< 2 Tarihi 20 >

1 Bayan wannan, Mowabawa da Ammonawa tare da waɗansu Meyunawa suka zo su yaƙi Yehoshafat.
Kwasekusithi emva kwalokho abantwana bakoMowabi labantwana bakoAmoni belabanye ngaphandle kwamaAmoni beza bamelana loJehoshafathi empini.
2 Sai waɗansu mutane suka zo suka faɗa wa Yehoshafat, “Ga babban runduna tana zuwa a kanka daga Edom, daga ƙetaren Teku, daga Aram. Ta ma kai Hazazon Tamar” (wato, En Gedi).
Kwasekusiza abanye babikela uJehoshafathi besithi: Kuyeza ixuku elikhulu ukumelana lawe elivela phetsheya kolwandle, eSiriya; khangela-ke, liseHazazoni-Tamari, eyiEngedi.
3 A firgice, Yehoshafat ya yanke shawara yă nemi nufin Ubangiji, ya kuma yi shelar azumi a dukan Yahuda.
UJehoshafathi wasesesaba, wamisa ubuso bakhe ukudinga iNkosi, wamemezela ukuzila ukudla kuye wonke uJuda.
4 Mutanen Yahuda suka taru gaba ɗaya don su nemi taimako daga wurin Ubangiji, tabbatacce suka fito daga kowane garin Yahuda don su neme shi.
UJuda wasezibuthanisa ukudinga eNkosini; lasemizini yonke yakoJuda baphuma beza ukudinga iNkosi.
5 Sa’an nan Yehoshafat ya miƙe tsaye a taron Yahuda da Urushalima a haikalin Ubangiji a sabon filin
UJehoshafathi wasesima ebandleni lakoJuda leJerusalema endlini yeNkosi phambi kweguma elitsha.
6 ya ce, “Ya Ubangiji Allah na kakanninmu, ba kai ne Allah wanda yake sama ba? Kana mulki a bisa dukan mulkokin ƙasashe. Iko da girma suna a hannunka, kuma ba wanda zai iya tsayayya da kai.
Wasesithi: Nkosi, Nkulunkulu wabobaba, wena kawusuye yini uNkulunkulu emazulwini? Yebo, kawubusi yini kuyo yonke imibuso yezizwe? Lesandleni sakho kukhona amandla lengalo, ukuze kungabi khona ongamelana lawe.
7 Ya Allahnmu, ba kai ba ne ka kore mazaunan wannan ƙasa a gaban mutanenka Isra’ila ka kuma ba da ita har abada ga zuriyar Ibrahim abokinka?
KawusiNkulunkulu wethu yini? Uxotshile abahlali balelilizwe elifeni phambi kwabantu bakho uIsrayeli, walinika inzalo kaAbrahama umngane wakho kuze kube phakade.
8 Sun yi zama a cikinta suka kuma yi gina wuri mai tsarki a cikinta domin Sunanka cewa,
Basebehlala kilo, bakwakhela indawo engcwele kulo eyebizo lakho, besithi:
9 ‘In masifa ta zo mana, ko takobin hukunci, ko annoba ko yunwa, za mu tsaya a gabanka a gaban wannan haikalin da yake ɗauke da Sunanka, mu kuma yi kuka gare ka cikin azaba, za ka kuwa ji mu, ka cece mu.’
Uba kusehlela phezu kwethu ububi, inkemba, isahlulelo, loba umatshayabhuqe wesifo, loba indlala, sizakuma phambi kwalindlu laphambi kwakho (ngoba ibizo lakho likulindlu), sikhale kuwe ekubandezelekeni kwethu, uzakuzwa-ke usindise.
10 “Yanzu kuma ga mutanen Ammon, da na Mowab, da na Dutsen Seyir, waɗanda ka hana Isra’ilawa su kai musu yaƙi sa’ad da suka fito daga ƙasar Masar, su ne mutanen da Isra’ila suka ƙyale, ba su hallaka su ba.
