< 2 Tarihi 20 >

1 Bayan wannan, Mowabawa da Ammonawa tare da waɗansu Meyunawa suka zo su yaƙi Yehoshafat.
Aftir these thingis the sones of Moab, and the sones of Amon, and with hem of Idumeis, weren gaderid togidere to Josaphat, for to fiyte ayens hym.
2 Sai waɗansu mutane suka zo suka faɗa wa Yehoshafat, “Ga babban runduna tana zuwa a kanka daga Edom, daga ƙetaren Teku, daga Aram. Ta ma kai Hazazon Tamar” (wato, En Gedi).
And messangeris camen, and schewiden to Josaphat, seiden, A greet multitude of tho placis that ben biyondis the see, and of Sirie, is comun ayens thee; and, lo! thei stonden in Asasonthamar, which is Engaddi.
3 A firgice, Yehoshafat ya yanke shawara yă nemi nufin Ubangiji, ya kuma yi shelar azumi a dukan Yahuda.
Forsothe Josaphat was aferd by drede, and `yaf hym silf al for to preye `the Lord, and prechide fastynge to al Juda.
4 Mutanen Yahuda suka taru gaba ɗaya don su nemi taimako daga wurin Ubangiji, tabbatacce suka fito daga kowane garin Yahuda don su neme shi.
And Juda was gaderid togidere for to preye the Lord, but also alle men camen fro her citees for to biseche hym.
5 Sa’an nan Yehoshafat ya miƙe tsaye a taron Yahuda da Urushalima a haikalin Ubangiji a sabon filin
And whanne Josaphat hadde stonde in the myddis of the cumpeny of Juda and of Jerusalem, in the hows of the Lord, bifor the newe large place,
6 ya ce, “Ya Ubangiji Allah na kakanninmu, ba kai ne Allah wanda yake sama ba? Kana mulki a bisa dukan mulkokin ƙasashe. Iko da girma suna a hannunka, kuma ba wanda zai iya tsayayya da kai.
he seide, Lord God of oure fadris, thou art God in heuene, and thou art lord of alle rewmes of folkis; strengthe and power ben in thin hond, `and noon may ayenstonde thee.
7 Ya Allahnmu, ba kai ba ne ka kore mazaunan wannan ƙasa a gaban mutanenka Isra’ila ka kuma ba da ita har abada ga zuriyar Ibrahim abokinka?
Whether not thou, oure God, hast slayn alle the dwelleris of this lond bifor thi puple Israel, and hast youe it to the seed of Abraham, thi freend, withouten ende?
8 Sun yi zama a cikinta suka kuma yi gina wuri mai tsarki a cikinta domin Sunanka cewa,
And thei dwelliden therynne, and bildiden therinne a seyntuarie to thi name, and seiden,
9 ‘In masifa ta zo mana, ko takobin hukunci, ko annoba ko yunwa, za mu tsaya a gabanka a gaban wannan haikalin da yake ɗauke da Sunanka, mu kuma yi kuka gare ka cikin azaba, za ka kuwa ji mu, ka cece mu.’
If yuelis comen on vs, the swerd of doom, pestilence, and hungur, we schulen stonde bifor this hows withouten ende in thi siyt, in which hows thi name is clepid, and we schulen crie to thee in oure tribulaciouns; and thou schalt here vs, and schalt make vs saaf.
10 “Yanzu kuma ga mutanen Ammon, da na Mowab, da na Dutsen Seyir, waɗanda ka hana Isra’ilawa su kai musu yaƙi sa’ad da suka fito daga ƙasar Masar, su ne mutanen da Isra’ila suka ƙyale, ba su hallaka su ba.
Now therfor lo! the sones of Amon and of Moab and the hil of Seir, bi whiche thou grauntidist not to the sones of Israel for to passe, whanne thei yeden out of Egipt, but thei bowiden awei fro hem, and killiden not hem,
11 Yau ga yadda suke so su biya mu. Su suke so su kore mu daga ƙasar da ka ba mu gādo.
thei doon ayenward, and enforsen to caste vs out of the possessioun, which thou, oure God, hast youe to vs;
12 Ya Allahnmu, ba za ka hukunta su ba? Gama ba mu da ƙarfin fuskantar wannan babbar rundunar da take so ta yaƙe mu. Ba mu san abin da za mu yi ba, mu dai mun zuba maka ido.”
therfor whether thou schalt not deme hem? Treuli in vs is not so greet strengthe, that we moun ayenstonde this multitude, that felde yn on vs; but sithen we witen not what we owen to do, we `han oneli this residue, that we dresse oure iyen to thee.
13 Dukan mazan Yahuda, tare da matansu da yaransu da ƙananansu, suka tsaya a gaban Ubangiji.
Sotheli al Juda stood bifor the Lord, with her litle children and wyues and fre children.
14 Sa’an nan Ruhun Ubangiji ya sauko a kan Yahaziyel ɗan Zakariya, ɗan Benahiya, ɗan Yehiyel, ɗan Mattaniya, wani Balawe kuma zuriyar Asaf, yayinda yake tsaye a cikin taron.
