< 2 Tarihi 19 >

1 Sa’ad da Yehoshafat sarkin Yahuda ya dawo zuwa fadansa a Urushalima lafiya,
Men Josaphat, Juda Konung, kom hem igen med frid till Jerusalem.
2 Yehu mai duba, ɗan Hanani, ya fita don yă tarye shi, ya kuma ce wa sarki, “Ya yi kyau ke nan da ka taimaki mugu ka kuma ƙaunaci waɗanda suke ƙin Ubangiji? Da yake ka yi haka fushin Ubangiji yana a kanka
Och gick ut emot honom. Jehu, Hanani son, Siaren, och sade till Konung Josaphat: Skulle du så hjelpa den ogudaktiga, och älska dem som Herran hata? Och fördenskull är öfver dig Herrans vrede.
3 Duk da haka an sami wani abin kirki a wurinka, gama ka kawar da ginshiƙan Ashera a ƙasar, ka kuma sa zuciyarka a kan neman Allah.”
Så är dock likväl något godt funnet i dig, att du hafver borthäfvit de lundar utu landena, och hafver skickat ditt hjerta till att söka Gud.
4 Yehoshafat ya zauna a Urushalima, ya kuma fita yana shiga cikin mutane daga Beyersheba zuwa ƙasar tudun Efraim ya kuma juyar da su ga Ubangiji Allah na kakanninsu.
Alltså blef Josaphat i Jerusalem. Och han drog åter ut ibland folket, allt ifrå BerSeba, och in uppå Ephraims berg, och igenkallade dem till Herran deras fäders Gud.
5 Ya naɗa alƙalai a kowanne daga cikin biranen katanga na Yahuda a ƙasar.
Och han beställde domare i landena uti alla Juda fasta städer, ju några uti hvar stad;
6 Ya faɗa musu, “Ku lura da abin da kuke yi, gama shari’ar da kuke yi ba ta mutum ba ce, amma ta Ubangiji ce, yana tare da ku sa’ad da kuke yanke shari’a.
Och sade till domarena: Ser till hvad I gören; förty I hållen icke menniskodom, utan Herrans, och han är med eder i domen.
7 Yanzu fa ku ji tsoron Ubangiji. Ku yi hankali a kan abin da kuke yi, gama Ubangiji Allahnmu ba ya sonkai ko nuna wariya ko cin hanci.”
Derföre, låter Herrans fruktan vara när eder. Tager eder vara, och görer så; ty när Herranom vårom Gud är ingen orätt, eller anseende till personer, ej heller tager han gåfvor.
8 A Urushalima kuma, Yehoshafat ya naɗa waɗansu Lawiyawa, firistoci da kawunan iyalan Isra’ilawa don su tabbatar da an bi dokar Ubangiji, su kuma sasanta tsakanin mutane. A Urushalima za su zauna.
Ock satte Josaphat i Jerusalem utaf Leviterna och Presterna, och utaf de öfversta fäderna i Israel, öfver Herrans dom och saker, och lät dem bo i Jerusalem;
9 Ya ba su waɗannan umarnai, “Ku yi aikinku da aminci da tsoron Ubangiji da dukan zuciyarku.
Och böd dem och sade: Görer alltså uti Herrans fruktan, med tro och rätto hjerta.
10 Cikin kowane batun da ya zo gabanku daga’yan’uwanku waɗanda suke zama a birane, ko batun na kisa ne ko kuwa waɗansu batuttuwan da suka shafi doka, umarnai, ƙa’idodi ko farillai, dole ku ja musu kunne kada su yi wa Ubangiji zunubi; in ba haka ba fushinsa zai sauko a kanku da’yan’uwanku. Ku yi wannan, ta haka ba za ku kuwa yi zunubi ba.
Uti alla de saker, som komma till eder ifrån edra bröder, som bo i sina städer, emellan blod och blod, emellan lag och bud, emellan seder och rätter, skolen I undervisa dem, att de icke förbryta sig emot Herran, och en vrede må komma öfver eder, och edra bröder; görer alltså, så varden I icke brottslige.
11 “Amariya, babban firist, shi ne zai shugabance ku a kan dukan al’amuran da suke na wajen Ubangiji, Zebadiya ɗan Ishmayel kuwa, shugabanku a kan dukan al’amuran da suka shafi sarki, Lawiyawa kuma za su zama a matsayin manya a gabanku. Ku yi abubuwa da ƙarfin hali, bari kuma Ubangiji yă kasance tare da masu yin gaskiya.”
Si, Amaria Presten är öfverste öfver eder i alla Herrans saker; så är Sebadia, Ismaels son, Förste i Juda hus, i alla Konungssaker; så hafven I ämbetsmän Leviterna för eder. Varer tröste, och görer så, och Herren varder blifvandes med dem goda.

< 2 Tarihi 19 >