Ngakho-ke, khangela, abantwana bakoAmoni labakoMowabi labentabeni iSeyiri ongavumanga ukuthi uIsrayeli adlule phakathi kwabo lapho besuka elizweni leGibhithe, kodwa babafulathela kabababhubhisanga;
11 Yau ga yadda suke so su biya mu. Su suke so su kore mu daga ƙasar da ka ba mu gādo.
khangela-ke, basivuza beza ukuzasixotsha elifeni lakho owenze ukuthi silidle.
12 Ya Allahnmu, ba za ka hukunta su ba? Gama ba mu da ƙarfin fuskantar wannan babbar rundunar da take so ta yaƙe mu. Ba mu san abin da za mu yi ba, mu dai mun zuba maka ido.”
Nkulunkulu wethu, kawuyikubahlulela yini? Ngoba amandla kawakho kithi okumelana lalelixuku elikhulu elize ukumelana lathi; njalo thina kasikwazi esingakwenza, kodwa amehlo ethu akuwe.
13 Dukan mazan Yahuda, tare da matansu da yaransu da ƙananansu, suka tsaya a gaban Ubangiji.
UJuda wonke wasesima phambi kweNkosi, lensane zabo, omkabo labantwana babo.
14 Sa’an nan Ruhun Ubangiji ya sauko a kan Yahaziyel ɗan Zakariya, ɗan Benahiya, ɗan Yehiyel, ɗan Mattaniya, wani Balawe kuma zuriyar Asaf, yayinda yake tsaye a cikin taron.
Khona uJahaziyeli indodana kaZekhariya indodana kaBhenaya indodana kaJeyiyeli indodana kaMathaniya, umLevi emadodaneni kaAsafi, uMoya weNkosi wafika phezu kwakhe phakathi kwebandla.
15 Ya ce, “Saurara, Sarki Yehoshafat da dukan waɗanda suke zama a Yahuda da Urushalima! Ga abin da Ubangiji ya ce muku, ‘Kada ku ji tsoro ko ku fid da zuciya saboda wannan babbar runduna. Gama yaƙin ba naku ba ne, amma na Allah.
Wasesithi: Lalelani lonke bakoJuda labahlali beJerusalema, lawe nkosi Jehoshafathi; itsho njalo iNkosi kini: Lina lingesabi lingatshaywa luvalo ngenxa yalelixuku elikhulu, ngoba impi kayisiyo yenu, kodwa ngekaNkulunkulu.
16 Gobe ku fito ku gangara ku yaƙe su. Za su yi ta haurawa ta Mashigin Ziz, ku kuwa za ku same su a ƙarshen kwari a Hamadan Yeruwel.
Kusasa yehlani limelane labo; khangela, bayenyuka ngomqanso weZizi; lizabathola ekucineni kwesihotsha phambi kwenkangala yeJeruweli.
17 Ba lalle ba ne ku yi wannan yaƙi. Ku dai, ku ja dāgā, ku tsaya kurum ku ga nasarar da Ubangiji zai ba ku, ya Yahuda da Urushalima. Kada ku ji tsoro; kada ku karai. Ku fito don ku fuskance su gobe, Ubangiji kuwa zai kasance tare ku.’”
Kakusikwenu ukulwa kule impi; zimiseni lime, libone usindiso lweNkosi lani, Juda leJerusalema. Lingesabi lingatshaywa luvalo; kusasa phumani limelene labo, ngoba iNkosi izakuba lani.
18 Yehoshafat ya rusuna da fuskarsa har ƙasa, dukan mutanen Yahuda da Urushalima suka fāɗi rubda ciki suka yi sujada a gaban Ubangiji.
UJehoshafathi wasekhothamisa ikhanda emhlabathini, laye wonke uJuda labahlali beJerusalema bawa phambi kweNkosi, beyikhonza iNkosi.
19 Sa’an nan waɗansu Lawiyawa daga Kohatawa da Korayawa suka tashi tsaye suka yabe Ubangiji, Allah na Isra’ila, da babbar murya sosai.
AmaLevi kubantwana bakoKohathi lakubantwana bakoKora asesukuma ukudumisa iNkosi, uNkulunkulu kaIsrayeli, ngelizwi elikhulu eliphezulu.
