< 2 Tarihi 20 >

1 Bayan wannan, Mowabawa da Ammonawa tare da waɗansu Meyunawa suka zo su yaƙi Yehoshafat.
Un pēc tam notika, ka Moaba bērni un Amona bērni, un līdz ar tiem kādi no tiem Meunim nāca, karot pret Jehošafatu.
2 Sai waɗansu mutane suka zo suka faɗa wa Yehoshafat, “Ga babban runduna tana zuwa a kanka daga Edom, daga ƙetaren Teku, daga Aram. Ta ma kai Hazazon Tamar” (wato, En Gedi).
Un vēstneši nāca un sacīja Jehošafatam: liels pulks nāk pret tevi no viņpus jūras, no Sīrijas, un redzi, tie ir AceconaTamarā, tas ir Enģedos.
3 A firgice, Yehoshafat ya yanke shawara yă nemi nufin Ubangiji, ya kuma yi shelar azumi a dukan Yahuda.
Tad Jehošafats izbijās un grieza savu vaigu, To Kungu meklēt, un izsauca gavēni pa visu Jūdu.
4 Mutanen Yahuda suka taru gaba ɗaya don su nemi taimako daga wurin Ubangiji, tabbatacce suka fito daga kowane garin Yahuda don su neme shi.
Un Jūda ļaudis sapulcinājās, meklēt no Tā Kunga palīgu, un no visām Jūda pilsētām tie nāca, To Kungu meklēt.
5 Sa’an nan Yehoshafat ya miƙe tsaye a taron Yahuda da Urushalima a haikalin Ubangiji a sabon filin
Un Jehošafats stāvēja Jūda un Jeruzālemes draudzes vidū Tā Kunga namā priekš tā jaunā pagalma
6 ya ce, “Ya Ubangiji Allah na kakanninmu, ba kai ne Allah wanda yake sama ba? Kana mulki a bisa dukan mulkokin ƙasashe. Iko da girma suna a hannunka, kuma ba wanda zai iya tsayayya da kai.
Un sacīja: Kungs mūsu tēvu Dievs! Vai Tu neesi Dievs debesīs un valdītājs visu ļaužu valstīs? Un Tavā rokā ir spēks un vara, ka neviens pret Tevi nevar celties!
7 Ya Allahnmu, ba kai ba ne ka kore mazaunan wannan ƙasa a gaban mutanenka Isra’ila ka kuma ba da ita har abada ga zuriyar Ibrahim abokinka?
Vai Tu, mūsu Dievs, šās zemes iedzīvotājus neesi izdzinis Savu Israēla ļaužu priekšā, un vai to neesi devis Ābrahāma, Sava mīļā, dzimumam uz mūžīgiem laikiem?
8 Sun yi zama a cikinta suka kuma yi gina wuri mai tsarki a cikinta domin Sunanka cewa,
Un tie tur dzīvojuši un Tev tur taisījuši svētu vietu Tavam vārdam, sacīdami:
9 ‘In masifa ta zo mana, ko takobin hukunci, ko annoba ko yunwa, za mu tsaya a gabanka a gaban wannan haikalin da yake ɗauke da Sunanka, mu kuma yi kuka gare ka cikin azaba, za ka kuwa ji mu, ka cece mu.’
Kad pār mums nāk nelaime, zobens, sodība, mēris un bads, tad mēs stāvēsim priekš šī nama un priekš Tava vaiga, tāpēc ka Tavs vārds ir šinī namā, un kad Tevi piesauksim savās bēdās, tad Tu paklausīsi un izpestīsi.
10 “Yanzu kuma ga mutanen Ammon, da na Mowab, da na Dutsen Seyir, waɗanda ka hana Isra’ilawa su kai musu yaƙi sa’ad da suka fito daga ƙasar Masar, su ne mutanen da Isra’ila suka ƙyale, ba su hallaka su ba.
