< 2 Tarihi 20 >

1 Bayan wannan, Mowabawa da Ammonawa tare da waɗansu Meyunawa suka zo su yaƙi Yehoshafat.
Nogen tid efter hendte det at Moabs barn og Ammons barn og sammen med dem en del av me'unittene gjorde et krigstog mot Josafat.
2 Sai waɗansu mutane suka zo suka faɗa wa Yehoshafat, “Ga babban runduna tana zuwa a kanka daga Edom, daga ƙetaren Teku, daga Aram. Ta ma kai Hazazon Tamar” (wato, En Gedi).
Folk kom med tidende derom til Josafat og sa: Det kommer en stor hær imot dig fra hin side havet, fra Syria; de er allerede i Haseson-Tamar, det er En-Gedi.
3 A firgice, Yehoshafat ya yanke shawara yă nemi nufin Ubangiji, ya kuma yi shelar azumi a dukan Yahuda.
Da blev Josafat redd, og han v endte sig i bønn til Herren og lot utrope en faste over hele Juda.
4 Mutanen Yahuda suka taru gaba ɗaya don su nemi taimako daga wurin Ubangiji, tabbatacce suka fito daga kowane garin Yahuda don su neme shi.
Og Juda samlet sig for å søke hjelp hos Herren; ja, fra alle Judas byer kom de for å søke Herren.
5 Sa’an nan Yehoshafat ya miƙe tsaye a taron Yahuda da Urushalima a haikalin Ubangiji a sabon filin
Da stod Josafat frem blandt dem som var kommet sammen fra Juda og Jerusalem, i Herrens hus foran den nye forgård
6 ya ce, “Ya Ubangiji Allah na kakanninmu, ba kai ne Allah wanda yake sama ba? Kana mulki a bisa dukan mulkokin ƙasashe. Iko da girma suna a hannunka, kuma ba wanda zai iya tsayayya da kai.
og sa: Herre, våre fedres Gud! Er det ikke du som er Gud i himmelen? Du råder over alle folkenes riker; i din hånd er kraft og velde, og det er ingen som kan holde stand mot dig.
7 Ya Allahnmu, ba kai ba ne ka kore mazaunan wannan ƙasa a gaban mutanenka Isra’ila ka kuma ba da ita har abada ga zuriyar Ibrahim abokinka?
Har ikke du, vår Gud, drevet dette lands innbyggere ut for ditt folk Israel og gitt det til din venn Abrahams efterkommere for alle tider?
8 Sun yi zama a cikinta suka kuma yi gina wuri mai tsarki a cikinta domin Sunanka cewa,
De bosatte sig der og bygget dig der en helligdom for ditt navn og sa:
9 ‘In masifa ta zo mana, ko takobin hukunci, ko annoba ko yunwa, za mu tsaya a gabanka a gaban wannan haikalin da yake ɗauke da Sunanka, mu kuma yi kuka gare ka cikin azaba, za ka kuwa ji mu, ka cece mu.’
Om nogen ulykke kommer over oss, sverd, straffedom, pest eller hungersnød, så vil vi stille oss foran dette hus og for ditt åsyn, for ditt navn bor i dette hus, og vi vil rope til dig i vår trengsel, og du vil høre og frelse.
10 “Yanzu kuma ga mutanen Ammon, da na Mowab, da na Dutsen Seyir, waɗanda ka hana Isra’ilawa su kai musu yaƙi sa’ad da suka fito daga ƙasar Masar, su ne mutanen da Isra’ila suka ƙyale, ba su hallaka su ba.
Se nu hvorledes Ammons barn og Moab og folket fra Se'ir-fjellet - disse folk som du ikke gav Israel lov til å trenge inn iblandt da de kom fra Egyptens land, så de bøide av og drog bort fra dem og ikke ødela dem -
11 Yau ga yadda suke so su biya mu. Su suke so su kore mu daga ƙasar da ka ba mu gādo.
se hvorledes de lønner oss! Nu kommer de og vil drive oss ut av din eiendom, som du har gitt oss i eie.
12 Ya Allahnmu, ba za ka hukunta su ba? Gama ba mu da ƙarfin fuskantar wannan babbar rundunar da take so ta yaƙe mu. Ba mu san abin da za mu yi ba, mu dai mun zuba maka ido.”
Vår Gud! Vil du ikke holde dom over dem? For vi har ikke kraft nok til å motstå denne store hær som kommer imot oss, og vi vet ikke hvad vi skal gjøre; men til dig er våre øine vendt.
13 Dukan mazan Yahuda, tare da matansu da yaransu da ƙananansu, suka tsaya a gaban Ubangiji.
Og hele Juda stod der for Herrens åsyn, endog deres små barn, deres hustruer og deres sønner.
14 Sa’an nan Ruhun Ubangiji ya sauko a kan Yahaziyel ɗan Zakariya, ɗan Benahiya, ɗan Yehiyel, ɗan Mattaniya, wani Balawe kuma zuriyar Asaf, yayinda yake tsaye a cikin taron.
