< 2 Tarihi 19 >

1 Sa’ad da Yehoshafat sarkin Yahuda ya dawo zuwa fadansa a Urushalima lafiya,
Josaphat, roi de Juda, revint en paix dans sa maison à Jérusalem.
2 Yehu mai duba, ɗan Hanani, ya fita don yă tarye shi, ya kuma ce wa sarki, “Ya yi kyau ke nan da ka taimaki mugu ka kuma ƙaunaci waɗanda suke ƙin Ubangiji? Da yake ka yi haka fushin Ubangiji yana a kanka
Jéhu, fils de Hanani, le voyant, sortit au-devant de lui, et il dit au roi Josaphat: « Doit-on secourir le méchant, et aimes-tu ceux qui haïssent Yahweh? A cause de cela, est venue sur toi la colère, de par Yahweh.
3 Duk da haka an sami wani abin kirki a wurinka, gama ka kawar da ginshiƙan Ashera a ƙasar, ka kuma sa zuciyarka a kan neman Allah.”
Pourtant, il s’est trouvé quelque bien en toi, car tu as fait disparaître du pays les aschérahs, et tu as appliqué ton cœur à chercher Dieu. »
4 Yehoshafat ya zauna a Urushalima, ya kuma fita yana shiga cikin mutane daga Beyersheba zuwa ƙasar tudun Efraim ya kuma juyar da su ga Ubangiji Allah na kakanninsu.
Josaphat résida à Jérusalem; et de nouveau il visita le peuple depuis Bersabée jusqu’à la montagne d’Ephraïm, et il les ramena à Yahweh, le Dieu de leurs pères.
5 Ya naɗa alƙalai a kowanne daga cikin biranen katanga na Yahuda a ƙasar.
Il établit des juges dans le pays, dans toutes les villes fortes de Juda, pour chaque ville.
6 Ya faɗa musu, “Ku lura da abin da kuke yi, gama shari’ar da kuke yi ba ta mutum ba ce, amma ta Ubangiji ce, yana tare da ku sa’ad da kuke yanke shari’a.
Et il dit aux juges: « Prenez garde. à ce que vous ferez, car ce n’est pas pour les hommes que vous rendrez la justice, mais c’est pour Yahweh; il sera avec vous quand vous rendrez la justice.
7 Yanzu fa ku ji tsoron Ubangiji. Ku yi hankali a kan abin da kuke yi, gama Ubangiji Allahnmu ba ya sonkai ko nuna wariya ko cin hanci.”
Et moi maintenant, que la crainte de Yahweh soit sur vous; veillez sur vos actes, car il n’y a avec Yahweh, notre Dieu, ni iniquité, ni acception des personnes, ni acceptation des présents. »
8 A Urushalima kuma, Yehoshafat ya naɗa waɗansu Lawiyawa, firistoci da kawunan iyalan Isra’ilawa don su tabbatar da an bi dokar Ubangiji, su kuma sasanta tsakanin mutane. A Urushalima za su zauna.
A Jérusalem aussi, quand ils revinrent dans cette ville, Josaphat établit, pour les jugements de Yahweh et pour les contestations, des lévites, des prêtres et des chefs de maisons d’Israël.
9 Ya ba su waɗannan umarnai, “Ku yi aikinku da aminci da tsoron Ubangiji da dukan zuciyarku.
Et il leur donna des ordres en ces termes: « Vous agirez ainsi en craignant Yahweh, dans la fidélité et l’intégrité du cœur.
10 Cikin kowane batun da ya zo gabanku daga’yan’uwanku waɗanda suke zama a birane, ko batun na kisa ne ko kuwa waɗansu batuttuwan da suka shafi doka, umarnai, ƙa’idodi ko farillai, dole ku ja musu kunne kada su yi wa Ubangiji zunubi; in ba haka ba fushinsa zai sauko a kanku da’yan’uwanku. Ku yi wannan, ta haka ba za ku kuwa yi zunubi ba.
Dans toute cause qui viendra devant vous de la part de vos frères établis dans leurs villes, quand il s’agira de distinguer entre meurtre et meurtre, entre loi, commandement, précepte ou ordonnance, vous les éclairerez, afin qu’ils ne se rendent pas coupables envers Yahweh, et que sa colère ne vienne pas sur vous et sur vos frères. Vous agirez ainsi, et vous ne serez pas coupables.
11 “Amariya, babban firist, shi ne zai shugabance ku a kan dukan al’amuran da suke na wajen Ubangiji, Zebadiya ɗan Ishmayel kuwa, shugabanku a kan dukan al’amuran da suka shafi sarki, Lawiyawa kuma za su zama a matsayin manya a gabanku. Ku yi abubuwa da ƙarfin hali, bari kuma Ubangiji yă kasance tare da masu yin gaskiya.”
Et voici que vous aurez à votre tête Amarias, le grand prêtre, pour toutes les affaires de Yahweh, et Zabadias, fils d’Ismaël, le prince de la maison de Juda, pour toutes les affaires du roi, et vous aurez devant vous les lévites comme officiers. Courage et à l’œuvre! et que Yahweh soit avec vous! »

< 2 Tarihi 19 >