Un nu, redzi, Amona bērni un Moabs un tie no Seīra kalniem, kur Tu Israēlim neļāvi iet cauri, kad tie nāca no Ēģiptes zemes, bet tie no tiem atstājās un tos neizdeldēja, -
11 Yau ga yadda suke so su biya mu. Su suke so su kore mu daga ƙasar da ka ba mu gādo.
Redzi nu, tie mums to atmaksā, nākdami, mūs izdzīt no mūsu zemes, ko Tu mums licis iemantot.
12 Ya Allahnmu, ba za ka hukunta su ba? Gama ba mu da ƙarfin fuskantar wannan babbar rundunar da take so ta yaƙe mu. Ba mu san abin da za mu yi ba, mu dai mun zuba maka ido.”
Ak mūsu Dievs! Vai Tu nenesīsi tiesu pret viņiem? Jo mums nav spēka pret šo lielo pulku, kas pret mums nāk, un mēs nezinām, ko būs darīt, bet mūsu acis griežas uz Tevi.
13 Dukan mazan Yahuda, tare da matansu da yaransu da ƙananansu, suka tsaya a gaban Ubangiji.
Un visa Jūda valsts stāvēja Tā Kunga priekšā, arī viņu bērni, viņu sievas un viņu dēli.
14 Sa’an nan Ruhun Ubangiji ya sauko a kan Yahaziyel ɗan Zakariya, ɗan Benahiya, ɗan Yehiyel, ɗan Mattaniya, wani Balawe kuma zuriyar Asaf, yayinda yake tsaye a cikin taron.
Tad Tā Kunga Gars nāca draudzes vidū pār Jeaziēli, Zakarijas dēlu, tas bija Benajas, tas Jeiēļa, tas Levita Matanijas dēls, no Asafa bērniem.
15 Ya ce, “Saurara, Sarki Yehoshafat da dukan waɗanda suke zama a Yahuda da Urushalima! Ga abin da Ubangiji ya ce muku, ‘Kada ku ji tsoro ko ku fid da zuciya saboda wannan babbar runduna. Gama yaƙin ba naku ba ne, amma na Allah.
Un tas sacīja: klausāties, visa Jūda valsts un Jeruzālemes iedzīvotāji, un ķēniņ Jehošafat, - tā saka Tas Kungs uz jums: nebīstaties un neizbaiļojaties priekš šā lielā pulka, jo tas karš nepieder jums, bet Dievam.
16 Gobe ku fito ku gangara ku yaƙe su. Za su yi ta haurawa ta Mashigin Ziz, ku kuwa za ku same su a ƙarshen kwari a Hamadan Yeruwel.
Ejat rītu tiem pretī, redzi, tie nāks augšā pa Cic kalnu, un jūs tos sastapsiet ielejas galā šaipus Jeruēles tuksneša.
17 Ba lalle ba ne ku yi wannan yaƙi. Ku dai, ku ja dāgā, ku tsaya kurum ku ga nasarar da Ubangiji zai ba ku, ya Yahuda da Urushalima. Kada ku ji tsoro; kada ku karai. Ku fito don ku fuskance su gobe, Ubangiji kuwa zai kasance tare ku.’”
Šinī kaujā jums nebūs jākaujas, ejat tikai klāt, stāviet un redziet Tā Kunga pestīšanu, kas ir ar jums. Jūda un Jeruzāleme, nebīstaties un neizbaiļojaties, izejat rītu viņiem pretī, jo Tas Kungs būs ar jums.
18 Yehoshafat ya rusuna da fuskarsa har ƙasa, dukan mutanen Yahuda da Urushalima suka fāɗi rubda ciki suka yi sujada a gaban Ubangiji.
Tad Jehošafats locījās ar savu vaigu pie zemes, un visi Jūda un Jeruzālemes iedzīvotāji metās pie zemes priekš Tā Kunga un pielūdza To Kungu.
19 Sa’an nan waɗansu Lawiyawa daga Kohatawa da Korayawa suka tashi tsaye suka yabe Ubangiji, Allah na Isra’ila, da babbar murya sosai.
