< 2 Tarihi 20 >

1 Bayan wannan, Mowabawa da Ammonawa tare da waɗansu Meyunawa suka zo su yaƙi Yehoshafat.
Après ces choses les enfants de Moab, et les enfants de Hammon vinrent, car les Hammonites s'étaient joints aux Moabites pour faire la guerre à Josaphat.
2 Sai waɗansu mutane suka zo suka faɗa wa Yehoshafat, “Ga babban runduna tana zuwa a kanka daga Edom, daga ƙetaren Teku, daga Aram. Ta ma kai Hazazon Tamar” (wato, En Gedi).
Et on vint faire ce rapport à Josaphat, en disant: Il est venu contre toi une grande multitude de gens, des quartiers de delà la mer, [et] de Syrie; et voici ils sont à Hatsa-tson-tamar, qui est Henguedi.
3 A firgice, Yehoshafat ya yanke shawara yă nemi nufin Ubangiji, ya kuma yi shelar azumi a dukan Yahuda.
Alors Josaphat craignit, et se disposa à rechercher l'Eternel, et publia le jeûne par tout Juda.
4 Mutanen Yahuda suka taru gaba ɗaya don su nemi taimako daga wurin Ubangiji, tabbatacce suka fito daga kowane garin Yahuda don su neme shi.
Ainsi Juda fut assemblé pour demander du secours à l'Eternel; et on vint de toutes les villes de Juda pour invoquer l'Eternel.
5 Sa’an nan Yehoshafat ya miƙe tsaye a taron Yahuda da Urushalima a haikalin Ubangiji a sabon filin
Et Josaphat se tint debout en l'assemblée de Juda et de Jérusalem dans la maison de l'Eternel, au devant du nouveau parvis.
6 ya ce, “Ya Ubangiji Allah na kakanninmu, ba kai ne Allah wanda yake sama ba? Kana mulki a bisa dukan mulkokin ƙasashe. Iko da girma suna a hannunka, kuma ba wanda zai iya tsayayya da kai.
Et il dit: Ô Eternel! Dieu de nos pères, n'es-tu pas le Dieu qui es aux cieux, et qui domines sur tous les Royaumes des nations? et certes en ta main est la force et la puissance, de sorte que nul ne peut te résister.
7 Ya Allahnmu, ba kai ba ne ka kore mazaunan wannan ƙasa a gaban mutanenka Isra’ila ka kuma ba da ita har abada ga zuriyar Ibrahim abokinka?
N'est-ce pas toi, ô notre Dieu! qui as dépossédé les habitants de ce pays de devant ton peuple d'Israël; et qui l'as donné pour toujours à la postérité d'Abraham, lequel t'aimait?
8 Sun yi zama a cikinta suka kuma yi gina wuri mai tsarki a cikinta domin Sunanka cewa,
De sorte qu'ils y ont habité, et t'y ont bâti un Sanctuaire pour ton Nom, en disant:
9 ‘In masifa ta zo mana, ko takobin hukunci, ko annoba ko yunwa, za mu tsaya a gabanka a gaban wannan haikalin da yake ɗauke da Sunanka, mu kuma yi kuka gare ka cikin azaba, za ka kuwa ji mu, ka cece mu.’
S'il nous arrive quelque mal, [savoir] l'épée de la vengeance, ou la peste, ou la famine, nous nous tiendrons devant cette maison et en ta présence; parce que ton Nom est en cette maison, nous crierons à toi à cause de notre angoisse, tu nous exauceras, et tu nous délivreras.
10 “Yanzu kuma ga mutanen Ammon, da na Mowab, da na Dutsen Seyir, waɗanda ka hana Isra’ilawa su kai musu yaƙi sa’ad da suka fito daga ƙasar Masar, su ne mutanen da Isra’ila suka ƙyale, ba su hallaka su ba.
