< 2 Tarihi 20 >
1 Bayan wannan, Mowabawa da Ammonawa tare da waɗansu Meyunawa suka zo su yaƙi Yehoshafat.
And it cometh to pass after this, the sons of Moab have come in, and the sons of Ammon, and with them of the peoples, against Jehoshaphat to battle.
2 Sai waɗansu mutane suka zo suka faɗa wa Yehoshafat, “Ga babban runduna tana zuwa a kanka daga Edom, daga ƙetaren Teku, daga Aram. Ta ma kai Hazazon Tamar” (wato, En Gedi).
And they come in and declare to Jehoshaphat, saying, 'Come against thee hath a great multitude from beyond the sea, from Aram, and lo, they [are] in Hazezon-Tamar — it [is] En-Gedi.'
3 A firgice, Yehoshafat ya yanke shawara yă nemi nufin Ubangiji, ya kuma yi shelar azumi a dukan Yahuda.
And Jehoshaphat feareth, and setteth his face to seek to Jehovah, and proclaimeth a fast over all Judah;
4 Mutanen Yahuda suka taru gaba ɗaya don su nemi taimako daga wurin Ubangiji, tabbatacce suka fito daga kowane garin Yahuda don su neme shi.
and Judah is gathered to inquire of Jehovah; also, from all the cities of Judah they have come in to seek Jehovah.
5 Sa’an nan Yehoshafat ya miƙe tsaye a taron Yahuda da Urushalima a haikalin Ubangiji a sabon filin
And Jehoshaphat standeth in the assembly of Judah and Jerusalem, in the house of Jehovah, at the front of the new court,
6 ya ce, “Ya Ubangiji Allah na kakanninmu, ba kai ne Allah wanda yake sama ba? Kana mulki a bisa dukan mulkokin ƙasashe. Iko da girma suna a hannunka, kuma ba wanda zai iya tsayayya da kai.
and saith, 'O Jehovah, God of our fathers, art not Thou — God in the heavens? yea, Thou art ruling over all kingdoms of the nations, and in Thy hand [is] power and might, and there is none with Thee to station himself.
7 Ya Allahnmu, ba kai ba ne ka kore mazaunan wannan ƙasa a gaban mutanenka Isra’ila ka kuma ba da ita har abada ga zuriyar Ibrahim abokinka?
'Art not Thou our God? Thou hast dispossessed the inhabitants of this land from before Thy people Israel, and dost give it to the seed of Abraham Thy friend to the age,
8 Sun yi zama a cikinta suka kuma yi gina wuri mai tsarki a cikinta domin Sunanka cewa,
and they dwell in it, and build to Thee in it a sanctuary for Thy name, saying,
9 ‘In masifa ta zo mana, ko takobin hukunci, ko annoba ko yunwa, za mu tsaya a gabanka a gaban wannan haikalin da yake ɗauke da Sunanka, mu kuma yi kuka gare ka cikin azaba, za ka kuwa ji mu, ka cece mu.’
If evil doth come upon us — sword, judgment, and pestilence, and famine — we stand before this house, and before Thee, for Thy name [is] in this house, and cry unto Thee out of our distress, and Thou dost hear and save.
10 “Yanzu kuma ga mutanen Ammon, da na Mowab, da na Dutsen Seyir, waɗanda ka hana Isra’ilawa su kai musu yaƙi sa’ad da suka fito daga ƙasar Masar, su ne mutanen da Isra’ila suka ƙyale, ba su hallaka su ba.
'And now, lo, sons of Ammon, and Moab, and mount Seir, whom Thou didst not grant to Israel to go in against in their coming out of the land of Egypt, for they turned aside from off them and destroyed them not,
11 Yau ga yadda suke so su biya mu. Su suke so su kore mu daga ƙasar da ka ba mu gādo.
and lo, they are recompensing to us — to come in to drive us out of Thy possession, that Thou hast caused us to possess.
12 Ya Allahnmu, ba za ka hukunta su ba? Gama ba mu da ƙarfin fuskantar wannan babbar rundunar da take so ta yaƙe mu. Ba mu san abin da za mu yi ba, mu dai mun zuba maka ido.”
'O our God, dost Thou not execute judgment upon them? for there is no power in us before this great multitude that hath come against us, and we know not what we do, but on Thee [are] our eyes.'
13 Dukan mazan Yahuda, tare da matansu da yaransu da ƙananansu, suka tsaya a gaban Ubangiji.
And all Judah are standing before Jehovah, also their infants, their wives, and their sons.
14 Sa’an nan Ruhun Ubangiji ya sauko a kan Yahaziyel ɗan Zakariya, ɗan Benahiya, ɗan Yehiyel, ɗan Mattaniya, wani Balawe kuma zuriyar Asaf, yayinda yake tsaye a cikin taron.