20 Da sassafe suka tashi suka nufi Hamadan Tekowa. Yayinda suka kama hanya, Yehoshafat ya tsaya ya ce, “Ku saurare ni, Yahuda da mutanen Urushalima! Ku amince da Ubangiji Allahnku za a kuwa kafa ku; ku amince da annabawansa za ku kuwa yi nasara.”
Basebevuka ekuseni kakhulu, baphuma baya enkangala yeThekhowa; lekuphumeni kwabo uJehoshafathi wema wathi: Ngilalelani Juda labahlali beJerusalema. Kholwani eNkosini uNkulunkulu wenu, lizaqiniswa; likholwe kubaprofethi bayo, lizaphumelela.
21 Bayan suka yi shawara tare da shugabanni, sai ya zaɓi mutanen da za su ja gaban sojoji suna waƙa ga Ubangiji suna yabonsa saboda tsarkinsa suna cewa, “Ku yi godiya ga Ubangiji, gama ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.”
Esecebisene labantu wamisela iNkosi abahlabeleli, abazadumisa ubuhle bobungcwele, ekuphumeni phambi kwabahlomileyo, besithi: Dumisani iNkosi, ngoba umusa wayo umi kuze kube nininini.
22 Da suka fara waƙa, suna kuma yabo, sai Ubangiji ya kai hari a kan mutanen Ammon da Mowab da Dutsen Seyir, waɗanda suka kawo hari a Yahuda, aka kuwa ci su da yaƙi.
Kwathi lapho beqalisa ukuhlabelela lokudumisa, iNkosi yabeka abacathameli ukumelana labantwana bakoAmoni, uMowabi, lentaba iSeyiri, ababezemelana loJuda; basebetshaywa.
23 Mutanen Ammon da Mowab suka tasar wa mazaunan Dutsen Seyir, suka hallaka su ƙaƙaf. Sa’ad da suka karkashe mazaunan Seyir sai suka fāɗa wa juna, suka yi ta hallaka juna.
Ngoba abantwana bakoAmoni labakoMowabi basukuma bamelana labahlali bentaba yeSeyiri ukutshabalalisa lokuchitha; njalo sebebaqedile abahlali beSeyiri, bancedisa ngulowo umakhelwane wakhe encithakalweni.
24 Sa’ad da mutanen Yahuda suka zo wurin da yake fuskantar hamada, suka duba ta wajen babban rundunar, sai suka ga gawawwaki birjik a ƙasa; babu wani wanda ya kuɓuta.
UJuda esefikile enqabeni yokulinda enkangala bakhangela ngasexukwini, khangela-ke, kwakulezidumbu eziwele emhlabathini; njalo kungekho ophephileyo.
25 Sa’ad da Yehoshafat da jama’arsa suka je kwasar ganima, sai suka sami shanu masu yawan gaske, da kayayyaki, da tufafi, da abubuwa masu daraja, waɗanda suka yi ta kwasa har suka gaji. Kwana uku suka yi suna kwasar ganimar saboda yawanta.
UJehoshafathi labantu bakhe sebefikile ukuphanga impango bathola phakathi kwabo ngobunengi, impahla lazo, lezidumbu, lezinto eziligugu, baziphangela baze behluleka ukuzithwala. Njalo baba lensuku ezintathu bephanga impango ngoba yayinengi.
26 A rana ta huɗu sai suka taru a Kwarin Beraka, inda suka yabi Ubangiji. Wannan ne ya sa ake kiransa Kwarin Beraka har wa yau.
Njalo ngosuku lwesine babuthana esihotsheni seBeraka, ngoba lapho bayibusisa iNkosi; ngenxa yalokho babiza ibizo laleyondawo ngokuthi yisihotsha seBeraka kuze kube lamuhla.
27 Sa’an nan Yehoshafat ya jagoranci dukan mutanen Yahuda da Urushalima suka dawo da farin ciki zuwa Urushalima, gama Ubangiji ya ba su dalilin farin ciki a kan abokan gābansu.
