< 2 Tarihi 18 >

1 Yanzu fa Yehoshafat ya wadace ƙwarai yana kuma da girma, ya kuma haɗa kansa da Ahab ta wurin aure.
Et Josaphat avait en abondance richesse et gloire, et il s'allia à Achab.
2 Bayan’yan shekaru sai ya gangara don yă ziyarci Ahab a Samariya. Ahab kuwa ya yanka tumaki da shanu masu yawa dominsa da kuma mutanen da suke tare da shi, ya kuma lallashe shi yă yaƙi Ramot Gileyad.
Et au bout de quelques années il descendit chez Achab à Samarie, et Achab tua pour lui nombre de moutons et des bœufs, ainsi que pour les gens de sa suite et l'invita à marcher contre Ramoth en Galaad.
3 Ahab sarkin Isra’ila ya tambayi Yehoshafat sarkin Yahuda ya ce, “Za ka tafi tare da ni mu yaƙi Ramot Gileyad?” Yehoshafat ya amsa ya ce, “Ni kamar kai ne, kuma mutanena kamar naka ne; za mu tafi tare da kai a yaƙin.”
Et Achab, roi d'Israël, dit à Josaphat, roi de Juda: Veux-tu marcher avec moi contre Ramoth en Galaad? Et il lui répondit: Nous serons de pair moi et toi, et ton peuple et mon peuple, et avec toi j'irai en guerre.
4 Amma Yehoshafat ya kuma ce wa sarkin Isra’ila, “Da fari mu nemi bishewar Ubangiji.”
Et Josaphat dit au roi d'Israël: Qu'il te plaise requérir aujourd'hui la parole de l'Éternel!
5 Saboda haka sarkin Isra’ila ya tattara annabawa duka, mutane ɗari huɗu, ya kuma tambaye su, “Mu tafi yaƙi a kan Ramot Gileyad ko kada mu tafi?” Suka amsa “Tafi, gama Allah zai ba da shi cikin hannun sarki.”
Et le roi d'Israël réunit les prophètes au nombre de quatre cents hommes, et leur dit: Marcherons-nous à l'attaque de Ramoth en Galaad? ou y renoncerai-je? Et ils dirent: Marche! et Dieu la livrera aux mains du roi.
6 Amma Yehoshafat ya yi tambaya ya ce, “Babu wani annabin Ubangiji a nan da za mu tambaya?”
Et Josaphat dit: N'y a-t-il point encore ici de prophète de l'Éternel, par qui nous puissions consulter?
7 Sarki Isra’ila ya amsa wa Yehoshafat, “Akwai guda har yanzu mai suna Mikahiya ɗan Imla, za mu iya nemi nufin Ubangiji daga gare shi, sai dai ba na sonsa domin bai taɓa yin annabci wani abu mai kyau game da ni ba, sai kullum masifa.” Yehoshafat ya amsa ya ce, “Kada sarki yă faɗa haka.”
Et le roi d'Israël dit à Josaphat: Il y a encore un homme par qui nous pourrions consulter l'Éternel; mais je le hais parce que pour moi il ne prophétise jamais en bien, mais toujours en mal; c'est Michée, fils de Jimla. Et Josaphat dit: Que le roi ne parle pas de la sorte!
8 Saboda haka sarkin Isra’ila ya kira ɗaya daga cikin ma’aikatansa ya ce, “A kawo Mikahiya ɗan Imla nan da nan.”
Alors le roi d'Israël appela un eunuque et lui dit: Fais vite venir Michée, fils de Jimla.
9 Saye da rigunan sarakuna, sarki Isra’ila da Yehoshafat sarkin Yahuda suna zaune a kan kujerunsu na mulki a masussuka ta ƙofar shigar Samariya, tare da dukan annabawa suna ta annabci a gabansu.
Cependant le roi d'Israël et Josaphat, roi de Juda, étaient assis, chacun sur son trône, revêtus de leur costume, et se tenaient dans une aire aux abords de la porte de Samarie, et tous les prophètes prophétisaient devant eux.
10 To, fa, Zedekiya ɗan Kena’ana ya yi ƙahonin ƙarfe, ya kuma furta, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Da waɗannan za ka sassoki Arameyawa sai sun hallaka.’”
Et Sédécias, fils de Cnaana, se fit des cornes de fer et dit: Ainsi parle l'Éternel: Avec ceci tu heurteras les Syriens jusqu'à les achever.
11 Dukan sauran annabawan suka yi irin annabcin nan. Suka ce, “A haura zuwa Ramot Gileyad a yi nasara, gama Ubangiji zai ba da shi cikin hannun sarki.”
Et tous les prophètes prophétisaient de même et disaient: Marche contre Ramoth en Galaad et tu viendras à bout d'elle, et l'Éternel la livrera aux mains du roi.
