< 2 Tarihi 21 >

1 Yehoshafat ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda. Sai Yehoram ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Or Josaphat dormit avec ses pères, et il fut enseveli avec eux dans la cité de David, et son fils Joram régna en sa place.
2 ’Yan’uwan Yehoram,’ya’yan Yehoshafat maza su ne, Azariya, Yehiyel, Zakariya, Azariyahu, Mika’ilu da Shefatiya. Dukan waɗannan su ne’ya’yan Yehoshafat sarkin Isra’ila maza.
Joram eut pour frères les fils de Josaphat, Azarias, Jahiel, Zacharie, Azarias, Michaël et Saphatia; tous ceux-là furent fils de Josaphat, roi de Juda.
3 Mahaifinsu ya ba su kyautai masu yawa na azurfa da zinariya da kayayyaki masu daraja, tare da birane masu katanga a Yahuda, amma ya ba da mulki ga Yehoram domin shi ne ɗan farinsa.
Et leur père leur donna beaucoup de présents en argent et en or, ainsi que des pensions, et des villes très fortifiées dans Juda; mais le royaume, il le remit à Joram, parce qu’il était le premier-né.
4 Sa’ad da Yehoram ya kafa kansa sosai a bisa mulkin mahaifinsa, sai ya kashe dukan’yan’uwansa da takobi tare da waɗansu sarakunan Isra’ila.
Joram se leva donc sur le royaume de son père, et, lorsqu’il se fut affermi, il tua par le glaive tous ses frères et quelques-uns des princes d’Israël.
5 Yehoram yana da shekara talatin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara takwas.
Joram avait trente-deux ans lorsqu’il commença à régner, et il régna huit ans à Jérusalem.
6 Ya yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila, kamar yadda gidan Ahab ta yi, gama ya auri’yar Ahab. Ya aikata mugayen ayyuka a idon Ubangiji.
Et il marcha dans les voies des rois d’Israël, comme avait fait la maison d’Achab: car la fille d’Achab était sa femme, et il fit le mal en la présence du Seigneur.
7 Duk da haka, domin alkawarin da Ubangiji ya yi wa Dawuda, Ubangiji bai so yă hallaka gidan Dawuda ba. Ubangiji ya riga ya yi alkawari zai ci gaba da riƙe fitila domin Dawuda da zuriyarsa har abada.
Cependant le Seigneur ne voulut point perdre la maison de David, à cause de l’alliance qu’il avait faite avec lui, et parce qu’il lui avait promis qu’il lui donnerait une lampe à lui et à ses fils en tout temps.
8 A zamanin Yehoram, Edom ya tayar wa Yahuda ya kuma naɗa sarkinsa.
En ces jours-là, Edom se révolta pour n’être pas assujetti à Juda, et il s’établit un roi.
9 Saboda haka Yehoram ya tafi can tare da shugabannin sojojinsa da kuma dukan keken yaƙinsa. Mutanen Edom suka kewaye shi da shugabannin keken yaƙinsa, amma ya tashi ya fatattaki su da dare.
Et lorsque Joram eut passé en Idumée avec ses principaux chefs et toute la cavalerie qui était avec lui, il se leva pendant la nuit, et il battit Edom qui l’avait environné, et tous les chefs de sa cavalerie.
10 Har yă zuwa yau Edom na tawaye a kan Yahuda. Libna ya yi tawaye a lokaci guda, domin Yehoram ya yashe Ubangiji Allah na kakanninsa.
Cependant Edom s’est révolté jusqu’à ce jour pour n’être pas sous la domination de Juda. En ce temps-là Lobna aussi se retira pour n’être pas sous sa main; car il avait abandonné le Seigneur Dieu de ses pères;
11 Ya gina masujadan kan tudu a tuddan Yahuda, ya kuma sa mutanen Urushalima suka yi karuwanci, ya sa Yahuda suka kauce.
Et de plus il fit même des hauts lieux dans les villes de Juda, et il fit forniquer tous les habitants de Jérusalem, et prévariquer Juda.