Or maintenant voici, les enfants de Hammon et de Moab, et ceux du mont de Séhir, parmi lesquels tu ne permis point aux enfants d'Israël de passer quand ils venaient du pays d'Egypte, car ils se détournèrent d'eux, et ils ne les détruisirent point;
11 Yau ga yadda suke so su biya mu. Su suke so su kore mu daga ƙasar da ka ba mu gādo.
Voici, pour nous récompenser, ils viennent nous chasser de ton héritage, que tu nous as fait posséder.
12 Ya Allahnmu, ba za ka hukunta su ba? Gama ba mu da ƙarfin fuskantar wannan babbar rundunar da take so ta yaƙe mu. Ba mu san abin da za mu yi ba, mu dai mun zuba maka ido.”
Ô notre Dieu! ne les jugeras-tu pas? vu qu'il n'y a point de force en nous [pour subsister] devant cette grande multitude qui vient contre nous, et nous ne savons ce que nous devons faire; mais nos yeux sont sur toi.
13 Dukan mazan Yahuda, tare da matansu da yaransu da ƙananansu, suka tsaya a gaban Ubangiji.
Et tous ceux de Juda se tenaient debout devant l'Eternel, avec leurs familles, leurs femmes, et leurs enfants.
14 Sa’an nan Ruhun Ubangiji ya sauko a kan Yahaziyel ɗan Zakariya, ɗan Benahiya, ɗan Yehiyel, ɗan Mattaniya, wani Balawe kuma zuriyar Asaf, yayinda yake tsaye a cikin taron.
Alors l'Esprit de l'Eternel fut sur Jahaziël, fils de Zacharie, fils de Bénéia, fils de Jéhiël, fils de Mattania Lévite d'entre les enfants d'Asaph, au milieu de l'assemblée.
15 Ya ce, “Saurara, Sarki Yehoshafat da dukan waɗanda suke zama a Yahuda da Urushalima! Ga abin da Ubangiji ya ce muku, ‘Kada ku ji tsoro ko ku fid da zuciya saboda wannan babbar runduna. Gama yaƙin ba naku ba ne, amma na Allah.
Et il dit: Vous tous de Juda, et vous qui habitez à Jérusalem, et toi, Roi Josaphat, soyez attentifs. L'Eternel vous parle ainsi: Ne craignez point, et ne soyez point effrayés à cause de cette grande multitude; car ce ne sera pas à vous de conduire cette guerre, mais à Dieu.
16 Gobe ku fito ku gangara ku yaƙe su. Za su yi ta haurawa ta Mashigin Ziz, ku kuwa za ku same su a ƙarshen kwari a Hamadan Yeruwel.
Descendez demain vers eux; voici, ils vont monter par la montée de Tsits, et vous les trouverez au bout du torrent, vis-à-vis du désert de Jéruël.
17 Ba lalle ba ne ku yi wannan yaƙi. Ku dai, ku ja dāgā, ku tsaya kurum ku ga nasarar da Ubangiji zai ba ku, ya Yahuda da Urushalima. Kada ku ji tsoro; kada ku karai. Ku fito don ku fuskance su gobe, Ubangiji kuwa zai kasance tare ku.’”
Ce ne sera point à vous à combattre dans cette bataille, présentez-vous, tenez-vous debout, et voyez la délivrance que l'Eternel vous va donner. Juda et Jérusalem, ne craignez point, et ne soyez point effrayés; sortez demain au devant d'eux, car l'Eternel sera avec vous.
18 Yehoshafat ya rusuna da fuskarsa har ƙasa, dukan mutanen Yahuda da Urushalima suka fāɗi rubda ciki suka yi sujada a gaban Ubangiji.
Alors Josaphat s'inclina le visage contre terre, et tout Juda et les habitants de Jérusalem se jetèrent devant l'Eternel, se prosternant devant l'Eternel.
19 Sa’an nan waɗansu Lawiyawa daga Kohatawa da Korayawa suka tashi tsaye suka yabe Ubangiji, Allah na Isra’ila, da babbar murya sosai.