And upon Jahaziel, son of Zechariah, son of Benaiah, son of Jeiel, son of Mattaniah, the Levite, of the sons of Asaph, hath the Spirit of Jehovah been, in the midst of the assembly,
15 Ya ce, “Saurara, Sarki Yehoshafat da dukan waɗanda suke zama a Yahuda da Urushalima! Ga abin da Ubangiji ya ce muku, ‘Kada ku ji tsoro ko ku fid da zuciya saboda wannan babbar runduna. Gama yaƙin ba naku ba ne, amma na Allah.
and he saith, 'Attend, all Judah, and ye inhabitants of Jerusalem, and O king Jehoshaphat, Thus said Jehovah to you, Ye fear not, nor are afraid of the face of this great multitude, for not for you [is] the battle, but for God.
16 Gobe ku fito ku gangara ku yaƙe su. Za su yi ta haurawa ta Mashigin Ziz, ku kuwa za ku same su a ƙarshen kwari a Hamadan Yeruwel.
To-morrow, go ye down against them, lo, they are coming up by the ascent of Ziz, and ye have found them in the end of the valley, the front of the wilderness of Jeruel.
17 Ba lalle ba ne ku yi wannan yaƙi. Ku dai, ku ja dāgā, ku tsaya kurum ku ga nasarar da Ubangiji zai ba ku, ya Yahuda da Urushalima. Kada ku ji tsoro; kada ku karai. Ku fito don ku fuskance su gobe, Ubangiji kuwa zai kasance tare ku.’”
Not for you to fight in this; station yourselves, stand, and see the salvation of Jehovah with you, O Judah and Jerusalem — be not afraid nor fear ye — to-morrow go out before them, and Jehovah [is] with you.'
18 Yehoshafat ya rusuna da fuskarsa har ƙasa, dukan mutanen Yahuda da Urushalima suka fāɗi rubda ciki suka yi sujada a gaban Ubangiji.
And Jehoshaphat boweth — face to the earth — and all Judah and the inhabitants of Jerusalem have fallen before Jehovah, to bow themselves to Jehovah.
19 Sa’an nan waɗansu Lawiyawa daga Kohatawa da Korayawa suka tashi tsaye suka yabe Ubangiji, Allah na Isra’ila, da babbar murya sosai.
And the Levites, of the sons of the Kohathites, and of the sons of the Korhites, rise to give praise to Jehovah, God of Israel, with a loud voice on high.
20 Da sassafe suka tashi suka nufi Hamadan Tekowa. Yayinda suka kama hanya, Yehoshafat ya tsaya ya ce, “Ku saurare ni, Yahuda da mutanen Urushalima! Ku amince da Ubangiji Allahnku za a kuwa kafa ku; ku amince da annabawansa za ku kuwa yi nasara.”
And they rise early in the morning, and go out to the wilderness of Tekoa, and in their going out Jehoshaphat hath stood and saith, 'Hear me, O Judah, and inhabitants of Jerusalem, remain stedfast in Jehovah your God, and be stedfast; remain stedfast in His prophets, and prosper.'
21 Bayan suka yi shawara tare da shugabanni, sai ya zaɓi mutanen da za su ja gaban sojoji suna waƙa ga Ubangiji suna yabonsa saboda tsarkinsa suna cewa, “Ku yi godiya ga Ubangiji, gama ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.”
And he taketh counsel with the people, and appointeth singers to Jehovah, and those giving praise to the honour of holiness, in the going out before the armed [men], and saying, 'Give ye thanks to Jehovah, for to the age [is] His kindness.'
22 Da suka fara waƙa, suna kuma yabo, sai Ubangiji ya kai hari a kan mutanen Ammon da Mowab da Dutsen Seyir, waɗanda suka kawo hari a Yahuda, aka kuwa ci su da yaƙi.
And at the time they have begun with singing and praise, Jehovah hath put ambushments against the sons of Ammon, Moab, and mount Seir, who are coming in to Judah, and they are smitten,
23 Mutanen Ammon da Mowab suka tasar wa mazaunan Dutsen Seyir, suka hallaka su ƙaƙaf. Sa’ad da suka karkashe mazaunan Seyir sai suka fāɗa wa juna, suka yi ta hallaka juna.
and the sons of Ammon stand up, and Moab, against the inhabitants of mount Seir, to devote and to destroy, and at their finishing with the inhabitants of Seir, they helped, a man against his neighbour, to destroy.
24 Sa’ad da mutanen Yahuda suka zo wurin da yake fuskantar hamada, suka duba ta wajen babban rundunar, sai suka ga gawawwaki birjik a ƙasa; babu wani wanda ya kuɓuta.
