< 2 Tarihi 2 >
1 Solomon ya ba da umarni don a gina haikali domin sunan Ubangiji da kuma fada wa kansa.
Or Salomon ordonna de bâtir une maison au nom de l'Éternel, et pour lui une maison royale.
2 Ya ɗebi mutane dubu saba’in su zama’yan ɗauko, mutane dubu tamanin su zama masu fasa dutse a tuddai, da kuma mutane dubu uku da ɗari shida su zama masu lura da su.
Et Salomon compta soixante et dix mille hommes pour porter les fardeaux, et quatre-vingt mille pour tailler les pierres dans la montagne, et trois mille six cents préposés sur eux.
3 Solomon ya aika wannan saƙo ga Hiram sarkin Taya. “Ka aika mini gumaguman al’ul kamar yadda ka yi wa mahaifina Dawuda sa’ad da ka aika masa al’ul don yă gina fada yă zauna a ciki.
Puis Salomon envoya vers Huram, roi de Tyr, pour lui dire: Fais pour moi comme tu as fait pour David, mon père, à qui tu as envoyé des cèdres, pour se bâtir une maison afin d'y habiter.
4 Yanzu ina shirin ginin haikali domin Sunan Ubangiji Allahna, in kuma keɓe shi gare shi don ƙona turare mai ƙanshi a gabansa, don kuma ajiyar burodi mai tsarki kullum, da kuma don miƙa hadayun ƙonawa kowace safiya, kowace yamma, da a Asabbatai da Sababbin Wata, da kuma a ƙayyadaddun bukukkuwan Ubangiji Allahnmu. Wannan dawwammamiyar farilla ce don Isra’ila.
Voici, je vais bâtir une maison au nom de l'Éternel mon Dieu, pour la lui consacrer, pour faire fumer devant lui le parfum des aromates, pour présenter continuellement devant lui les pains de proposition, et pour offrir les holocaustes du matin et du soir, des sabbats, des nouvelles lunes, et des fêtes de l'Éternel, notre Dieu, ce qui est un devoir pour Israël à perpétuité.
5 “Haikalin da zan gina zai zama mai girma, domin Allahnmu ya fi dukan sauran alloli girma.
La maison que je vais bâtir sera grande; car notre Dieu est plus grand que tous les dieux.
6 Amma wa zai iya gina haikali dominsa, shi wanda sammai, har ma da sama sammai, ba za su iya riƙe shi ba? To, wane ne ni da zan gina haikali dominsa, in ba dai wurin ƙona hadayu a gabansa ba?
Mais qui aurait le pouvoir de lui bâtir une maison, puisque les cieux et les cieux des cieux ne sauraient le contenir? Et qui suis-je pour lui bâtir une maison, si ce n'est pour faire fumer des parfums devant sa face?
7 “Saboda haka sai ka aiko mini da mutum wanda ya gwanince a aiki da azurfa, tagulla, baƙin ƙarfe, da kuma shunayya, da garura, da shuɗɗan zare, da wanda kuma ya gwanince da aikin sassaƙa, domin yă yi aiki tare da gwanayen mutane da nake da su a Yahuda da Urushalima, waɗanda mahaifina Dawuda ya tanada.
Maintenant envoie-moi un homme habile à travailler en or, en argent, en airain et en fer, en écarlate, en cramoisi et en pourpre, sachant sculpter des sculptures, pour travailler avec les hommes habiles que j'ai avec moi en Juda et à Jérusalem, et que David, mon père, a préparés.
8 “Ka kuma aika mini al’ul, fir da gumaguman algum daga Lebanon, gama na san cewa mutanenka sun gwanince a yakan katakai a can. Mutanena kuwa za su yi aiki tare da naka
Envoie-moi aussi du Liban du bois de cèdre, de cyprès et de santal; car je sais que tes serviteurs savent couper le bois du Liban. Voici, mes serviteurs seront avec les tiens.
9 don su tanada mini katakai da yawa, domin haikalin da zan gina dole yă zama mai girma da kuma ƙasaitacce.
Qu'on me prépare du bois en grande quantité; car la maison que je vais bâtir sera grande et magnifique.