Et les Lévites d'entre les enfants des Kéhathites, et d'entre les enfants des Corites, se levèrent pour louer d'une voix haute et éclatante l'Eternel le Dieu d'Israël.
20 Da sassafe suka tashi suka nufi Hamadan Tekowa. Yayinda suka kama hanya, Yehoshafat ya tsaya ya ce, “Ku saurare ni, Yahuda da mutanen Urushalima! Ku amince da Ubangiji Allahnku za a kuwa kafa ku; ku amince da annabawansa za ku kuwa yi nasara.”
Puis ils se levèrent de grand matin, et sortirent vers le désert de Tékoah, et comme ils sortaient, Josaphat se tenant debout, dit: Juda, et vous habitants de Jérusalem, écoutez-moi. Croyez en l'Eternel votre Dieu, et vous serez en sûreté; croyez ses Prophètes, et vous prospérerez.
21 Bayan suka yi shawara tare da shugabanni, sai ya zaɓi mutanen da za su ja gaban sojoji suna waƙa ga Ubangiji suna yabonsa saboda tsarkinsa suna cewa, “Ku yi godiya ga Ubangiji, gama ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.”
Puis ayant consulté avec le peuple, il établit des gens pour chanter à l'Eternel et pour louer sa sainte magnificence, [lesquels] marchant devant l'armée, disaient: Célébrez l'Eternel, car sa gratuité demeure à toujours.
22 Da suka fara waƙa, suna kuma yabo, sai Ubangiji ya kai hari a kan mutanen Ammon da Mowab da Dutsen Seyir, waɗanda suka kawo hari a Yahuda, aka kuwa ci su da yaƙi.
Et à l'heure qu'ils commencèrent le chant du triomphe et la louange, l'Eternel mit des embûches contre les enfants de Hammon, les Moabites, et ceux du mont de Séhir, qui venaient contre Juda, de sorte qu'ils furent battus.
23 Mutanen Ammon da Mowab suka tasar wa mazaunan Dutsen Seyir, suka hallaka su ƙaƙaf. Sa’ad da suka karkashe mazaunan Seyir sai suka fāɗa wa juna, suka yi ta hallaka juna.
Car les enfants de Hammon et les Moabites s'élevèrent contre les habitants du mont de Séhir, pour les détruire à la façon de l'interdit, et pour les exterminer; et quand ils eurent achevé d'exterminer les habitants de Séhir, ils s'aidèrent l'un l'autre à se détruire mutuellement.
24 Sa’ad da mutanen Yahuda suka zo wurin da yake fuskantar hamada, suka duba ta wajen babban rundunar, sai suka ga gawawwaki birjik a ƙasa; babu wani wanda ya kuɓuta.
Et ceux de Juda vinrent jusqu'à l'endroit de Mitspa au désert, et regardant vers cette multitude, voilà, c'étaient tous des corps abattus par terre, sans qu'il en fût échappé un seul.
25 Sa’ad da Yehoshafat da jama’arsa suka je kwasar ganima, sai suka sami shanu masu yawan gaske, da kayayyaki, da tufafi, da abubuwa masu daraja, waɗanda suka yi ta kwasa har suka gaji. Kwana uku suka yi suna kwasar ganimar saboda yawanta.
Ainsi Josaphat et son peuple vinrent pour piller leur butin, et ils trouvèrent de grandes richesses parmi les morts, et des hardes précieuses, et ils en prirent tant, qu'ils n'en pouvaient plus porter; ils pillèrent le butin pendant trois jours, car il y en avait en abondance.
26 A rana ta huɗu sai suka taru a Kwarin Beraka, inda suka yabi Ubangiji. Wannan ne ya sa ake kiransa Kwarin Beraka har wa yau.
Puis au quatrième jour ils s'assemblèrent dans la vallée [appelée] de bénédiction, parce qu'ils bénirent là l'Eternel; c'est pourquoi on a appelé ce lieu-là, la vallée de bénédiction, jusqu'à ce jour.
