< 2 Tarihi 18 >
1 Yanzu fa Yehoshafat ya wadace ƙwarai yana kuma da girma, ya kuma haɗa kansa da Ahab ta wurin aure.
Torej Józafat je imel bogastev in časti v obilju in sklenil svaštvo z Ahábom.
2 Bayan’yan shekaru sai ya gangara don yă ziyarci Ahab a Samariya. Ahab kuwa ya yanka tumaki da shanu masu yawa dominsa da kuma mutanen da suke tare da shi, ya kuma lallashe shi yă yaƙi Ramot Gileyad.
Po nekaj letih je odšel dol k Ahábu v Samarijo. Aháb je zanj in za ljudstvo, ki ga je imel s seboj, v obilju zaklal ovce in vole in pregovoril ga je, da gre z njim gor v Ramót Gileád.
3 Ahab sarkin Isra’ila ya tambayi Yehoshafat sarkin Yahuda ya ce, “Za ka tafi tare da ni mu yaƙi Ramot Gileyad?” Yehoshafat ya amsa ya ce, “Ni kamar kai ne, kuma mutanena kamar naka ne; za mu tafi tare da kai a yaƙin.”
Izraelov kralj Aháb je rekel Judovemu kralju Józafatu: »Hočeš iti z menoj v Ramót Gileád?« Ta mu je odgovoril: »Jaz sem, kakor si ti in moje ljudstvo kakor tvoje ljudstvo, in mi bomo s teboj v vojni.«
4 Amma Yehoshafat ya kuma ce wa sarkin Isra’ila, “Da fari mu nemi bishewar Ubangiji.”
Józafat je Izraelovemu kralju rekel: »Poizvedi, prosim te, danes pri Gospodovi besedi.«
5 Saboda haka sarkin Isra’ila ya tattara annabawa duka, mutane ɗari huɗu, ya kuma tambaye su, “Mu tafi yaƙi a kan Ramot Gileyad ko kada mu tafi?” Suka amsa “Tafi, gama Allah zai ba da shi cikin hannun sarki.”
Zato je Izraelov kralj izmed prerokov skupaj zbral štiristo mož in jim rekel: »Ali naj gremo v Ramót Gileád, da se bojujemo ali naj [to] opustim?« Rekli so: »Pojdi gor, kajti Bog ga bo izročil v kraljevo roko.«
6 Amma Yehoshafat ya yi tambaya ya ce, “Babu wani annabin Ubangiji a nan da za mu tambaya?”
Toda Józafat je rekel: » Ali tukaj poleg ni Gospodovega preroka, da bi lahko poizvedeli od njega?
7 Sarki Isra’ila ya amsa wa Yehoshafat, “Akwai guda har yanzu mai suna Mikahiya ɗan Imla, za mu iya nemi nufin Ubangiji daga gare shi, sai dai ba na sonsa domin bai taɓa yin annabci wani abu mai kyau game da ni ba, sai kullum masifa.” Yehoshafat ya amsa ya ce, “Kada sarki yă faɗa haka.”
Izraelov kralj je Józafatu rekel: » Je še en mož, pri katerem bi lahko povprašali Gospoda, toda jaz ga sovražim, kajti nikoli mi ne prerokuje dobro, temveč vedno hudo. Ta isti je Jimlájev sin Miha.« Józafat je rekel: »Naj kralj ne govori tako.«
8 Saboda haka sarkin Isra’ila ya kira ɗaya daga cikin ma’aikatansa ya ce, “A kawo Mikahiya ɗan Imla nan da nan.”
Izraelov kralj je dal poklicati enega izmed svojih častnikov in rekel: »Pojdi hitro po Jimlájevega sina Miha.«
9 Saye da rigunan sarakuna, sarki Isra’ila da Yehoshafat sarkin Yahuda suna zaune a kan kujerunsu na mulki a masussuka ta ƙofar shigar Samariya, tare da dukan annabawa suna ta annabci a gabansu.
Izraelov kralj in Judov kralj Józafat sta sedela, vsak izmed njiju na svojem prestolu, oblečena v njuna svečana oblačila in sedela na odprtem kraju pri vhodu velikih vrat Samarije, vsi preroki pa so prerokovali pred njima.
10 To, fa, Zedekiya ɗan Kena’ana ya yi ƙahonin ƙarfe, ya kuma furta, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Da waɗannan za ka sassoki Arameyawa sai sun hallaka.’”
Kenaanájev sin Cidkijá si je naredil rogove iz železa in rekel: »Tako govori Gospod: ›S temi boš porinil Sirijo, dokler ne bodo použiti.
11 Dukan sauran annabawan suka yi irin annabcin nan. Suka ce, “A haura zuwa Ramot Gileyad a yi nasara, gama Ubangiji zai ba da shi cikin hannun sarki.”