Un tie Leviti no Kehāta bērniem un no Koraha bērniem cēlās, augsti slavēt To Kungu, Israēla Dievu ar skanīgu balsi,
20 Da sassafe suka tashi suka nufi Hamadan Tekowa. Yayinda suka kama hanya, Yehoshafat ya tsaya ya ce, “Ku saurare ni, Yahuda da mutanen Urushalima! Ku amince da Ubangiji Allahnku za a kuwa kafa ku; ku amince da annabawansa za ku kuwa yi nasara.”
Un tie cēlās it agri un izgāja uz Tekoas tuksnesi, un tiem izejot Jehošafats stāvēja un sacīja: klausiet mani, Jūda un Jeruzālemes iedzīvotāji, ticiet uz To Kungu, savu Dievu, tad jūs pastāvēsiet; ticiet Viņa praviešiem, tad jums labi izdosies.
21 Bayan suka yi shawara tare da shugabanni, sai ya zaɓi mutanen da za su ja gaban sojoji suna waƙa ga Ubangiji suna yabonsa saboda tsarkinsa suna cewa, “Ku yi godiya ga Ubangiji, gama ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.”
Un viņš sarunājās ar tiem ļaudīm un iecēla dziedātājus priekš Tā Kunga, ka tie svētā glītumā slavētu, apbruņoto priekšā iedami un sacīdami: teiciet To Kungu, jo Viņa žēlastība paliek mūžīgi!
22 Da suka fara waƙa, suna kuma yabo, sai Ubangiji ya kai hari a kan mutanen Ammon da Mowab da Dutsen Seyir, waɗanda suka kawo hari a Yahuda, aka kuwa ci su da yaƙi.
Un to brīdi, kad tie sāka dziedāt tās priecīgās un teicamās dziesmas, tad Tas Kungs sūtīja glūnētājus pret Amona bērniem, Moabu un tiem no Seīra kalniem, kas bija nākuši uz Jūdu, un tie tika sakauti.
23 Mutanen Ammon da Mowab suka tasar wa mazaunan Dutsen Seyir, suka hallaka su ƙaƙaf. Sa’ad da suka karkashe mazaunan Seyir sai suka fāɗa wa juna, suka yi ta hallaka juna.
Jo Amona bērni un Moabs cēlās pret Seīra kalnu iedzīvotājiem un tos izdeldēja un nomaitāja, un kad tie visus Seīra iedzīvotājus bija nokāvuši, tad tie palīdzēja nomaitāt cits citu.
24 Sa’ad da mutanen Yahuda suka zo wurin da yake fuskantar hamada, suka duba ta wajen babban rundunar, sai suka ga gawawwaki birjik a ƙasa; babu wani wanda ya kuɓuta.
Un Jūda nāca kalna galā pie tuksneša un griezās pret tiem pulkiem, un redzi, tur bija miroņi, kas zemē gulēja, un neviens nebija izbēdzis.
25 Sa’ad da Yehoshafat da jama’arsa suka je kwasar ganima, sai suka sami shanu masu yawan gaske, da kayayyaki, da tufafi, da abubuwa masu daraja, waɗanda suka yi ta kwasa har suka gaji. Kwana uku suka yi suna kwasar ganimar saboda yawanta.
Tad Jehošafats un viņa ļaudis nāca un tos aplaupīja un atrada pie tiem ļoti daudz mantas un drēbes un dārgus rīkus, un paņēma tik daudz, ka nevarēja panest, un tie laupīja laupījumu trīs dienas, jo tur bija ļoti daudz.
26 A rana ta huɗu sai suka taru a Kwarin Beraka, inda suka yabi Ubangiji. Wannan ne ya sa ake kiransa Kwarin Beraka har wa yau.
Un ceturtā dienā tie sapulcējās teikšanas ielejā, jo tur tie teica To Kungu, tāpēc tie tās vietas vārdu nosauca Teikšanas ieleja līdz šai dienai.
27 Sa’an nan Yehoshafat ya jagoranci dukan mutanen Yahuda da Urushalima suka dawo da farin ciki zuwa Urushalima, gama Ubangiji ya ba su dalilin farin ciki a kan abokan gābansu.