Da kom Herrens Ånd midt i forsamlingen over levitten Jahasiel, sønn av Sakarja, sønn av Benaja, sønn av Je'iel, sønn av Mattanja, en av Asafs sønner,
15 Ya ce, “Saurara, Sarki Yehoshafat da dukan waɗanda suke zama a Yahuda da Urushalima! Ga abin da Ubangiji ya ce muku, ‘Kada ku ji tsoro ko ku fid da zuciya saboda wannan babbar runduna. Gama yaƙin ba naku ba ne, amma na Allah.
Og han sa: Hør efter, hele Juda og I Jerusalems innbyggere og du kong Josafat! Så sier Herren til eder: Frykt ikke og reddes ikke for denne store hær! For dette er ikke eders krig, men Guds.
16 Gobe ku fito ku gangara ku yaƙe su. Za su yi ta haurawa ta Mashigin Ziz, ku kuwa za ku same su a ƙarshen kwari a Hamadan Yeruwel.
Dra ned mot dem imorgen! Da drar de opefter Hassis-bakken, Og I kommer til å møte dem ved enden av dalen midt imot Jeruelørkenen.
17 Ba lalle ba ne ku yi wannan yaƙi. Ku dai, ku ja dāgā, ku tsaya kurum ku ga nasarar da Ubangiji zai ba ku, ya Yahuda da Urushalima. Kada ku ji tsoro; kada ku karai. Ku fito don ku fuskance su gobe, Ubangiji kuwa zai kasance tare ku.’”
Men det er ikke I som skal stride her; I skal bare stille eder op og stå og se på hvorledes Herren frelser eder, I fra Juda og Jerusalem! Frykt ikke og reddes ikke! Dra ut imot dem imorgen, og Herren skal være med eder.
18 Yehoshafat ya rusuna da fuskarsa har ƙasa, dukan mutanen Yahuda da Urushalima suka fāɗi rubda ciki suka yi sujada a gaban Ubangiji.
Da bøide Josafat sig med ansiktet til jorden, og hele Juda og alle Jerusalems innbyggere falt ned for Herrens åsyn og tilbad Herren.
19 Sa’an nan waɗansu Lawiyawa daga Kohatawa da Korayawa suka tashi tsaye suka yabe Ubangiji, Allah na Isra’ila, da babbar murya sosai.
Og de levitter som hørte til kahatittenes og korahittenes barn, reiste sig og lovet Herren, Israels Gud, med høi og lydelig røst.
20 Da sassafe suka tashi suka nufi Hamadan Tekowa. Yayinda suka kama hanya, Yehoshafat ya tsaya ya ce, “Ku saurare ni, Yahuda da mutanen Urushalima! Ku amince da Ubangiji Allahnku za a kuwa kafa ku; ku amince da annabawansa za ku kuwa yi nasara.”
Morgenen efter tok de tidlig ut og drog avsted til Tekoa-ørkenen; og med det samme de drog ut, stod Josafat frem og sa: Hør på mig, Juda og I Jerusalems innbyggere! Tro på Herren eders Gud, så skal I holde stand! Tro på hans profeter, så skal I ha lykke med eder!
21 Bayan suka yi shawara tare da shugabanni, sai ya zaɓi mutanen da za su ja gaban sojoji suna waƙa ga Ubangiji suna yabonsa saboda tsarkinsa suna cewa, “Ku yi godiya ga Ubangiji, gama ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.”
Og han rådførte sig med folket og stilte op sangere som skulde love Herren i hellig skrud mens de drog ut foran den væbnede hær, og si: Lov Herren, for hans miskunnhet varer evindelig!
22 Da suka fara waƙa, suna kuma yabo, sai Ubangiji ya kai hari a kan mutanen Ammon da Mowab da Dutsen Seyir, waɗanda suka kawo hari a Yahuda, aka kuwa ci su da yaƙi.
Og straks de begynte med sine fryderop og lovsanger, lot Herren en flokk bakfra komme over Ammons barn, Moab og folket fra Se'ir-fjellet, som var kommet mot Juda, og de blev slått.
23 Mutanen Ammon da Mowab suka tasar wa mazaunan Dutsen Seyir, suka hallaka su ƙaƙaf. Sa’ad da suka karkashe mazaunan Seyir sai suka fāɗa wa juna, suka yi ta hallaka juna.
Og Ammons barn og Moab vendte sig mot folket fra Se'ir-fjellet og hugg dem ned og ødela dem; og da de hadde gjort ende på folket fra Se'ir, hjalp de hverandre med innbyrdes ødeleggelse.
24 Sa’ad da mutanen Yahuda suka zo wurin da yake fuskantar hamada, suka duba ta wajen babban rundunar, sai suka ga gawawwaki birjik a ƙasa; babu wani wanda ya kuɓuta.