Vsi preroki so prerokovali tako, rekoč: »Pojdi gor v Ramót Gileád in uspevaj, kajti Gospod ga bo izročil v kraljevo roko.«
12 Ɗan saƙon da ya tafi don yă kawo Mikahiya kuwa ya ce masa, “Duba, kowannen a cikin annabawa ya yi faɗin nasara wa sarki. Don haka kai ma ka yi maganar da za tă gamshi sarki kamar yadda suka yi.”
Poslanec, ki je odšel, da pokliče Miha, mu je spregovoril, rekoč: »Glej, besede prerokov soglasno kralju razglašajo dobro. Naj bo torej tvoja beseda, prosim te, kakor ena izmed njihovih in govori dobro.«
13 Amma Mikahiya ya ce, “Na rantse da ran Ubangiji, zan faɗa masa kawai abin da Allahna ya faɗa.”
Miha je rekel: » Kakor živi Gospod, kar reče moj Bog, to bom govoril.«
14 Da suka iso, sarki ya tambaye shi, “Mika, mu tafi mu yaƙi Ramot Gileyad, ko kada mu tafi?” Ya amsa, “Kai masa yaƙi za ka kuwa yi nasara, gama za a ba da su a hannunka.”
Ko je prišel h kralju, mu je kralj rekel: »Miha, ali naj gremo gor v Ramót Gileád, da se bojujemo ali naj [to] opustim?« Ta je rekel: »Pojdite gor in uspevajte in izročeni bodo v vašo roko.«
15 Sarki ya ce masa, “Sau nawa zan sa ka rantse don ka faɗa gaskiya a cikin sunan Ubangiji?”
Kralj mu je rekel: »Kolikokrat te bom zaklinjal, da mi ne poveš ničesar, razen resnice, v Gospodovem imenu?«
16 Sa’an nan Mikahiya ya amsa, “Na ga dukan Isra’ila sun warwatsu a kan tuddai kamar tumakin da ba su da makiyaya, kuma Ubangiji ya ce, ‘Waɗannan mutane ba su da maigida. Bari kowanne yă tafi gida cikin salama.’”
Potem je rekel: »Videl sem vsega Izraela razkropljenega po gorah kakor ovce, ki nimajo pastirja in Gospod je rekel: ›Ti nimajo gospodarja, naj se torej vrnejo v miru, vsak mož k svoji hiši.‹«
17 Sarkin Isra’ila ya ce wa Yehoshafat, “Ban faɗa maka cewa bai taɓa yin annabci wani abu mai kyau game da ni, in ba masifa ba?”
Izraelov kralj je Józafatu rekel: »Ali ti nisem rekel, da mi ne bo prerokoval dobro, temveč zlo?«
18 Mikahiya ya ci gaba, “Saboda haka sai ka ji maganar Ubangiji. Na ga Ubangiji yana zama a kan kursiyinsa tare da dukan rundunar sama tsaye a damansa da hagunsa.
Ponovno je rekel: »Zato poslušajte besedo od Gospoda: ›Videl sem Gospoda sedeti na svojem prestolu in vso nebeško vojsko stati na njegovi desni roki in na njegovi levi.‹
19 Ubangiji kuwa ya ce, ‘Wa zai ruɗe Ahab sarki Isra’ila zuwa yaƙi da Ramot Gileyad da kuma zuwa mutuwarsa a can?’ “Wani ya ba da wata shawara, wani kuma wata dabam.
Gospod je rekel: ›Kdo bo premamil Izraelovega kralj Ahába, da gre lahko gor in pade pri Ramót Gileádu?‹ Eden je odgovoril na ta način, drugi je odgovoril na ta način.
20 A ƙarshe, wani ruhu ya zo gaba, ya tsaya a gaban Ubangiji ya ce, ‘Zan ruɗe shi.’ “Ubangiji ya yi tambaya, ‘Ta wace hanya?’
Tedaj je šel naprej duh in obstal pred Gospodom ter rekel: ›Jaz ga bom premamil.‹ Gospod mu je rekel: ›S čim?‹
21 “Ya ce, ‘Zan tafi in zama ruhun ƙarya a bakunan dukan annabawansa.’ “Ubangiji ya ce, ‘Za ka yi nasara a ruɗinsa. Ka tafi, ka yi haka.’
Rekel je: ›Šel bom ven in bom lažniv duh v ustih vseh njegovih prerokov.‹ In Gospod je rekel: ›Ti ga boš premamil in ti ga boš tudi pregovoril. Pojdi ven in stôri tako.‹
22 “To yanzu, Ubangiji ya sa ruhun ruɗu a bakunan waɗannan annabawanka. Ubangiji ya ƙayyade masifa dominka.”
Zdaj torej glejte, Gospod je položil lažnivega duha v usta teh tvojih prerokov in Gospod je zoper tebe govoril zlo.«
23 Sai Zedekiya ɗan Kena’ana ya haura ya mari Mikahiya a fuska. Ya ce, “Ta wace hanya ce ruhun Ubangiji ya fita daga gare ni ya zo ya yi magana da kai?”