12 Yehoram ya sami wasiƙa daga Iliya annabi, wadda ta ce, “Ga abin da Ubangiji Allah na kakanka Dawuda ya ce, ‘Ba ka yi tafiya a hanyoyin mahaifinka Yehoshafat ko Asa sarkin Yahuda ba.
Or on lui apporta des lettres du prophète Élie, dans lesquelles il était écrit: Voici ce que dit le Seigneur Dieu de David, votre père: Parce que tu n’as pas marché dans les voies de Josaphat, ton père, et dans les voies d’Asa, roi de Juda,
13 Amma ka yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila, ka sa Yahuda ya kauce, ka kuma sa mutanen Urushalima suka yi karuwanci, kamar yadda gidan Ahab ta yi. Ka kuma kashe’yan’uwanka, membobi gidan mahaifinka, mutanen da suka fi ka kirki.
Mais que tu es entré dans le chemin des rois d’Israël, que tu as fait forniquer Juda et les habitants de Jérusalem, ayant imité la fornication de la maison d’Achab, et que de plus tu as tué tes frères mêmes, la maison de ton père, meilleure que toi,
14 Saboda haka a yanzu Ubangiji yana shirin ya bugi mutanenka,’ya’yanka maza, matanka da kuma kome da yake naka, da bugu mai ƙarfi.
Voilà que le Seigneur te frappera d’une grande plaie, avec ton peuple, tes fils, tes femmes, et tout ce qui t’appartient;
15 Kai kuma za ka kamu da ciwon hanji wanda zai yi ta cinka kowace rana sai har hanjinka sun fito.’”
Mais toi, tu seras malade d’une très cruelle langueur, jusqu’à ce que tes entrailles sortent peu à peu chaque jour.
16 Ubangiji ya sa Filistiyawa da Larabawa waɗanda suke zama kusa da Kushawa su yi gāba da Yehoram
Le Seigneur suscita donc contre Joram l’esprit des Philistins et des Arabes, qui confinent avec les Ethiopiens;
17 Suka yaƙi Yahuda, suka kai masa hari, suka kwashe dukan abubuwa masu kyau da suka samu a fadan sarki, tare da’ya’yansa maza da kuma matansa. Ba wanda aka bari, sai dai Ahaziya autansa.
Et ils montèrent dans la terre de Juda, et ils la ravagèrent, et ils pillèrent tout objet qui fut trouvé dans la maison du roi, et de plus, ils emmenèrent ses fils et ses femmes; et il ne lui resta de fils que Joachaz, le plus jeune de tous.
18 Bayan dukan wannan, sai Ubangiji ya sa wa Yehoram cuta marar warkarwa ta ciki.
Et par dessus tout cela, le Seigneur le frappa d’une maladie d’intestins incurable.
19 Cikin lokaci, a ƙarshen shekara ta biyu, sai hanjin cikinsa suka fito saboda cutar, ya kuma mutu cikin tsananin zafi. Mutanensa suka hura wuta don girmama shi, kamar yadda suka yi wa kakanninsa.
Or un jour succédant à un autre jour, et des espaces de temps se déroulant, un cours de deux années fut accompli; alors, ainsi consumé par un si long dépérissement, qu’il répandait même ses entrailles, il fut quitte de la maladie en même temps que de la vie. Il mourut donc de cette infirmité très cruelle, et le peuple ne l’ensevelit point selon la coutume, en le brûlant, comme il avait fait à ses ancêtres.
20 Yehoram yana da shekara talatin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara takwas. Ya mutu, ba ma wanda ya kula, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda, amma ba a makabartan sarakuna ba.
Il avait trente-deux ans lorsqu’il commença à régner, et il régna huit ans à Jérusalem; et il ne marcha pas droit. Or on l’ensevelit dans la cité de David, mais non pas dans le sépulcre des rois.

< 2 Tarihi 21 >