< 2 Tarihi 19 >

1 Sa’ad da Yehoshafat sarkin Yahuda ya dawo zuwa fadansa a Urushalima lafiya,
Josaphat, roi de Juda, revint sain et sauf dans sa maison, à Jérusalem.
2 Yehu mai duba, ɗan Hanani, ya fita don yă tarye shi, ya kuma ce wa sarki, “Ya yi kyau ke nan da ka taimaki mugu ka kuma ƙaunaci waɗanda suke ƙin Ubangiji? Da yake ka yi haka fushin Ubangiji yana a kanka
Mais Jéhu, fils de Hanani, le Voyant, sortit au-devant du roi Josaphat, et lui dit: Est-ce le méchant qu'il faut aider? Sont-ce les ennemis de l'Éternel que tu aimes? A cause de cela, l'Éternel est irrité contre toi.
3 Duk da haka an sami wani abin kirki a wurinka, gama ka kawar da ginshiƙan Ashera a ƙasar, ka kuma sa zuciyarka a kan neman Allah.”
Mais il s'est trouvé de bonnes choses en toi, car tu as ôté du pays les emblèmes d'Ashéra, et tu as appliqué ton cœur à rechercher Dieu.
4 Yehoshafat ya zauna a Urushalima, ya kuma fita yana shiga cikin mutane daga Beyersheba zuwa ƙasar tudun Efraim ya kuma juyar da su ga Ubangiji Allah na kakanninsu.
Et Josaphat habita à Jérusalem. Puis, de nouveau, il sortit parmi le peuple, depuis Béer-Shéba jusqu'à la montagne d'Éphraïm, et il les ramena à l'Éternel, le Dieu de leurs pères.
5 Ya naɗa alƙalai a kowanne daga cikin biranen katanga na Yahuda a ƙasar.
Il établit aussi des juges dans le pays, dans toutes les villes fortes de Juda, dans chaque ville.
6 Ya faɗa musu, “Ku lura da abin da kuke yi, gama shari’ar da kuke yi ba ta mutum ba ce, amma ta Ubangiji ce, yana tare da ku sa’ad da kuke yanke shari’a.
Et il dit aux juges: Regardez à ce que vous ferez; car ce n'est pas pour l'homme que vous jugerez, mais pour l'Éternel, qui sera avec vous quand vous jugerez.
7 Yanzu fa ku ji tsoron Ubangiji. Ku yi hankali a kan abin da kuke yi, gama Ubangiji Allahnmu ba ya sonkai ko nuna wariya ko cin hanci.”
Maintenant, que la crainte de l'Éternel soit sur vous; prenez garde à ce que vous ferez; car il n'y a point d'iniquité dans l'Éternel notre Dieu, ni d'acception de personnes, ni d'acceptation de présents.
8 A Urushalima kuma, Yehoshafat ya naɗa waɗansu Lawiyawa, firistoci da kawunan iyalan Isra’ilawa don su tabbatar da an bi dokar Ubangiji, su kuma sasanta tsakanin mutane. A Urushalima za su zauna.
Josaphat établit aussi à Jérusalem des Lévites, et des sacrificateurs, et des chefs des pères d'Israël, pour le jugement de l'Éternel, et pour les contestations. Et on revint à Jérusalem.
9 Ya ba su waɗannan umarnai, “Ku yi aikinku da aminci da tsoron Ubangiji da dukan zuciyarku.
Et il leur donna des ordres, en disant: Vous agirez ainsi dans la crainte de l'Éternel, avec fidélité et avec intégrité de cœur.
10 Cikin kowane batun da ya zo gabanku daga’yan’uwanku waɗanda suke zama a birane, ko batun na kisa ne ko kuwa waɗansu batuttuwan da suka shafi doka, umarnai, ƙa’idodi ko farillai, dole ku ja musu kunne kada su yi wa Ubangiji zunubi; in ba haka ba fushinsa zai sauko a kanku da’yan’uwanku. Ku yi wannan, ta haka ba za ku kuwa yi zunubi ba.
Et pour les différends qui viendront devant vous, de la part de vos frères qui habitent dans leurs villes, qu'il s'agisse d'un meurtre, d'une loi, d'un commandement, de statuts ou d'ordonnances, vous les éclairerez, afin qu'ils ne se rendent pas coupables envers l'Éternel, et qu'il n'y ait point de courroux sur vous et sur vos frères. Vous agirez ainsi, et vous ne serez point trouvés coupables.
11 “Amariya, babban firist, shi ne zai shugabance ku a kan dukan al’amuran da suke na wajen Ubangiji, Zebadiya ɗan Ishmayel kuwa, shugabanku a kan dukan al’amuran da suka shafi sarki, Lawiyawa kuma za su zama a matsayin manya a gabanku. Ku yi abubuwa da ƙarfin hali, bari kuma Ubangiji yă kasance tare da masu yin gaskiya.”
Et voici, Amaria, le principal sacrificateur, est préposé sur vous pour toutes les affaires de l'Éternel, et Zébadia, fils d'Ismaël, prince de la maison de Juda, pour toutes les affaires du roi; et pour secrétaires vous avez devant vous les Lévites. Fortifiez-vous et agissez; et que l'Éternel soit avec l'homme de bien!

< 2 Tarihi 19 >