< 2 Tarihi 21 >

1 Yehoshafat ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda. Sai Yehoram ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Puis Josaphat s'endormit avec ses pères, et fut enseveli avec eux en la Cité de David; et Joram son fils régna en sa place.
2 ’Yan’uwan Yehoram,’ya’yan Yehoshafat maza su ne, Azariya, Yehiyel, Zakariya, Azariyahu, Mika’ilu da Shefatiya. Dukan waɗannan su ne’ya’yan Yehoshafat sarkin Isra’ila maza.
Il eut des frères fils de Josaphat, [savoir] Hazaria, Jéhiël, Zacharie, Hazaria, Micaël, et Séphatia; tous ceux-là [furent] fils de Josaphat, Roi d'Israël.
3 Mahaifinsu ya ba su kyautai masu yawa na azurfa da zinariya da kayayyaki masu daraja, tare da birane masu katanga a Yahuda, amma ya ba da mulki ga Yehoram domin shi ne ɗan farinsa.
Or leur père leur avait fait de grands dons d'argent, d'or, et de choses exquises, avec des villes fortes en Juda; mais il avait donné le Royaume à Joram, parce qu'il était l'aîné.
4 Sa’ad da Yehoram ya kafa kansa sosai a bisa mulkin mahaifinsa, sai ya kashe dukan’yan’uwansa da takobi tare da waɗansu sarakunan Isra’ila.
Et Joram étant élevé sur le Royaume de son père, se fortifia, et tua avec l'épée tous ses frères, et quelques-uns des principaux d'Israël.
5 Yehoram yana da shekara talatin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara takwas.
Joram était âgé de trente-deux ans quand il commença à régner, et il régna huit ans à Jérusalem.
6 Ya yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila, kamar yadda gidan Ahab ta yi, gama ya auri’yar Ahab. Ya aikata mugayen ayyuka a idon Ubangiji.
Et il suivit le train des Rois d'Israël, comme avait fait la maison d'Achab; car la fille d'Achab était sa femme; de sorte qu'il fit ce qui est déplaisant à l'Eternel.
7 Duk da haka, domin alkawarin da Ubangiji ya yi wa Dawuda, Ubangiji bai so yă hallaka gidan Dawuda ba. Ubangiji ya riga ya yi alkawari zai ci gaba da riƙe fitila domin Dawuda da zuriyarsa har abada.
Toutefois l'Eternel ne voulut point détruire la maison de David, à cause de l'alliance qu'il avait traitée avec David, et selon ce qu'il avait dit, qu'il lui donnerait une Lampe, à lui et à ses fils à toujours.
8 A zamanin Yehoram, Edom ya tayar wa Yahuda ya kuma naɗa sarkinsa.
De son temps ceux d'Edom se révoltèrent de l'obéissance de Juda, et établirent un Roi sur eux.
9 Saboda haka Yehoram ya tafi can tare da shugabannin sojojinsa da kuma dukan keken yaƙinsa. Mutanen Edom suka kewaye shi da shugabannin keken yaƙinsa, amma ya tashi ya fatattaki su da dare.
C'est pourquoi Joram marcha [vers Tsahir] avec ses capitaines et tous les chariots qu'il avait, et s'étant levé de nuit il battit les Iduméens qui étaient autour de lui, et tous les gouverneurs des chariots.
10 Har yă zuwa yau Edom na tawaye a kan Yahuda. Libna ya yi tawaye a lokaci guda, domin Yehoram ya yashe Ubangiji Allah na kakanninsa.
Néanmoins les Iduméens se révoltèrent de l'obéissance de Juda, jusqu'à ce jour. En ce même temps Libna se révolta de l'obéissance de [Joram], parce qu'il avait abandonné l'Eternel le Dieu de ses pères.
11 Ya gina masujadan kan tudu a tuddan Yahuda, ya kuma sa mutanen Urushalima suka yi karuwanci, ya sa Yahuda suka kauce.
Il fit aussi des hauts lieux dans les montagnes de Juda, et fit paillarder les habitants de Jérusalem, et il y poussa aussi Juda.