Da Juda kom op på høiden hvorfra en kunde se ut over ørkenen, og så sig om efter hæren, fikk de se dem ligge døde på jorden, og ingen var sloppet unda.
25 Sa’ad da Yehoshafat da jama’arsa suka je kwasar ganima, sai suka sami shanu masu yawan gaske, da kayayyaki, da tufafi, da abubuwa masu daraja, waɗanda suka yi ta kwasa har suka gaji. Kwana uku suka yi suna kwasar ganimar saboda yawanta.
Josafat og hans folk drog dit for å plyndre, og de fant der både gods og døde kropper og kostbare ting i mengde, og det hærfang de tok, var så stort at de ikke kunde bære det; i tre dager holdt de på med å plyndre, så meget hærfang var det.
26 A rana ta huɗu sai suka taru a Kwarin Beraka, inda suka yabi Ubangiji. Wannan ne ya sa ake kiransa Kwarin Beraka har wa yau.
Den fjerde dag samlet de sig i Lovprisnings-dalen. Der lovet de Herren; derfor heter dette sted Lovprisnings-dalen den dag idag.
27 Sa’an nan Yehoshafat ya jagoranci dukan mutanen Yahuda da Urushalima suka dawo da farin ciki zuwa Urushalima, gama Ubangiji ya ba su dalilin farin ciki a kan abokan gābansu.
Så vendte alle Judas og Jerusalems menn om med Josafat foran og drog glade tilbake til Jerusalem; for Herren hadde unt dem den glede å vinne over sine fiender.
28 Suka shiga Urushalima suka shiga haikalin Ubangiji da kiɗin molaye da sarewa da kuma garayu.
De drog inn i Jerusalem til Herrens hus med harper og citarer og trompeter.
29 Tsoron Allah ya kama dukan mulkokin ƙasashe sa’ad da suka ji yadda Ubangiji ya yi yaƙi a kan abokan gāban Isra’ila.
Og frykt for Gud kom over alle riker rundt i landene, da de hørte at Herren hadde stridt mot Israels fiender.
30 Mulkin Yehoshafat kuwa ya zauna lafiya, gama Allahnsa ya ba shi hutu a kowane gefe.
Og Josafats rike hadde nu fred, fordi hans Gud lot ham få ro på alle kanter.
31 Ta haka Yehoshafat ya yi mulki a bisa Yahuda. Yana da shekara talatin da biyar sa’ad da ya zama sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ashirin da biyar. Sunan mahaifiyarsa Azuba ce,’yar Shilhi.
Således regjerte Josafat over Juda. Han var fem og tretti år gammel da han blev konge, og regjerte fem og tyve år i Jerusalem. Hans mor hette Asuba og var datter av Silhi.
32 Ya yi tafiya a hanyoyin mahaifinsa Asa bai kuwa kauce daga gare su ba; ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji.
Han vandret på sin far Asas vei og vek ikke fra den, men gjorde hvad rett var i Herrens øine.
33 Duk da haka ba a kawar da masujadai kan tudu ba, domin har yanzu mutanen ba su tsayar da zukatansu ga Allahn kakanninsu ba.
Dog blev offerhaugene ikke nedlagt, og folket hadde ennu ikke vendt sitt hjerte til sine fedres Gud.
34 Sauran ayyukan mulkin Yehoshafat, daga farko zuwa ƙarshe, an rubuta su a tarihin Yehu ɗan Hanani, waɗanda aka rubuta a littafin sarakunan Isra’ila.
Hvad som ellers er å fortelle om Josafat, både i hans første og i hans senere dager, det er opskrevet i Jehus, Hananis sønns krønike, som er optatt i boken om Israels konger.
35 Daga baya, Yehoshafat sarkin Yahuda ya haɗa kai da Ahaziya sarkin Isra’ila, wanda yake da laifin mugunta.
Siden inngikk Josafat, Judas konge, en overenskomst med Akasja, Israels konge, han som bar sig så ugudelig at.
36 Ya yarda da shi su gina jiragen ruwan kasuwanci. Bayan aka gina waɗannan a Eziyon Geber,
Han kom overens med ham om å bygge skiber som skulde gå til Tarsis; og de bygget skiber i Esjon-Geber.
37 Eliyezer ɗan Dodabahu na Maresha ya yi annabci a kan Yehoshafat cewa, “Domin ka haɗa kai da Ahaziya, Ubangiji zai hallaka abin da ka yi.” Jiragen ruwan kuwa suka farfashe, ba a kuwa iya sa su je kasuwanci ba.
Da spådde Elieser, Dodavas sønn, fra Maresa, mot Josafat og sa: Fordi du har inngått forbund med Akasja, skal Herren la ditt foretagende bli til intet. Og nogen av skibene forliste, så de ikke kunde gå til Tarsis.

< 2 Tarihi 20 >