< 2 Tarihi 2 >
1 Solomon ya ba da umarni don a gina haikali domin sunan Ubangiji da kuma fada wa kansa.
And Solomon ordered to build a house for the name of the Lord, and a house for his royal residence.
2 Ya ɗebi mutane dubu saba’in su zama’yan ɗauko, mutane dubu tamanin su zama masu fasa dutse a tuddai, da kuma mutane dubu uku da ɗari shida su zama masu lura da su.
And Solomon numbered seventy thousand men to bear burdens, and eighty thousand stonecutters in the mountain, and as superintendents over them three thousand and six hundred.
3 Solomon ya aika wannan saƙo ga Hiram sarkin Taya. “Ka aika mini gumaguman al’ul kamar yadda ka yi wa mahaifina Dawuda sa’ad da ka aika masa al’ul don yă gina fada yă zauna a ciki.
And Solomon sent to Churam the king of Tyre, saying, As thou hast dealt with David my father, and didst send him cedars to build him a house to dwell therein, [even so deal with me].
4 Yanzu ina shirin ginin haikali domin Sunan Ubangiji Allahna, in kuma keɓe shi gare shi don ƙona turare mai ƙanshi a gabansa, don kuma ajiyar burodi mai tsarki kullum, da kuma don miƙa hadayun ƙonawa kowace safiya, kowace yamma, da a Asabbatai da Sababbin Wata, da kuma a ƙayyadaddun bukukkuwan Ubangiji Allahnmu. Wannan dawwammamiyar farilla ce don Isra’ila.
Behold, I am building a house to the name of the Lord my God, to sanctify it to him, to burn before him incense of spices, and for the continual rows of show-bread, and for the burnt-offerings at morning and evening, on the sabbaths, and on the new-moons, and on the stated festivals of the Lord our God: this being for ever obligatory on Israel.
5 “Haikalin da zan gina zai zama mai girma, domin Allahnmu ya fi dukan sauran alloli girma.
And the house which I am building is great; for greater is our God than all the gods.
6 Amma wa zai iya gina haikali dominsa, shi wanda sammai, har ma da sama sammai, ba za su iya riƙe shi ba? To, wane ne ni da zan gina haikali dominsa, in ba dai wurin ƙona hadayu a gabansa ba?
But who possesseth the power to build him a house? for the heavens and the heavens of heavens cannot contain him: and who am I then, that I should build him a house, save only to burn incense before him?
7 “Saboda haka sai ka aiko mini da mutum wanda ya gwanince a aiki da azurfa, tagulla, baƙin ƙarfe, da kuma shunayya, da garura, da shuɗɗan zare, da wanda kuma ya gwanince da aikin sassaƙa, domin yă yi aiki tare da gwanayen mutane da nake da su a Yahuda da Urushalima, waɗanda mahaifina Dawuda ya tanada.
And now send me a skilful man to work in gold, and in silver and in copper, and in iron, and in purple, and crimson, and blue, and that understandeth how to engrave with the skilful men that are with me in Judah and in Jerusalem whom David my father hath provided.
8 “Ka kuma aika mini al’ul, fir da gumaguman algum daga Lebanon, gama na san cewa mutanenka sun gwanince a yakan katakai a can. Mutanena kuwa za su yi aiki tare da naka
Send me also cedar-trees, fir-trees, and sandal-wood, from the Lebanon; for I know well that thy servants have the skill to cut the trees of Lebanon: and, behold, my servants shall be with thy servants,
9 don su tanada mini katakai da yawa, domin haikalin da zan gina dole yă zama mai girma da kuma ƙasaitacce.
Even to prepare for me timber in abundance; for the house which I am building is to be wonderfully great.
10 Zan ba wa bayinka masu yankan katakai waɗanda suka yanka katako, garwa niƙaƙƙen alkama dubu ashirin, garwan sha’ir dubu ashirin da randunan ruwan inabi dubu ashirin da kuma randunan man zaitun dubu ashirin.”
And, behold, for the hewers that cut the timber will I give unto thy servants twenty thousand cors of threshed wheat, and twenty thousand cors of barley, and twenty thousand baths of wine, and twenty thousand baths of oil.
11 Hiram sarkin Taya ya amsa ta wurin rubuta wasiƙa zuwa ga Solomon. “Domin Ubangiji yana ƙaunar mutanensa, ya naɗa ka sarkinsu.”
Then answered Churam the king of Tyre in writing, and he sent it to Solomon, Out of the love of the Lord for his people hath he set thee as king over them.
12 Hiram ya ƙara da cewa, “Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya yi sama da ƙasa! Ya ba Sarki Dawuda ɗa mai hikima, cike da wayo da kuma sani, wanda zai gina haikali domin Ubangiji da kuma fada wa kansa.
And Churam said, Blessed be the Lord the God of Israel, that hath made the heavens and the earth, who hath given to king David a wise son, endowed with intelligence and understanding, who is to build a house unto the Lord, and a house for royal residence.
13 “Zan aika maka Huram-Abi, wani gwani wanda ya iya aiki, kuma mai hikima,
And now have I sent a skilful man, endowed with understanding, namely, Churam-Abi,
14 wanda mahaifiyarsa ta fito daga Dan, mahaifinsa kuma daga Taya. An horar da shi a aikin zinariya, azurfa, tagulla, baƙin ƙarfe, dutse, itace, da kuma shuɗi, shunayya, garura, da lilin mai kyau. Ya gogu a kowane irin zāne-zāne, zai kuma iya yin kowane zānen da aka ba shi. Zai yi aiki tare da masu sana’arka, da kuma tare da waɗanda ranka yă daɗe, Dawuda mahaifinka ya tanada.
The son of a woman from the daughters of Dan, while his father was a man of Tyre, skilful to work in gold, and in silver, in copper, in iron, in stone, and in wood, in purple, in blue, and in fine linen, and in crimson; also to execute any manner of engraving, and to devise every kind of work of art which may be given to him, together with thy skilful men, and skilful men of my lord David thy father.
15 “Yanzu fa, bari ranka yă daɗe, yă aiko wa bayinsa alkama da sha’ir da kuma man zaitun da ruwan inabin da ka alkawarta,
And now the wheat, and the barley, the oil, and the wine, of which my lord hath spoken, let him send unto his servants:
16 za mu kuwa yanka dukan gumagumai daga Lebanon da kake bukata za mu kuwa yi fitonsu ta teku, su gangara zuwa Yaffa. Za ka iya kwashe su daga can ka haura zuwa Urushalima.”
And we will truly cut down trees out of the Lebanon, as much as thou mayest need; and we will bring them to thee in boats by sea to Joppa; and thou shalt carry them up to Jerusalem.
17 Solomon ya ƙidaya dukan baƙin da suke cikin Isra’ila, bayan ƙidayan da mahaifinsa Dawuda ya yi; aka kuma tarar sun kai 153,600.
And Solomon numbered all the strange men that were in the land of Israel, after the numbering wherewith David his father had numbered them; and they were found to be one hundred and fifty thousand and three thousand and six hundred.
18 Ya sa 70,000 a cikinsu su zama’yan ɗauko, 80,000 kuma su zama masu fasan dutse a tuddai, sa’an nan 3,600 su zama shugabanni masu lura da aiki.
And he made of them seventy thousand bearers of burdens, and eighty thousand stonecutters in the mountain, and three thousand and six hundred superintendents to set the people to work.