< 2 Tarihi 18 >

1 Yanzu fa Yehoshafat ya wadace ƙwarai yana kuma da girma, ya kuma haɗa kansa da Ahab ta wurin aure.
Büyük bir zenginlik ve onura kavuşan Yehoşafat, evlilik bağıyla Ahav'a akraba oldu.
2 Bayan’yan shekaru sai ya gangara don yă ziyarci Ahab a Samariya. Ahab kuwa ya yanka tumaki da shanu masu yawa dominsa da kuma mutanen da suke tare da shi, ya kuma lallashe shi yă yaƙi Ramot Gileyad.
Birkaç yıl sonra Samiriye Kenti'nde yaşayan Ahav'ı görmeye gitti. Ahav onun ve yanındakilerin onuruna birçok davar, sığır keserek Ramot-Gilat'a saldırmak için onu kışkırttı.
3 Ahab sarkin Isra’ila ya tambayi Yehoshafat sarkin Yahuda ya ce, “Za ka tafi tare da ni mu yaƙi Ramot Gileyad?” Yehoshafat ya amsa ya ce, “Ni kamar kai ne, kuma mutanena kamar naka ne; za mu tafi tare da kai a yaƙin.”
İsrail Kralı Ahav, Yahuda Kralı Yehoşafat'a, “Ramot-Gilat'a karşı benimle birlikte savaşır mısın?” diye sordu. Yehoşafat, “Beni kendin, halkımı halkın say. Savaşta sana eşlik edeceğiz” diye yanıtladı,
4 Amma Yehoshafat ya kuma ce wa sarkin Isra’ila, “Da fari mu nemi bishewar Ubangiji.”
“Ama önce RAB'be danışalım” diye ekledi.
5 Saboda haka sarkin Isra’ila ya tattara annabawa duka, mutane ɗari huɗu, ya kuma tambaye su, “Mu tafi yaƙi a kan Ramot Gileyad ko kada mu tafi?” Suka amsa “Tafi, gama Allah zai ba da shi cikin hannun sarki.”
İsrail Kralı Ahav dört yüz peygamber toplayıp, “Ramot-Gilat'a karşı savaşalım mı, yoksa vaz mı geçeyim?” diye sordu. Peygamberler, “Savaş, çünkü Tanrı kenti senin eline teslim edecek” diye yanıtladılar.
6 Amma Yehoshafat ya yi tambaya ya ce, “Babu wani annabin Ubangiji a nan da za mu tambaya?”
Ama Yehoşafat, “Burada danışabileceğimiz RAB'bin başka peygamberi yok mu?” diye sordu.
7 Sarki Isra’ila ya amsa wa Yehoshafat, “Akwai guda har yanzu mai suna Mikahiya ɗan Imla, za mu iya nemi nufin Ubangiji daga gare shi, sai dai ba na sonsa domin bai taɓa yin annabci wani abu mai kyau game da ni ba, sai kullum masifa.” Yehoshafat ya amsa ya ce, “Kada sarki yă faɗa haka.”
İsrail Kralı, “Yimla oğlu Mikaya adında biri daha var” diye yanıtladı, “Onun aracılığıyla RAB'be danışabiliriz. Ama ben ondan nefret ederim. Çünkü benimle ilgili hiç iyi peygamberlik etmez, hep kötü şeyler söyler.” Yehoşafat, “Böyle konuşmaman gerekir, ey kral!” dedi.
8 Saboda haka sarkin Isra’ila ya kira ɗaya daga cikin ma’aikatansa ya ce, “A kawo Mikahiya ɗan Imla nan da nan.”
İsrail Kralı bir görevli çağırıp, “Hemen Yimla oğlu Mikaya'yı getir!” diye buyurdu.
9 Saye da rigunan sarakuna, sarki Isra’ila da Yehoshafat sarkin Yahuda suna zaune a kan kujerunsu na mulki a masussuka ta ƙofar shigar Samariya, tare da dukan annabawa suna ta annabci a gabansu.
İsrail Kralı Ahav ile Yahuda Kralı Yehoşafat kral giysileriyle Samiriye Kapısı'nın girişinde, harman yerine konan tahtlarında oturuyorlardı. Bütün peygamberler de onların önünde peygamberlik ediyordu.
10 To, fa, Zedekiya ɗan Kena’ana ya yi ƙahonin ƙarfe, ya kuma furta, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Da waɗannan za ka sassoki Arameyawa sai sun hallaka.’”
Kenaana oğlu Sidkiya, yaptığı demir boynuzları göstererek şöyle dedi: “RAB diyor ki, ‘Aramlılar'ı yok edinceye dek onları bu boynuzlarla vuracaksın.’”
11 Dukan sauran annabawan suka yi irin annabcin nan. Suka ce, “A haura zuwa Ramot Gileyad a yi nasara, gama Ubangiji zai ba da shi cikin hannun sarki.”