Potem je Kenaanájev sin Cidkijá prišel bliže in udaril Miha po licu ter rekel: »Katero pot je odšel Gospodov duh od mene, da govori tebi?«
24 Mikahiya ya amsa ya ce, “Za ka gane a ranar da ka je ka ɓuya a can cikin ɗaki.”
Miha je rekel: »Glej, videl boš ta dan, ko boš šel v notranjo sobo, da se skriješ.«
25 Sa’an nan sarkin Isra’ila ya umarta, “Ɗauki Mikahiya ku aika da shi zuwa ga Amon mai mulkin birni da kuma ga Yowash ɗan sarki,
Potem je Izraelov kralj rekel: »Vzemite Miha in ga odvedite nazaj k Amónu, voditelju mesta in h kraljevemu sinu Joášu
26 ku ce ga abin da sarki ya ce, ‘Ku jefa wannan mutum a kurkuku kada kuma ku ba shi wani abu sai dai burodi da ruwa har sai na dawo lafiya.’”
ter recite: ›Tako govori kralj: ›Tega pajdaša postavita v ječo in ga hranita s kruhom stiske in z vodo stiske, dokler se ne vrnem v miru.‹«
27 Mikahiya ya furta ya ce, “Idan har ka dawo lafiya, to, Ubangiji bai yi magana ta wurina ba.” Ya kuma ƙara da cewa, “Dukanku mutane, ku lura da maganata!”
Miha je rekel: »Če se zagotovo vrneš v miru, potem po meni ni govoril Gospod.« Rekel je [še]: »Prisluhnite vsa ve ljudstva.«
28 Saboda haka sarkin Isra’ila da Yehoshafat sarkin Yahuda suka haura zuwa Ramot Gileyad.
Tako sta Izraelov kralj in Judov kralj Józafat odšla gor do Ramót Gileáda.
29 Sarkin Isra’ila ya ce wa Yehoshafat, “Zan ɓad da kama in shiga yaƙin, amma ka sa kayanka na sarauta.” Saboda haka sarkin Isra’ila ya ɓad da kama ya shiga cikin yaƙin.
Izraelov kralj je Józafatu rekel: »Preoblekel se bom in šel v bitko, toda ti si nadeni svoja svečana oblačila.« Tako se je Izraelov kralj preoblekel in odšla sta na bitko.
30 To, fa, sarkin Aram ya umarce shugabannin keken yaƙinsa ya ce, “Kada ku yaƙi kowa, ƙarami ko babba, sai dai sarkin Isra’ila.”
Torej sirski kralj je zapovedal poveljnikom bojnih vozov, ki so bili z njim, rekoč: »Ne borite se z malim ali velikim, razen samo z Izraelovim kraljem.«
31 Sa’ad da shugabannin kekunan yaƙi suka ga Yehoshafat, sai suka yi tsammani, “Wannan ne sarkin Isra’ila.” Saboda haka suka juya don su yaƙe shi, amma Yehoshafat ya yi ihu, Ubangiji kuma ya taimake shi. Allah ya janye su daga gare shi,
Pripetilo se je, ko so poveljniki bojnih vozov zagledali Józafata, da so rekli: »Ta je Izraelov kralj.« Zato so ga obdali, da se bojujejo, toda Józafat je zavpil in Gospod mu je pomagal in Bog jih je spodbodel, da odidejo od njega.
32 gama sa’ad da shugabannin keken yaƙi suka ga cewa ba shi ne sarkin Isra’ila ba, sai suka daina binsa.
Kajti pripetilo se je, da ko so poveljniki bojnih vozov zaznali, da to ni bil Izraelov kralj, so se ponovno obrnili nazaj od zasledovanja [za] njim.
33 Amma wani ya harba kibiya haka kawai, sai kibiyar ta sami sarki Ahab na Isra’ila a kafaɗa tsakanin rigar yaƙinsa na ƙarfe da ƙarfen ƙirjinsa. Sai sarki ya ce wa mai tuƙan keken yaƙi, “Juya ka fitar da ni daga wurin yaƙin. An ji mini rauni.”
Nek mož pa je preprosto napel lok in Izraelovega kralja zadel med člene prsnega oklepa. Zato je vozniku svojega bojnega voza rekel: »Obrni svojo roko, da me lahko odvedeš iz vojske, kajti ranjen sem.«
34 Duk yini yaƙi ya yi ta cin gaba, sarkin Isra’ila kuwa ya jingina kansa a cikin keken yaƙinsa yana duban Arameyawa har yamma. Sa’an nan a fāɗuwar rana sai ya mutu.
Bitka je ta dan narasla, vendar je Izraelov kralj sam stal pokonci na svojem bojnem vozu zoper Sirce do večera, okoli časa zahajanja sonca pa je umrl.