Pēc tam visi vīri no Jūda un Jeruzālemes griezās atpakaļ, un Jehošafats viņu priekšā, un gāja uz Jeruzālemi ar prieku; jo Tas Kungs viņus bija darījis priecīgus par viņu ienaidniekiem.
28 Suka shiga Urushalima suka shiga haikalin Ubangiji da kiɗin molaye da sarewa da kuma garayu.
Un tie nonāca Jeruzālemē ar somastabulēm un koklēm un trumetēm uz Tā Kunga namu.
29 Tsoron Allah ya kama dukan mulkokin ƙasashe sa’ad da suka ji yadda Ubangiji ya yi yaƙi a kan abokan gāban Isra’ila.
Un bailes no Dieva nāca pār visām zemes valstīm, kad dzirdēja, ka Tas Kungs bija karojis pret Israēla ienaidniekiem.
30 Mulkin Yehoshafat kuwa ya zauna lafiya, gama Allahnsa ya ba shi hutu a kowane gefe.
Un Jehošafata valsts bija mierā, un viņa Dievs tam deva mieru visapkārt.
31 Ta haka Yehoshafat ya yi mulki a bisa Yahuda. Yana da shekara talatin da biyar sa’ad da ya zama sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ashirin da biyar. Sunan mahaifiyarsa Azuba ce,’yar Shilhi.
Un Jehošafats valdīja pār Jūdu; viņš bija trīsdesmit piecus gadus vecs, kad tas palika par ķēniņu, un valdīja divdesmit piecus gadus Jeruzālemē, un viņa mātei bija vārds Azuba, Šilkus meita.
32 Ya yi tafiya a hanyoyin mahaifinsa Asa bai kuwa kauce daga gare su ba; ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji.
Un viņš staigāja sava tēva Asas ceļos un neatstājās no tiem, darīdams, kas Tam Kungam patika.
33 Duk da haka ba a kawar da masujadai kan tudu ba, domin har yanzu mutanen ba su tsayar da zukatansu ga Allahn kakanninsu ba.
Taču kalnu altāri netapa nopostīti, un vēl tie ļaudis ar savu sirdi pilnīgi neturējās pie savu tēvu Dieva.
34 Sauran ayyukan mulkin Yehoshafat, daga farko zuwa ƙarshe, an rubuta su a tarihin Yehu ɗan Hanani, waɗanda aka rubuta a littafin sarakunan Isra’ila.
Un kas vēl par Jehošafatu stāstāms, par viņa pirmām un pēdējām dienām, redzi, tas rakstīts Jeūs, Anana dēla, stāstos, ko viņš sarakstījis Israēla ķēniņu grāmatā.
35 Daga baya, Yehoshafat sarkin Yahuda ya haɗa kai da Ahaziya sarkin Isra’ila, wanda yake da laifin mugunta.
Un pēc tam Jehošafats, Jūda ķēniņš, sabiedrojās ar Ahaziju, Israēla ķēniņu; tas bija bezdievīgs savos darbos.
36 Ya yarda da shi su gina jiragen ruwan kasuwanci. Bayan aka gina waɗannan a Eziyon Geber,
Un viņš ar to vienojās, kuģus taisīt, ar ko braukt uz Taršišu, un tie taisīja kuģus EceonĢeberā.
37 Eliyezer ɗan Dodabahu na Maresha ya yi annabci a kan Yehoshafat cewa, “Domin ka haɗa kai da Ahaziya, Ubangiji zai hallaka abin da ka yi.” Jiragen ruwan kuwa suka farfashe, ba a kuwa iya sa su je kasuwanci ba.
Bet Eliēzers, Dodava dēls, no Marezas, sludināja pret Jehošafatu sacīdams: tādēļ ka tu ar Ahaziju esi sabiedrojies, Tas Kungs salauzīs tavu darbu. Un tie kuģi tika sadragāti un nevarēja tikt uz Taršišu.

< 2 Tarihi 20 >