Öteki peygamberlerin hepsi de aynı şeyi söylediler: “Ramot– Gilat'a saldır, kazanacaksın! Çünkü RAB onları senin eline teslim edecek.”
12 Ɗan saƙon da ya tafi don yă kawo Mikahiya kuwa ya ce masa, “Duba, kowannen a cikin annabawa ya yi faɗin nasara wa sarki. Don haka kai ma ka yi maganar da za tă gamshi sarki kamar yadda suka yi.”
Mikaya'yı çağırmaya giden görevli ona, “Bak! Peygamberler bir ağızdan kral için olumlu şeyler söylüyorlar” dedi, “Rica ederim, senin sözün de onlarınkine uygun olsun; olumlu bir şey söyle.”
13 Amma Mikahiya ya ce, “Na rantse da ran Ubangiji, zan faɗa masa kawai abin da Allahna ya faɗa.”
Mikaya, “Yaşayan RAB'bin hakkı için, Tanrım ne derse onu söyleyeceğim” diye karşılık verdi.
14 Da suka iso, sarki ya tambaye shi, “Mika, mu tafi mu yaƙi Ramot Gileyad, ko kada mu tafi?” Ya amsa, “Kai masa yaƙi za ka kuwa yi nasara, gama za a ba da su a hannunka.”
Mikaya gelince kral, “Mikaya, Ramot-Gilat'a karşı savaşa gidelim mi, yoksa vaz mı geçeyim?” diye sordu. Mikaya, “Saldırın, kazanacaksınız! Çünkü onlar sizin elinize teslim edilecek” diye yanıtladı.
15 Sarki ya ce masa, “Sau nawa zan sa ka rantse don ka faɗa gaskiya a cikin sunan Ubangiji?”
Bunun üzerine kral, “RAB'bin adına bana gerçeğin dışında bir şey söylemeyeceğine ilişkin sana kaç kez ant içireyim?” diye sordu.
16 Sa’an nan Mikahiya ya amsa, “Na ga dukan Isra’ila sun warwatsu a kan tuddai kamar tumakin da ba su da makiyaya, kuma Ubangiji ya ce, ‘Waɗannan mutane ba su da maigida. Bari kowanne yă tafi gida cikin salama.’”
Mikaya şöyle karşılık verdi: “İsrailliler'i dağlara dağılmış çobansız koyunlar gibi gördüm. RAB, ‘Bunların sahibi yok. Herkes güvenlik içinde evine dönsün’ dedi.”
17 Sarkin Isra’ila ya ce wa Yehoshafat, “Ban faɗa maka cewa bai taɓa yin annabci wani abu mai kyau game da ni, in ba masifa ba?”
İsrail Kralı Ahav Yehoşafat'a, “Benimle ilgili iyi peygamberlik etmez, hep kötü şeyler söyler dememiş miydim?” dedi.
18 Mikahiya ya ci gaba, “Saboda haka sai ka ji maganar Ubangiji. Na ga Ubangiji yana zama a kan kursiyinsa tare da dukan rundunar sama tsaye a damansa da hagunsa.
Mikaya konuşmasını sürdürdü: “Öyleyse RAB'bin sözünü dinleyin! Gördüm ki, RAB tahtında oturuyor, bütün göksel varlıklar da sağında, solunda duruyordu.
19 Ubangiji kuwa ya ce, ‘Wa zai ruɗe Ahab sarki Isra’ila zuwa yaƙi da Ramot Gileyad da kuma zuwa mutuwarsa a can?’ “Wani ya ba da wata shawara, wani kuma wata dabam.
RAB sordu: ‘Ramot-Gilat'a saldırıp ölsün diye İsrail Kralı Ahav'ı kim kandıracak?’ “Kimi şöyle, kimi böyle derken,
20 A ƙarshe, wani ruhu ya zo gaba, ya tsaya a gaban Ubangiji ya ce, ‘Zan ruɗe shi.’ “Ubangiji ya yi tambaya, ‘Ta wace hanya?’
bir ruh çıkıp RAB'bin önünde durdu ve, ‘Ben onu kandıracağım’ dedi. “RAB, ‘Nasıl?’ diye sordu.
21 “Ya ce, ‘Zan tafi in zama ruhun ƙarya a bakunan dukan annabawansa.’ “Ubangiji ya ce, ‘Za ka yi nasara a ruɗinsa. Ka tafi, ka yi haka.’
“Ruh, ‘Aldatıcı ruh olarak gidip Ahav'ın bütün peygamberlerine yalan söyleteceğim’ diye karşılık verdi. “RAB, ‘Onu kandırmayı başaracaksın’ dedi, ‘Git, dediğini yap.’
22 “To yanzu, Ubangiji ya sa ruhun ruɗu a bakunan waɗannan annabawanka. Ubangiji ya ƙayyade masifa dominka.”
“İşte RAB bu peygamberlerinin ağzına aldatıcı bir ruh koydu. Çünkü sana kötülük etmeye karar verdi.”