Basebebuyela, wonke umuntu wakoJuda leJerusalema, loJehoshafathi enhlokweni yabo, ukuthi babuyele eJerusalema belentokozo, ngoba iNkosi yabathokozisa phezu kwezitha zabo.
28 Suka shiga Urushalima suka shiga haikalin Ubangiji da kiɗin molaye da sarewa da kuma garayu.
Basebengena eJerusalema belezigubhu zezintambo lamachacho lezimpondo, baya endlini yeNkosi.
29 Tsoron Allah ya kama dukan mulkokin ƙasashe sa’ad da suka ji yadda Ubangiji ya yi yaƙi a kan abokan gāban Isra’ila.
Uvalo ngoNkulunkulu lwaselusiba phezu kwayo yonke imibuso yamazwe lapho besizwa ukuthi iNkosi yalwa lezitha zikaIsrayeli.
30 Mulkin Yehoshafat kuwa ya zauna lafiya, gama Allahnsa ya ba shi hutu a kowane gefe.
Ngakho umbuso kaJehoshafathi waba lokuthula, ngoba uNkulunkulu wakhe wamphumuza inhlangothi zonke.
31 Ta haka Yehoshafat ya yi mulki a bisa Yahuda. Yana da shekara talatin da biyar sa’ad da ya zama sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ashirin da biyar. Sunan mahaifiyarsa Azuba ce,’yar Shilhi.
UJehoshafathi wabusa-ke phezu kukaJuda; wayeleminyaka engamatshumi amathathu lanhlanu lapho esiba yinkosi, wabusa iminyaka engamatshumi amabili lanhlanu eJerusalema. Lebizo likanina lalinguAzuba indodakazi kaShilehi.
32 Ya yi tafiya a hanyoyin mahaifinsa Asa bai kuwa kauce daga gare su ba; ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji.
Wasehamba ngendlela kayise uAsa, kaphambukanga kuyo, esenza okulungileyo emehlweni eNkosi.
33 Duk da haka ba a kawar da masujadai kan tudu ba, domin har yanzu mutanen ba su tsayar da zukatansu ga Allahn kakanninsu ba.
Lanxa kunjalo indawo eziphakemeyo kazisuswanga; ngoba abantu babelokhu bengalungisanga inhliziyo yabo kuNkulunkulu waboyise.
34 Sauran ayyukan mulkin Yehoshafat, daga farko zuwa ƙarshe, an rubuta su a tarihin Yehu ɗan Hanani, waɗanda aka rubuta a littafin sarakunan Isra’ila.
Ezinye-ke zezindaba zikaJehoshafathi, ezokuqala lezokucina, khangela, zibhaliwe ezindabeni zikaJehu indodana kaHanani ezagoqelwa egwalweni lwamakhosi akoIsrayeli.
35 Daga baya, Yehoshafat sarkin Yahuda ya haɗa kai da Ahaziya sarkin Isra’ila, wanda yake da laifin mugunta.
Lemva kwalokho uJehoshafathi inkosi yakoJuda wazihlanganisa loAhaziya inkosi yakoIsrayeli owenza ngenkohlakalo ekwenzeni.
36 Ya yarda da shi su gina jiragen ruwan kasuwanci. Bayan aka gina waɗannan a Eziyon Geber,
Wasezihlanganisa laye ukwenza imikhumbi yokuya eTarshishi; basebeyenza imikhumbi eEziyoni-Geberi.
37 Eliyezer ɗan Dodabahu na Maresha ya yi annabci a kan Yehoshafat cewa, “Domin ka haɗa kai da Ahaziya, Ubangiji zai hallaka abin da ka yi.” Jiragen ruwan kuwa suka farfashe, ba a kuwa iya sa su je kasuwanci ba.
UEliyezeri indodana kaDodavahu weMaresha waseprofetha emelene loJehoshafathi esithi: Ngoba uzihlanganise loAhaziya, iNkosi yephulile imisebenzi yakho. Ngakho imikhumbi yephuka, ayaze yenelisa ukuya eTarshishi.

< 2 Tarihi 20 >