Forsothe Hiaziel, the sone of Zacarie, sone of Ananye, sone of Hieyel, sone of Machanye, was a dekene, and of the sones of Asaph, on whom the Spirit of the Lord was maad in the myddis of the cumpeny,
15 Ya ce, “Saurara, Sarki Yehoshafat da dukan waɗanda suke zama a Yahuda da Urushalima! Ga abin da Ubangiji ya ce muku, ‘Kada ku ji tsoro ko ku fid da zuciya saboda wannan babbar runduna. Gama yaƙin ba naku ba ne, amma na Allah.
and he seide, Al Juda, and ye that dwellen in Jerusalem, and thou, king Josaphat, perseyue ye, the Lord seith these thingis to you, Nyle ye drede, nether be ye aferd of this multitude, for it is not youre batel, but Goddis batel.
16 Gobe ku fito ku gangara ku yaƙe su. Za su yi ta haurawa ta Mashigin Ziz, ku kuwa za ku same su a ƙarshen kwari a Hamadan Yeruwel.
To morewe ye schulen stie `ayens hem; for thei schulen stie bi the side of the hil, `bi name Seys, and ye schulen fynde hem in the hiynesse of the stronde, which is ayens the wildirnesse of Jheruhel.
17 Ba lalle ba ne ku yi wannan yaƙi. Ku dai, ku ja dāgā, ku tsaya kurum ku ga nasarar da Ubangiji zai ba ku, ya Yahuda da Urushalima. Kada ku ji tsoro; kada ku karai. Ku fito don ku fuskance su gobe, Ubangiji kuwa zai kasance tare ku.’”
For it schulen not be ye, that schulen fiyte; but oneli stonde ye trustili, and ye schulen se the help of the Lord on you. A! Juda and Jerusalem, nyle ye drede, nether be ye aferd; to morewe ye schulen go out ayens hem, and the Lord schal be with you.
18 Yehoshafat ya rusuna da fuskarsa har ƙasa, dukan mutanen Yahuda da Urushalima suka fāɗi rubda ciki suka yi sujada a gaban Ubangiji.
Therfor Josaphat, and Juda, and alle the dwelleris of Jerusalem, felden lowli on the erthe bifor the Lord, and worschypiden hym.
19 Sa’an nan waɗansu Lawiyawa daga Kohatawa da Korayawa suka tashi tsaye suka yabe Ubangiji, Allah na Isra’ila, da babbar murya sosai.
Forsothe the dekenes of the sones of Caath, and of the sones of Chore, herieden the Lord God of Israel with greet vois an hiy.
20 Da sassafe suka tashi suka nufi Hamadan Tekowa. Yayinda suka kama hanya, Yehoshafat ya tsaya ya ce, “Ku saurare ni, Yahuda da mutanen Urushalima! Ku amince da Ubangiji Allahnku za a kuwa kafa ku; ku amince da annabawansa za ku kuwa yi nasara.”
And whanne thei hadden rise eerli, thei yeden not bi the deseert of Thecue; and whanne thei `hadden gon forth, Josaphat stood in the myddis of hem, and seide, Juda and alle the dwelleris of Jerusalem, here ye me; bileue ye in `youre Lord God, and ye schulen be sikur; bileue ye to hise prophetis, and alle prosperitees schulen come.
21 Bayan suka yi shawara tare da shugabanni, sai ya zaɓi mutanen da za su ja gaban sojoji suna waƙa ga Ubangiji suna yabonsa saboda tsarkinsa suna cewa, “Ku yi godiya ga Ubangiji, gama ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.”
And he yaf counsel to the puple, and he ordeynede the syngeris of the Lord, that thei schulden herye hym in her cumpanyes, and that thei schulden go bifor the oost, and seie with acordynge vois, Knouleche ye to the Lord, for he is good; for his merci is `in to the world.
22 Da suka fara waƙa, suna kuma yabo, sai Ubangiji ya kai hari a kan mutanen Ammon da Mowab da Dutsen Seyir, waɗanda suka kawo hari a Yahuda, aka kuwa ci su da yaƙi.
And whanne thei bigunnen to synge heriyngis, the Lord turnede the buyschementis of hem `in to hem silf, that is, of the sones of Amon and of Moab and of the hil of Seir, that yeden out to fiyte ayens Juda; and thei weren slayn.
23 Mutanen Ammon da Mowab suka tasar wa mazaunan Dutsen Seyir, suka hallaka su ƙaƙaf. Sa’ad da suka karkashe mazaunan Seyir sai suka fāɗa wa juna, suka yi ta hallaka juna.
For whi the sones of Amon and of Moab risiden togidere ayens the dwelleris of the hil of Seir, to sle, and to do awey hem; and whanne thei hadden do this in werk, thei weren `turned also `in to hem silf, and felden doun togidere bi woundis ech of othere.
24 Sa’ad da mutanen Yahuda suka zo wurin da yake fuskantar hamada, suka duba ta wajen babban rundunar, sai suka ga gawawwaki birjik a ƙasa; babu wani wanda ya kuɓuta.