And Judah hath come in unto the watch-tower, to the wilderness, and they look unto the multitude, and lo, they [are] carcases fallen to the earth, and there is none escaped,
25 Sa’ad da Yehoshafat da jama’arsa suka je kwasar ganima, sai suka sami shanu masu yawan gaske, da kayayyaki, da tufafi, da abubuwa masu daraja, waɗanda suka yi ta kwasa har suka gaji. Kwana uku suka yi suna kwasar ganimar saboda yawanta.
and Jehoshaphat cometh in, and his people, to seize their spoil, and they find among them, in abundance, both goods and carcases, and desirable vessels, and they take spoil to themselves without prohibition, and they are three days seizing the spoil, for it [is] abundant.
26 A rana ta huɗu sai suka taru a Kwarin Beraka, inda suka yabi Ubangiji. Wannan ne ya sa ake kiransa Kwarin Beraka har wa yau.
And on the fourth day they have been assembled at the valley of Blessing, for there they blessed Jehovah: therefore they have called the name of that place, 'Valley of Blessing,' unto this day.
27 Sa’an nan Yehoshafat ya jagoranci dukan mutanen Yahuda da Urushalima suka dawo da farin ciki zuwa Urushalima, gama Ubangiji ya ba su dalilin farin ciki a kan abokan gābansu.
And they turn back, every man of Judah and Jerusalem, and Jehoshaphat at their head, to go back unto Jerusalem with joy, for Jehovah hath made them rejoice over their enemies.
28 Suka shiga Urushalima suka shiga haikalin Ubangiji da kiɗin molaye da sarewa da kuma garayu.
And they come in to Jerusalem with psalteries, and with harps, and with trumpets, unto the house of Jehovah.
29 Tsoron Allah ya kama dukan mulkokin ƙasashe sa’ad da suka ji yadda Ubangiji ya yi yaƙi a kan abokan gāban Isra’ila.
And there is a fear of God on all kingdoms of the lands in their hearing that Jehovah hath fought with the enemies of Israel,
30 Mulkin Yehoshafat kuwa ya zauna lafiya, gama Allahnsa ya ba shi hutu a kowane gefe.
and the kingdom of Jehoshaphat is quiet, and his God giveth rest to him round about.
31 Ta haka Yehoshafat ya yi mulki a bisa Yahuda. Yana da shekara talatin da biyar sa’ad da ya zama sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ashirin da biyar. Sunan mahaifiyarsa Azuba ce,’yar Shilhi.
And Jehoshaphat reigneth over Judah, a son of thirty and five years in his reigning, and twenty and five years he hath reigned in Jerusalem, and the name of his mother [is] Azubah daughter of Shilhi.
32 Ya yi tafiya a hanyoyin mahaifinsa Asa bai kuwa kauce daga gare su ba; ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji.
And he walketh in the way of his father Asa, and hath not turned aside from it, to do that which is right in the eyes of Jehovah.
33 Duk da haka ba a kawar da masujadai kan tudu ba, domin har yanzu mutanen ba su tsayar da zukatansu ga Allahn kakanninsu ba.
Only, the high places have not turned aside, and still the people have not prepared their heart for the God of their fathers.
34 Sauran ayyukan mulkin Yehoshafat, daga farko zuwa ƙarshe, an rubuta su a tarihin Yehu ɗan Hanani, waɗanda aka rubuta a littafin sarakunan Isra’ila.
And the rest of the matters of Jehoshaphat, the first and the last, lo, they are written among the matters of Jehu son of Hanani, who hath been mentioned on the book of the kings of Israel.
35 Daga baya, Yehoshafat sarkin Yahuda ya haɗa kai da Ahaziya sarkin Isra’ila, wanda yake da laifin mugunta.
And after this hath Jehoshaphat king of Judah joined himself with Ahaziah king of Israel, (he did wickedly in [so] doing),
36 Ya yarda da shi su gina jiragen ruwan kasuwanci. Bayan aka gina waɗannan a Eziyon Geber,
and he joineth him with himself to make ships to go to Tarshish, and they make ships in Ezion-Geber,
37 Eliyezer ɗan Dodabahu na Maresha ya yi annabci a kan Yehoshafat cewa, “Domin ka haɗa kai da Ahaziya, Ubangiji zai hallaka abin da ka yi.” Jiragen ruwan kuwa suka farfashe, ba a kuwa iya sa su je kasuwanci ba.
and prophesy doth Eliezer son of Dodavah, of Mareshah, against Jehoshaphat, saying, 'For thy joining thyself with Ahaziah, Jehovah hath broken up thy works;' and the ships are broken, and have not retained [power] to go unto Tarshish.