, Michael e Shephatiah. Todos estes eram filhos de Jeosafá, rei de Israel.
3 Mahaifinsu ya ba su kyautai masu yawa na azurfa da zinariya da kayayyaki masu daraja, tare da birane masu katanga a Yahuda, amma ya ba da mulki ga Yehoram domin shi ne ɗan farinsa.
Seu pai lhes deu grandes dons de prata, de ouro e de coisas preciosas, com cidades fortificadas em Judá; mas ele deu o reino a Jeorão, porque ele era o primogênito.
4 Sa’ad da Yehoram ya kafa kansa sosai a bisa mulkin mahaifinsa, sai ya kashe dukan’yan’uwansa da takobi tare da waɗansu sarakunan Isra’ila.
Agora, quando Jeorão se levantou sobre o reino de seu pai e se fortaleceu, matou todos os seus irmãos com a espada, e também alguns dos príncipes de Israel.
5 Yehoram yana da shekara talatin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara takwas.
Jeorão tinha trinta e dois anos quando começou a reinar, e reinou oito anos em Jerusalém.
6 Ya yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila, kamar yadda gidan Ahab ta yi, gama ya auri’yar Ahab. Ya aikata mugayen ayyuka a idon Ubangiji.
Ele andou no caminho dos reis de Israel, assim como a casa de Acabe, pois ele tinha a filha de Acabe como esposa. Ele fez o que era mau aos olhos de Iavé.
7 Duk da haka, domin alkawarin da Ubangiji ya yi wa Dawuda, Ubangiji bai so yă hallaka gidan Dawuda ba. Ubangiji ya riga ya yi alkawari zai ci gaba da riƙe fitila domin Dawuda da zuriyarsa har abada.
However Javé não destruiria a casa de Davi, por causa do pacto que ele tinha feito com Davi, e como ele prometeu dar uma lâmpada para ele e para seus filhos sempre.
8 A zamanin Yehoram, Edom ya tayar wa Yahuda ya kuma naɗa sarkinsa.
Em seus dias, Edom se revoltou sob a mão de Judá, e fez um rei sobre si mesmo.
9 Saboda haka Yehoram ya tafi can tare da shugabannin sojojinsa da kuma dukan keken yaƙinsa. Mutanen Edom suka kewaye shi da shugabannin keken yaƙinsa, amma ya tashi ya fatattaki su da dare.
Então Jehoram foi para lá com seus capitães e todas as suas carruagens com ele. Ele se levantou à noite e atingiu os edomitas que o rodeavam, junto com os capitães das carruagens.
10 Har yă zuwa yau Edom na tawaye a kan Yahuda. Libna ya yi tawaye a lokaci guda, domin Yehoram ya yashe Ubangiji Allah na kakanninsa.
Então Edom tem estado em revolta desde debaixo da mão de Judá até os dias de hoje. Então Libnah revoltou-se ao mesmo tempo de debaixo de sua mão, porque havia abandonado Yahweh, o Deus de seus pais.
11 Ya gina masujadan kan tudu a tuddan Yahuda, ya kuma sa mutanen Urushalima suka yi karuwanci, ya sa Yahuda suka kauce.
Além disso, ele fez lugares altos nas montanhas de Judá, e fez com que os habitantes de Jerusalém se prostituíssem, e desviou Judá.
12 Yehoram ya sami wasiƙa daga Iliya annabi, wadda ta ce, “Ga abin da Ubangiji Allah na kakanka Dawuda ya ce, ‘Ba ka yi tafiya a hanyoyin mahaifinka Yehoshafat ko Asa sarkin Yahuda ba.
Veio a ele uma carta do profeta Elias, dizendo: “Javé, o Deus de Davi teu pai, diz: 'Porque não andaste nos caminhos de Jeosafá teu pai, nem nos caminhos de Asa, rei de Judá,
13 Amma ka yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila, ka sa Yahuda ya kauce, ka kuma sa mutanen Urushalima suka yi karuwanci, kamar yadda gidan Ahab ta yi. Ka kuma kashe’yan’uwanka, membobi gidan mahaifinka, mutanen da suka fi ka kirki.
mas andaste no caminho dos reis de Israel', e fizeram Judá e os habitantes de Jerusalém brincar de prostituta como fez a casa de Acabe, e também mataram seus irmãos da casa de seu pai, que eram melhores que você,
14 Saboda haka a yanzu Ubangiji yana shirin ya bugi mutanenka,’ya’yanka maza, matanka da kuma kome da yake naka, da bugu mai ƙarfi.
eis que Javé atacará seu povo com uma grande praga, incluindo seus filhos, suas esposas e todos os seus bens;
15 Kai kuma za ka kamu da ciwon hanji wanda zai yi ta cinka kowace rana sai har hanjinka sun fito.’”
e você terá uma grande doença com uma doença de suas entranhas, até que suas entranhas caiam por causa da doença, dia após dia.’”
16 Ubangiji ya sa Filistiyawa da Larabawa waɗanda suke zama kusa da Kushawa su yi gāba da Yehoram
Yahweh agitou contra Jeorão o espírito dos filisteus e dos árabes que estão ao lado dos etíopes;
17 Suka yaƙi Yahuda, suka kai masa hari, suka kwashe dukan abubuwa masu kyau da suka samu a fadan sarki, tare da’ya’yansa maza da kuma matansa. Ba wanda aka bari, sai dai Ahaziya autansa.
e eles vieram contra Judá, invadiram-na e levaram todos os bens que foram encontrados na casa do rei, incluindo seus filhos e suas esposas, de modo que não lhe restou nenhum filho, exceto Jehoahaz, o mais novo de seus filhos.
18 Bayan dukan wannan, sai Ubangiji ya sa wa Yehoram cuta marar warkarwa ta ciki.
Depois de tudo isso, Yahweh o atingiu em suas entranhas com uma doença incurável.
19 Cikin lokaci, a ƙarshen shekara ta biyu, sai hanjin cikinsa suka fito saboda cutar, ya kuma mutu cikin tsananin zafi. Mutanensa suka hura wuta don girmama shi, kamar yadda suka yi wa kakanninsa.
Com o passar do tempo, ao final de dois anos, suas entranhas caíram por causa de sua doença, e ele morreu de doenças graves. Seu povo não fez nenhuma queima para ele, como a queima de seus pais.
20 Yehoram yana da shekara talatin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara takwas. Ya mutu, ba ma wanda ya kula, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda, amma ba a makabartan sarakuna ba.
Ele tinha trinta e dois anos de idade quando começou a reinar, e reinou em Jerusalém oito anos. Ele partiu sem arrependimento de ninguém. Eles o enterraram na cidade de Davi, mas não nos túmulos dos reis.

< 2 Tarihi 21 >