< 2 Tarihi 19 >

1 Sa’ad da Yehoshafat sarkin Yahuda ya dawo zuwa fadansa a Urushalima lafiya,
Forsothe Josaphat, kyng of Juda, turnede ayen pesibli in to his hows in to Jerusalem.
2 Yehu mai duba, ɗan Hanani, ya fita don yă tarye shi, ya kuma ce wa sarki, “Ya yi kyau ke nan da ka taimaki mugu ka kuma ƙaunaci waɗanda suke ƙin Ubangiji? Da yake ka yi haka fushin Ubangiji yana a kanka
Whom the profete Hieu, the sone of Ananye, mette, and seide to hym, Thou yyuest help to a wickid man, and thou art ioyned bi frendschip to hem that haten the Lord; and therfor sotheli thou deseruedist the wraththe of the Lord;
3 Duk da haka an sami wani abin kirki a wurinka, gama ka kawar da ginshiƙan Ashera a ƙasar, ka kuma sa zuciyarka a kan neman Allah.”
but good werkis ben foundyn in thee, for thou didist awey wodis fro the lond of Juda, and thou hast maad redi thin herte, for to seke the Lord God of thi fadris.
4 Yehoshafat ya zauna a Urushalima, ya kuma fita yana shiga cikin mutane daga Beyersheba zuwa ƙasar tudun Efraim ya kuma juyar da su ga Ubangiji Allah na kakanninsu.
Therfor Josaphat dwellide in Jerusalem; and eft he yede out to the puple fro Bersabee til to the hil of Effraym, and he clepide hem ayen to the Lord God of her fadris.
5 Ya naɗa alƙalai a kowanne daga cikin biranen katanga na Yahuda a ƙasar.
And he ordeynede iugis of the lond in alle the strengthid citees of Juda, bi ech place.
6 Ya faɗa musu, “Ku lura da abin da kuke yi, gama shari’ar da kuke yi ba ta mutum ba ce, amma ta Ubangiji ce, yana tare da ku sa’ad da kuke yanke shari’a.
And he comaundide to the iugis, and seide, Se ye, what ye doen; for ye vsen not the doom of man, but of the Lord; and what euere thing ye demen, schal turne `in to you;
7 Yanzu fa ku ji tsoron Ubangiji. Ku yi hankali a kan abin da kuke yi, gama Ubangiji Allahnmu ba ya sonkai ko nuna wariya ko cin hanci.”
the drede of the Lord be with you, and do ye alle thingis with diligence; for anentis `youre Lord God is no wickidnesse, nether takynge of persoones, nether coueitise of yiftis.
8 A Urushalima kuma, Yehoshafat ya naɗa waɗansu Lawiyawa, firistoci da kawunan iyalan Isra’ilawa don su tabbatar da an bi dokar Ubangiji, su kuma sasanta tsakanin mutane. A Urushalima za su zauna.
Also in Jerusalem Josaphat ordeynede dekenes, and preestis, and the princes of meynees of Israel, that thei schulden deme the doom and cause of the Lord to the dwellers of it.
9 Ya ba su waɗannan umarnai, “Ku yi aikinku da aminci da tsoron Ubangiji da dukan zuciyarku.
And he comaundide to hem, and seide, Thus ye schulen do in the drede of the Lord, feithfuli and in perfite herte.
10 Cikin kowane batun da ya zo gabanku daga’yan’uwanku waɗanda suke zama a birane, ko batun na kisa ne ko kuwa waɗansu batuttuwan da suka shafi doka, umarnai, ƙa’idodi ko farillai, dole ku ja musu kunne kada su yi wa Ubangiji zunubi; in ba haka ba fushinsa zai sauko a kanku da’yan’uwanku. Ku yi wannan, ta haka ba za ku kuwa yi zunubi ba.
Ech cause that cometh to you of youre britheren, that dwellen in her citees, bitwixe kynrede and kynrede, where euere is questioun of the lawe, of `the comaundement, of cerymonyes, `ether sacrifices, of iustifyingis, schewe ye to hem, that thei do not synne ayens the Lord, and that wraththe com not on you and on youre britheren. Therfor ye doynge thus schulen not do synne.
11 “Amariya, babban firist, shi ne zai shugabance ku a kan dukan al’amuran da suke na wajen Ubangiji, Zebadiya ɗan Ishmayel kuwa, shugabanku a kan dukan al’amuran da suka shafi sarki, Lawiyawa kuma za su zama a matsayin manya a gabanku. Ku yi abubuwa da ƙarfin hali, bari kuma Ubangiji yă kasance tare da masu yin gaskiya.”
Forsothe Amarie, youre preest and bischop, schal be souereyn in these thingis, that perteynen to God. Sotheli Zabadie, the sone of Ismael, which is duyk in the hows of Juda, schal be on tho werkis that perteynen to the office of the kyng, and ye han maistris dekenes bifor you; be ye coumfortid, and do ye diligentli, and the Lord schal be with you in goodis.

< 2 Tarihi 19 >