27 Sa’an nan Yehoshafat ya jagoranci dukan mutanen Yahuda da Urushalima suka dawo da farin ciki zuwa Urushalima, gama Ubangiji ya ba su dalilin farin ciki a kan abokan gābansu.
Et tous les hommes de Juda et de Jérusalem, et Josaphat marchant le premier, tournèrent visage pour revenir à Jérusalem avec joie: car l'Eternel les avait remplis de joie à cause de leurs ennemis.
28 Suka shiga Urushalima suka shiga haikalin Ubangiji da kiɗin molaye da sarewa da kuma garayu.
Et ils entrèrent à Jérusalem dans la maison de l'Eternel, avec des musettes, des violons, et des trompettes.
29 Tsoron Allah ya kama dukan mulkokin ƙasashe sa’ad da suka ji yadda Ubangiji ya yi yaƙi a kan abokan gāban Isra’ila.
Et la frayeur de Dieu fut sur tous les Royaumes de ce pays-là, quand ils eurent appris que l'Eternel avait combattu contre les ennemis d'Israël.
30 Mulkin Yehoshafat kuwa ya zauna lafiya, gama Allahnsa ya ba shi hutu a kowane gefe.
Ainsi le Royaume de Josaphat fut en repos, parce que son Dieu lui donna du repos tout à l'entour.
31 Ta haka Yehoshafat ya yi mulki a bisa Yahuda. Yana da shekara talatin da biyar sa’ad da ya zama sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ashirin da biyar. Sunan mahaifiyarsa Azuba ce,’yar Shilhi.
Josaphat donc régna sur Juda. Il était âgé de trente-cinq ans quand il commença à régner, et il régna vingt-cinq ans à Jérusalem; sa mère avait nom Hazuba, et elle était fille de Silhi.
32 Ya yi tafiya a hanyoyin mahaifinsa Asa bai kuwa kauce daga gare su ba; ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji.
Il suivit la voie d'Asa son père, et ne s'en détourna point, faisant ce qui est droit devant l'Eternel.
33 Duk da haka ba a kawar da masujadai kan tudu ba, domin har yanzu mutanen ba su tsayar da zukatansu ga Allahn kakanninsu ba.
Toutefois les hauts lieux ne furent point ôtés, parce que le peuple n'avait pas encore disposé son cœur envers le Dieu de ses pères.
34 Sauran ayyukan mulkin Yehoshafat, daga farko zuwa ƙarshe, an rubuta su a tarihin Yehu ɗan Hanani, waɗanda aka rubuta a littafin sarakunan Isra’ila.
Or le reste des faits de Josaphat, tant les premiers que les derniers, voilà ils sont écrits dans les Mémoires de Jéhu fils de Hanani, selon qu'il a été enregistré au Livre des Rois d'Israël.
35 Daga baya, Yehoshafat sarkin Yahuda ya haɗa kai da Ahaziya sarkin Isra’ila, wanda yake da laifin mugunta.
Après cela Josaphat Roi de Juda se joignit à Achazia Roi d'Israël, qui ne s'employait qu'à faire du mal.
36 Ya yarda da shi su gina jiragen ruwan kasuwanci. Bayan aka gina waɗannan a Eziyon Geber,
Et il s'associa avec lui pour faire des navires et pour les envoyer en Tarsis; et ils firent ces navires à Hetsjonguéber.
37 Eliyezer ɗan Dodabahu na Maresha ya yi annabci a kan Yehoshafat cewa, “Domin ka haɗa kai da Ahaziya, Ubangiji zai hallaka abin da ka yi.” Jiragen ruwan kuwa suka farfashe, ba a kuwa iya sa su je kasuwanci ba.
Alors Elihézer fils de Dodava, de Marésa, prophétisa contre Josaphat, en disant: Parce que tu t'es joint à Achazia, l'Eternel a détruit tes ouvrages. Les navires donc furent brisés, et ils ne purent point aller en Tarsis.

< 2 Tarihi 20 >