< 2 Tarihi 19 >
1 Sa’ad da Yehoshafat sarkin Yahuda ya dawo zuwa fadansa a Urushalima lafiya,
Et Josaphat, roi de Juda, revint en son palais à Jérusalem.
2 Yehu mai duba, ɗan Hanani, ya fita don yă tarye shi, ya kuma ce wa sarki, “Ya yi kyau ke nan da ka taimaki mugu ka kuma ƙaunaci waɗanda suke ƙin Ubangiji? Da yake ka yi haka fushin Ubangiji yana a kanka
Et le prophète Jéhu, fils d'Anani, sortit à sa rencontre, et il lui dit Roi Josaphat, n'as-tu pas porté secours à un impie, et donné ton amitié à un ennemi du Seigneur? A cause de cela, la colère du Seigneur a été excitée contre toi.
3 Duk da haka an sami wani abin kirki a wurinka, gama ka kawar da ginshiƙan Ashera a ƙasar, ka kuma sa zuciyarka a kan neman Allah.”
Cependant, il s'est trouvé du bon en toi; car tu as détruit les bois sacrés en la terre de Juda, et, d'un cœur droit, tu as cherché Dieu.
4 Yehoshafat ya zauna a Urushalima, ya kuma fita yana shiga cikin mutane daga Beyersheba zuwa ƙasar tudun Efraim ya kuma juyar da su ga Ubangiji Allah na kakanninsu.
Et Josaphat résida en Jérusalem; il en sortit encore une fois pour visiter le peuple depuis Bersabée jusqu'aux montagnes d'Ephraïm, et il les ramena au Seigneur Dieu de leurs pères.
5 Ya naɗa alƙalai a kowanne daga cikin biranen katanga na Yahuda a ƙasar.
Et il institua des juges dans toutes les places fortes de Juda: un par ville.
6 Ya faɗa musu, “Ku lura da abin da kuke yi, gama shari’ar da kuke yi ba ta mutum ba ce, amma ta Ubangiji ce, yana tare da ku sa’ad da kuke yanke shari’a.
Et il dit aux juges: Soyez attentifs à ce que vous faites; car vous ne jugez pas pour l'homme, mais pour le Seigneur, et les paroles du jugement sont avec vous.
7 Yanzu fa ku ji tsoron Ubangiji. Ku yi hankali a kan abin da kuke yi, gama Ubangiji Allahnmu ba ya sonkai ko nuna wariya ko cin hanci.”
Que la crainte du Seigneur soit donc en vous; veillez et agissez; car, avec le Seigneur notre Dieu, il n'est point d'iniquité; il n'y a point à considérer la personne, ni à recevoir des présents.
8 A Urushalima kuma, Yehoshafat ya naɗa waɗansu Lawiyawa, firistoci da kawunan iyalan Isra’ilawa don su tabbatar da an bi dokar Ubangiji, su kuma sasanta tsakanin mutane. A Urushalima za su zauna.
Et Josaphat institua en Jérusalem des prêtres, des lévites et des chefs de familles d'Israël, pour juger les choses du Seigneur et les habitants de la ville.
9 Ya ba su waɗannan umarnai, “Ku yi aikinku da aminci da tsoron Ubangiji da dukan zuciyarku.
Et il leur donna ses ordres, disant: Vous ferez votre devoir avec la crainte de Dieu, en la plénitude et en la sincérité de votre cœur.
10 Cikin kowane batun da ya zo gabanku daga’yan’uwanku waɗanda suke zama a birane, ko batun na kisa ne ko kuwa waɗansu batuttuwan da suka shafi doka, umarnai, ƙa’idodi ko farillai, dole ku ja musu kunne kada su yi wa Ubangiji zunubi; in ba haka ba fushinsa zai sauko a kanku da’yan’uwanku. Ku yi wannan, ta haka ba za ku kuwa yi zunubi ba.
Quels que soient ceux de vos frères qui, de leurs villes, viendront à vous en justice, soit pour une décision entre le sang et le sang, soit pour une application des commandements et des préceptes, déterminez bien pour eux le droit et la sentence; et ils ne pècheront pas envers le Seigneur, et il n'y aura point de colère, ni contre vos frères, ni contre vous. Faites ainsi, et vous ne pècherez pas.
11 “Amariya, babban firist, shi ne zai shugabance ku a kan dukan al’amuran da suke na wajen Ubangiji, Zebadiya ɗan Ishmayel kuwa, shugabanku a kan dukan al’amuran da suka shafi sarki, Lawiyawa kuma za su zama a matsayin manya a gabanku. Ku yi abubuwa da ƙarfin hali, bari kuma Ubangiji yă kasance tare da masu yin gaskiya.”
Et Ananias le prêtre sera votre chef en ce qui concernera le Seigneur; Zabdias, fils d'Ismaël, prince de la maison de Juda, sera votre chef en ce qui concernera le roi, et vous aurez avec vous des scribes et des lévites; fortifiez-vous, et faites, et le Seigneur sera avec les bons.