12 Yehoram ya sami wasiƙa daga Iliya annabi, wadda ta ce, “Ga abin da Ubangiji Allah na kakanka Dawuda ya ce, ‘Ba ka yi tafiya a hanyoyin mahaifinka Yehoshafat ko Asa sarkin Yahuda ba.
Alors on lui apporta un écrit de la part d'Elie le Prophète, disant: Ainsi a dit l'Eternel, le Dieu de David ton père: Parce que tu n'as point suivi la voie de Josaphat ton père, ni la voie d'Asa Roi de Juda;
13 Amma ka yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila, ka sa Yahuda ya kauce, ka kuma sa mutanen Urushalima suka yi karuwanci, kamar yadda gidan Ahab ta yi. Ka kuma kashe’yan’uwanka, membobi gidan mahaifinka, mutanen da suka fi ka kirki.
Mais que tu as suivi le train des Rois d'Israël, et que tu as fait paillarder ceux de Juda, et les habitants de Jérusalem, comme la maison d'Achab a fait paillarder [Israël], et même que tu as tué tes frères, la famille de ton père, qui étaient meilleurs que toi;
14 Saboda haka a yanzu Ubangiji yana shirin ya bugi mutanenka,’ya’yanka maza, matanka da kuma kome da yake naka, da bugu mai ƙarfi.
Voici, l'Eternel s'en va frapper de grandes plaies ton peuple, tes enfants, tes femmes, et tous tes troupeaux.
15 Kai kuma za ka kamu da ciwon hanji wanda zai yi ta cinka kowace rana sai har hanjinka sun fito.’”
Et tu auras de grosses maladies, une maladie d'entrailles, jusques là que tes entrailles sortiront par la force de la maladie, qui durera deux ans.
16 Ubangiji ya sa Filistiyawa da Larabawa waɗanda suke zama kusa da Kushawa su yi gāba da Yehoram
L'Eternel souleva donc contre Joram l'esprit des Philistins, et des Arabes qui habitent près des Ethiopiens;
17 Suka yaƙi Yahuda, suka kai masa hari, suka kwashe dukan abubuwa masu kyau da suka samu a fadan sarki, tare da’ya’yansa maza da kuma matansa. Ba wanda aka bari, sai dai Ahaziya autansa.
Lesquels montèrent contre Juda, et se jetèrent sur tout le pays, et pillèrent toutes les richesses qui furent trouvées dans la maison du Roi, et même ils emmenèrent captifs ses enfants et ses femmes; de sorte qu'il ne lui demeura aucun fils, sinon Jéhoachaz, le plus petit de ses enfants.
18 Bayan dukan wannan, sai Ubangiji ya sa wa Yehoram cuta marar warkarwa ta ciki.
Et après toutes ces choses l'Eternel le frappa dans ses entrailles d'une maladie incurable.
19 Cikin lokaci, a ƙarshen shekara ta biyu, sai hanjin cikinsa suka fito saboda cutar, ya kuma mutu cikin tsananin zafi. Mutanensa suka hura wuta don girmama shi, kamar yadda suka yi wa kakanninsa.
Et il arriva qu'un jour s'écoulant après l'autre, et comme le temps de deux ans vint à expirer, ses entrailles sortirent par la force de la maladie; ainsi il mourut avec de grandes douleurs; et le peuple ne fit point brûler sur lui de choses aromatiques, comme on avait fait sur ses pères.
20 Yehoram yana da shekara talatin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara takwas. Ya mutu, ba ma wanda ya kula, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda, amma ba a makabartan sarakuna ba.
Il était âgé de trente-deux [ans] quand il commença à régner, et il régna huit ans à Jérusalem; il s'en alla sans être regretté, et on l'ensevelit en la Cité de David, mais non pas aux sépulcres des Rois.

< 2 Tarihi 21 >