Certis whanne Juda was comun to the denne, that biholdith the wildirnesse, he siy afer al the large cuntrei ful of deed bodies, and that noon was left, that miyte ascape deeth.
25 Sa’ad da Yehoshafat da jama’arsa suka je kwasar ganima, sai suka sami shanu masu yawan gaske, da kayayyaki, da tufafi, da abubuwa masu daraja, waɗanda suka yi ta kwasa har suka gaji. Kwana uku suka yi suna kwasar ganimar saboda yawanta.
Therfor Josaphat cam, and al the puple with hym, to drawe awey the spuylis of deed men, and thei founden among the deed bodies dyuerse purtenaunce of houshold, and clothis, and ful preciouse vessels; and thei rauyischiden in dyuerse maneres, so that thei myyten not bere alle thingis, nether thei myyten take awei the spuylis bi thre daies, for the greetnesse of prey.
26 A rana ta huɗu sai suka taru a Kwarin Beraka, inda suka yabi Ubangiji. Wannan ne ya sa ake kiransa Kwarin Beraka har wa yau.
Sotheli in the fourthe dai thei weren gaderid togidere in the valey of Blessyng; `forsothe for thei blessiden the Lord there, thei clepiden that place the valei of Blessyng `til in to present dai.
27 Sa’an nan Yehoshafat ya jagoranci dukan mutanen Yahuda da Urushalima suka dawo da farin ciki zuwa Urushalima, gama Ubangiji ya ba su dalilin farin ciki a kan abokan gābansu.
And ech man of Juda turnede ayen, and the dwelleris of Jerusalem, and Josaphat bifor hem, in to Jerusalem with greet gladnesse; for the Lord God hadde youe to hem ioye of her enemyes.
28 Suka shiga Urushalima suka shiga haikalin Ubangiji da kiɗin molaye da sarewa da kuma garayu.
And thei entriden in to Jerusalem with sawtrees, and harpis, and trumpis, in to the hows of the Lord.
29 Tsoron Allah ya kama dukan mulkokin ƙasashe sa’ad da suka ji yadda Ubangiji ya yi yaƙi a kan abokan gāban Isra’ila.
Forsothe the drede of the Lord felde on alle the rewmes of londis, whanne thei hadden herd, that the Lord hadde fouyte ayens the enemies of Israel.
30 Mulkin Yehoshafat kuwa ya zauna lafiya, gama Allahnsa ya ba shi hutu a kowane gefe.
And the rewme of Josaphat restide; and the Lord yaf `pees to hym `bi cumpas.
31 Ta haka Yehoshafat ya yi mulki a bisa Yahuda. Yana da shekara talatin da biyar sa’ad da ya zama sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ashirin da biyar. Sunan mahaifiyarsa Azuba ce,’yar Shilhi.
Therfor Josaphat regnede on Juda; and he was of fyue and thritti yeer, whanne he bigan to regne; sotheli he regnede fyue and twenti yeer in Jerusalem; and the name of his modir was Azuba, the douytir of Selathi.
32 Ya yi tafiya a hanyoyin mahaifinsa Asa bai kuwa kauce daga gare su ba; ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji.
And he yede in the weie of Asa his fadir, and bowide not fro it, and he dide what euer thingis weren plesaunt bifor the Lord.
33 Duk da haka ba a kawar da masujadai kan tudu ba, domin har yanzu mutanen ba su tsayar da zukatansu ga Allahn kakanninsu ba.
Netheles he dide not awei hiy thingis; yit the puple hadde not dressid her herte to the Lord God of her fadris.
34 Sauran ayyukan mulkin Yehoshafat, daga farko zuwa ƙarshe, an rubuta su a tarihin Yehu ɗan Hanani, waɗanda aka rubuta a littafin sarakunan Isra’ila.
Forsothe the residue of the formere and the laste dedis of Josaphat ben writun in the book of Hieu, the sone of Anany, which he ordeynede in the book of kyngis of Israel.
35 Daga baya, Yehoshafat sarkin Yahuda ya haɗa kai da Ahaziya sarkin Isra’ila, wanda yake da laifin mugunta.
After these thingis Josaphat, kyng of Juda, made frendschipis with Ocozie, kyng of Israel, whose werkis weren ful yuele;
36 Ya yarda da shi su gina jiragen ruwan kasuwanci. Bayan aka gina waɗannan a Eziyon Geber,
and he was parcener that thei maden schippis, that schulden go in to Tharsis; and thei maden o schip in to Asiongaber.
37 Eliyezer ɗan Dodabahu na Maresha ya yi annabci a kan Yehoshafat cewa, “Domin ka haɗa kai da Ahaziya, Ubangiji zai hallaka abin da ka yi.” Jiragen ruwan kuwa suka farfashe, ba a kuwa iya sa su je kasuwanci ba.
Sotheli Eliezer, sone of Dodan, of Maresa, profesiede to Josaphat, and seide, For thou haddist boond of pees with Ocozie, the Lord smoot thi werkis; and the schippis ben brokun, and myyten not go in to Tharsis.

< 2 Tarihi 20 >