23 Sai Zedekiya ɗan Kena’ana ya haura ya mari Mikahiya a fuska. Ya ce, “Ta wace hanya ce ruhun Ubangiji ya fita daga gare ni ya zo ya yi magana da kai?”
Kenaana oğlu Sidkiya yaklaşıp Mikaya'nın yüzüne bir tokat attı. “RAB'bin Ruhu nasıl benden çıkıp da seninle konuştu?” dedi.
24 Mikahiya ya amsa ya ce, “Za ka gane a ranar da ka je ka ɓuya a can cikin ɗaki.”
Mikaya, “Gizlenmek için bir iç odaya girdiğin gün göreceksin” diye yanıtladı.
25 Sa’an nan sarkin Isra’ila ya umarta, “Ɗauki Mikahiya ku aika da shi zuwa ga Amon mai mulkin birni da kuma ga Yowash ɗan sarki,
Bunun üzerine İsrail Kralı, “Mikaya'yı kentin yöneticisi Amon'a ve kralın oğlu Yoaş'a götürün” dedi,
26 ku ce ga abin da sarki ya ce, ‘Ku jefa wannan mutum a kurkuku kada kuma ku ba shi wani abu sai dai burodi da ruwa har sai na dawo lafiya.’”
“Ben güvenlik içinde dönünceye dek bu adamı cezaevinde tutmalarını, ona su ve ekmekten başka bir şey vermemelerini söyleyin!”
27 Mikahiya ya furta ya ce, “Idan har ka dawo lafiya, to, Ubangiji bai yi magana ta wurina ba.” Ya kuma ƙara da cewa, “Dukanku mutane, ku lura da maganata!”
Mikaya, “Eğer sen güvenlik içinde dönersen, RAB benim aracılığımla konuşmamış demektir” dedi ve, “Herkes bunu duysun!” diye ekledi.
28 Saboda haka sarkin Isra’ila da Yehoshafat sarkin Yahuda suka haura zuwa Ramot Gileyad.
İsrail Kralı Ahav'la Yahuda Kralı Yehoşafat Ramot-Gilat'a saldırmak için yola çıktılar.
29 Sarkin Isra’ila ya ce wa Yehoshafat, “Zan ɓad da kama in shiga yaƙin, amma ka sa kayanka na sarauta.” Saboda haka sarkin Isra’ila ya ɓad da kama ya shiga cikin yaƙin.
İsrail Kralı, Yehoşafat'a, “Ben kılık değiştirip savaşa öyle gireceğim, ama sen kral giysilerini giy” dedi. Böylece İsrail Kralı kılığını değiştirdi, sonra savaşa girdiler.
30 To, fa, sarkin Aram ya umarce shugabannin keken yaƙinsa ya ce, “Kada ku yaƙi kowa, ƙarami ko babba, sai dai sarkin Isra’ila.”
Aram Kralı, savaş arabalarının komutanlarına, “İsrail Kralı dışında, büyük küçük hiç kimseye saldırmayın!” diye buyruk vermişti.
31 Sa’ad da shugabannin kekunan yaƙi suka ga Yehoshafat, sai suka yi tsammani, “Wannan ne sarkin Isra’ila.” Saboda haka suka juya don su yaƙe shi, amma Yehoshafat ya yi ihu, Ubangiji kuma ya taimake shi. Allah ya janye su daga gare shi,
Savaş arabalarının komutanları Yehoşafat'ı görünce, İsrail Kralı sanıp saldırmak için ona döndüler. Yehoşafat yakarmaya başladı. RAB Tanrı ona yardım edip saldıranların yönünü değiştirdi.
32 gama sa’ad da shugabannin keken yaƙi suka ga cewa ba shi ne sarkin Isra’ila ba, sai suka daina binsa.
Komutanlar onun İsrail Kralı olmadığını anlayınca peşini bıraktılar.
33 Amma wani ya harba kibiya haka kawai, sai kibiyar ta sami sarki Ahab na Isra’ila a kafaɗa tsakanin rigar yaƙinsa na ƙarfe da ƙarfen ƙirjinsa. Sai sarki ya ce wa mai tuƙan keken yaƙi, “Juya ka fitar da ni daga wurin yaƙin. An ji mini rauni.”
O sırada bir asker rasgele attığı bir okla İsrail Kralı'nı zırhının parçalarının birleştiği yerden vurdu. Kral arabacısına, “Dönüp beni savaş alanından çıkar, yaralandım” dedi.
34 Duk yini yaƙi ya yi ta cin gaba, sarkin Isra’ila kuwa ya jingina kansa a cikin keken yaƙinsa yana duban Arameyawa har yamma. Sa’an nan a fāɗuwar rana sai ya mutu.
Savaş o gün şiddetlendi. Arabasında Aramlılar'a karşı akşama kadar dayanan İsrail Kralı gün batımında öldü.

< 2 Tarihi 18 >