10 Zan ba wa bayinka masu yankan katakai waɗanda suka yanka katako, garwa niƙaƙƙen alkama dubu ashirin, garwan sha’ir dubu ashirin da randunan ruwan inabi dubu ashirin da kuma randunan man zaitun dubu ashirin.”
Et je donnerai à tes serviteurs qui couperont, qui abattront les bois, vingt mille cores de froment foulé, vingt mille cores d'orge, vingt mille baths de vin, et vingt mille baths d'huile.
11 Hiram sarkin Taya ya amsa ta wurin rubuta wasiƙa zuwa ga Solomon. “Domin Ubangiji yana ƙaunar mutanensa, ya naɗa ka sarkinsu.”
Huram, roi de Tyr, répondit, dans un écrit qu'il envoya à Salomon: C'est parce que l'Éternel aime son peuple qu'il t'a établi roi sur eux.
12 Hiram ya ƙara da cewa, “Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya yi sama da ƙasa! Ya ba Sarki Dawuda ɗa mai hikima, cike da wayo da kuma sani, wanda zai gina haikali domin Ubangiji da kuma fada wa kansa.
Et Huram dit: Béni soit l'Éternel, le Dieu d'Israël, qui a fait les cieux et la terre, de ce qu'il a donné au roi David un fils sage, prudent et intelligent, qui va bâtir une maison à l'Éternel, et une maison royale pour lui!
13 “Zan aika maka Huram-Abi, wani gwani wanda ya iya aiki, kuma mai hikima,
Je t'envoie donc un homme habile et intelligent, Huram-Abi,
14 wanda mahaifiyarsa ta fito daga Dan, mahaifinsa kuma daga Taya. An horar da shi a aikin zinariya, azurfa, tagulla, baƙin ƙarfe, dutse, itace, da kuma shuɗi, shunayya, garura, da lilin mai kyau. Ya gogu a kowane irin zāne-zāne, zai kuma iya yin kowane zānen da aka ba shi. Zai yi aiki tare da masu sana’arka, da kuma tare da waɗanda ranka yă daɗe, Dawuda mahaifinka ya tanada.
Fils d'une femme d'entre les filles de Dan, et d'un père tyrien. Il sait travailler en or, en argent, en airain et en fer, en pierres et en bois, en écarlate, en pourpre, en fin lin et en cramoisi; il sait sculpter toutes sortes de sculptures et imaginer toutes sortes d'objets d'art qu'on lui donne à faire. Il travaillera avec tes hommes habiles et avec les hommes habiles de mon seigneur David, ton père.
15 “Yanzu fa, bari ranka yă daɗe, yă aiko wa bayinsa alkama da sha’ir da kuma man zaitun da ruwan inabin da ka alkawarta,
Et maintenant, que mon seigneur envoie à ses serviteurs le froment, l'orge, l'huile et le vin qu'il a dit.
16 za mu kuwa yanka dukan gumagumai daga Lebanon da kake bukata za mu kuwa yi fitonsu ta teku, su gangara zuwa Yaffa. Za ka iya kwashe su daga can ka haura zuwa Urushalima.”
Et nous couperons des bois du Liban autant qu'il t'en faudra, et nous te les amènerons en radeaux, par mer, jusqu'à Japho, et tu les feras monter à Jérusalem.
17 Solomon ya ƙidaya dukan baƙin da suke cikin Isra’ila, bayan ƙidayan da mahaifinsa Dawuda ya yi; aka kuma tarar sun kai 153,600.
Alors Salomon compta tous les étrangers qui étaient au pays d'Israël, après le dénombrement que David, son père, en avait fait; on en trouva cent cinquante-trois mille six cents.
18 Ya sa 70,000 a cikinsu su zama’yan ɗauko, 80,000 kuma su zama masu fasan dutse a tuddai, sa’an nan 3,600 su zama shugabanni masu lura da aiki.
Et il en établit soixante et dix mille qui portaient des fardeaux, quatre-vingt mille qui taillaient les pierres dans la montagne, et trois mille six cents préposés pour faire travailler le peuple.