< 2 Tarihi 19 >
1 Sa’ad da Yehoshafat sarkin Yahuda ya dawo zuwa fadansa a Urushalima lafiya,
And Jehoshaphat the king of Judah returned to his house in peace to Jerusalem.
2 Yehu mai duba, ɗan Hanani, ya fita don yă tarye shi, ya kuma ce wa sarki, “Ya yi kyau ke nan da ka taimaki mugu ka kuma ƙaunaci waɗanda suke ƙin Ubangiji? Da yake ka yi haka fushin Ubangiji yana a kanka
And Jehu the son of Hanani the seer went out to meet him, and said to king Jehoshaphat, Should thou help the wicked, and love those who hate Jehovah? For this thing wrath is upon thee from before Jehovah.
3 Duk da haka an sami wani abin kirki a wurinka, gama ka kawar da ginshiƙan Ashera a ƙasar, ka kuma sa zuciyarka a kan neman Allah.”
Nevertheless there are good things found in thee, in that thou have put away the Asheroth out of the land, and have set thy heart to seek God.
4 Yehoshafat ya zauna a Urushalima, ya kuma fita yana shiga cikin mutane daga Beyersheba zuwa ƙasar tudun Efraim ya kuma juyar da su ga Ubangiji Allah na kakanninsu.
And Jehoshaphat dwelt at Jerusalem. And he went out again among the people from Beersheba to the hill-country of Ephraim, and brought them back to Jehovah, the God of their fathers.
5 Ya naɗa alƙalai a kowanne daga cikin biranen katanga na Yahuda a ƙasar.
And he set judges in the land throughout all the fortified cities of Judah, city by city,
6 Ya faɗa musu, “Ku lura da abin da kuke yi, gama shari’ar da kuke yi ba ta mutum ba ce, amma ta Ubangiji ce, yana tare da ku sa’ad da kuke yanke shari’a.
and said to the judges, Consider what ye do. For ye judge not for man, but for Jehovah, and he is with you in the judgment.
7 Yanzu fa ku ji tsoron Ubangiji. Ku yi hankali a kan abin da kuke yi, gama Ubangiji Allahnmu ba ya sonkai ko nuna wariya ko cin hanci.”
Now therefore let the fear of Jehovah be upon you. Take heed and do it. For there is no iniquity with Jehovah our God, nor respect of persons, nor taking of bribes.
8 A Urushalima kuma, Yehoshafat ya naɗa waɗansu Lawiyawa, firistoci da kawunan iyalan Isra’ilawa don su tabbatar da an bi dokar Ubangiji, su kuma sasanta tsakanin mutane. A Urushalima za su zauna.
Moreover in Jerusalem Jehoshaphat set from the Levites and the priests, and from the heads of the fathers of Israel for the judgment of Jehovah, and for controversies. And they returned to Jerusalem.
9 Ya ba su waɗannan umarnai, “Ku yi aikinku da aminci da tsoron Ubangiji da dukan zuciyarku.
And he charged them, saying, Thus ye shall do in the fear of Jehovah, faithfully, and with a perfect heart.
10 Cikin kowane batun da ya zo gabanku daga’yan’uwanku waɗanda suke zama a birane, ko batun na kisa ne ko kuwa waɗansu batuttuwan da suka shafi doka, umarnai, ƙa’idodi ko farillai, dole ku ja musu kunne kada su yi wa Ubangiji zunubi; in ba haka ba fushinsa zai sauko a kanku da’yan’uwanku. Ku yi wannan, ta haka ba za ku kuwa yi zunubi ba.
And whenever any controversy shall come to you from your brothers who dwell in their cities, between blood and blood, between law and commandment, statutes and ordinances, ye shall warn them, that they not be guilty towards Jehovah, and so wrath come upon you and upon your brothers. Do this, and ye shall not be guilty.
11 “Amariya, babban firist, shi ne zai shugabance ku a kan dukan al’amuran da suke na wajen Ubangiji, Zebadiya ɗan Ishmayel kuwa, shugabanku a kan dukan al’amuran da suka shafi sarki, Lawiyawa kuma za su zama a matsayin manya a gabanku. Ku yi abubuwa da ƙarfin hali, bari kuma Ubangiji yă kasance tare da masu yin gaskiya.”
And, behold, Amariah the chief priest is over you in all matters of Jehovah, and Zebadiah the son of Ishmael, the ruler of the house of Judah, in all the king's matters. The Levites shall also be officers before you. Deal courageously, and Jehovah be with the good.