12 Ɗan saƙon da ya tafi don yă kawo Mikahiya kuwa ya ce masa, “Duba, kowannen a cikin annabawa ya yi faɗin nasara wa sarki. Don haka kai ma ka yi maganar da za tă gamshi sarki kamar yadda suka yi.”
Et le messager qui était allé quérir Michée, lui parla en ces termes: Voici, les discours des prophètes sont à l'unanimité favorables au roi, que ton discours soit donc comme celui de l'un d'eux, et parle favorablement.
13 Amma Mikahiya ya ce, “Na rantse da ran Ubangiji, zan faɗa masa kawai abin da Allahna ya faɗa.”
Et Michée dit: Par la vie de l'Éternel! ce que mon Dieu me dira, je le rendrai.
14 Da suka iso, sarki ya tambaye shi, “Mika, mu tafi mu yaƙi Ramot Gileyad, ko kada mu tafi?” Ya amsa, “Kai masa yaƙi za ka kuwa yi nasara, gama za a ba da su a hannunka.”
Et quand il fut arrivé vers le roi, le roi lui dit: Michée, marcherons-nous à l'attaque de Ramoth en Galaad? ou y renoncerai-je? Et il répondit: Marchez!…, et vous réussirez…, et elle sera livrée à vos mains!
15 Sarki ya ce masa, “Sau nawa zan sa ka rantse don ka faɗa gaskiya a cikin sunan Ubangiji?”
Et le roi lui dit: Combien de fois faut-il que je t'adjure ils de ne me dire que la vérité au nom de l'Éternel!
16 Sa’an nan Mikahiya ya amsa, “Na ga dukan Isra’ila sun warwatsu a kan tuddai kamar tumakin da ba su da makiyaya, kuma Ubangiji ya ce, ‘Waɗannan mutane ba su da maigida. Bari kowanne yă tafi gida cikin salama.’”
Et il dit: J'ai vu tout Israël épars sur les montagnes comme un troupeau sans pasteur. Et l'Éternel dit: Ils sont sans maîtres! qu'ils retournent chacun dans sa maison en paix!
17 Sarkin Isra’ila ya ce wa Yehoshafat, “Ban faɗa maka cewa bai taɓa yin annabci wani abu mai kyau game da ni, in ba masifa ba?”
Alors le roi d'Israël dit à Josaphat: Ne te l'ai-je pas dit? pour moi il ne prophétise pas en bien, mais en mal.
18 Mikahiya ya ci gaba, “Saboda haka sai ka ji maganar Ubangiji. Na ga Ubangiji yana zama a kan kursiyinsa tare da dukan rundunar sama tsaye a damansa da hagunsa.
Et il dit: En conséquence, écoutez la parole de l'Éternel: J'ai vu l'Éternel assis sur son trône, et toute l'armée des Cieux debout à sa droite et à sa gauche.
19 Ubangiji kuwa ya ce, ‘Wa zai ruɗe Ahab sarki Isra’ila zuwa yaƙi da Ramot Gileyad da kuma zuwa mutuwarsa a can?’ “Wani ya ba da wata shawara, wani kuma wata dabam.
Et l'Éternel dit: Qui veut suggérer à Achab, roi d'Israël, de marcher pour aller tomber à Ramoth en Galaad? Et l'un parla d'une manière, et l'autre d'une autre.
20 A ƙarshe, wani ruhu ya zo gaba, ya tsaya a gaban Ubangiji ya ce, ‘Zan ruɗe shi.’ “Ubangiji ya yi tambaya, ‘Ta wace hanya?’
Alors l'Esprit sortit et parut devant l'Éternel et dit: Moi, je le lui suggérerai.
21 “Ya ce, ‘Zan tafi in zama ruhun ƙarya a bakunan dukan annabawansa.’ “Ubangiji ya ce, ‘Za ka yi nasara a ruɗinsa. Ka tafi, ka yi haka.’
Et l'Éternel lui dit: Comment? Et il dit: Je partirai et serai esprit de mensonge dans la bouche de tous ses prophètes. Et il dit: Suggère! et emporte-le! pars et ainsi fais!
22 “To yanzu, Ubangiji ya sa ruhun ruɗu a bakunan waɗannan annabawanka. Ubangiji ya ƙayyade masifa dominka.”
Eh bien! voici, l'Éternel a mis un esprit de mensonge dans la bouche de ces tiens prophètes, et l'Éternel a prononcé sur toi la ruine.
23 Sai Zedekiya ɗan Kena’ana ya haura ya mari Mikahiya a fuska. Ya ce, “Ta wace hanya ce ruhun Ubangiji ya fita daga gare ni ya zo ya yi magana da kai?”
Alors Sédécias, fils de Cnaana, s'approcha et frappa Michée sur la joue et dit: Est-ce là la voie par où l'esprit de l'Éternel se serait retiré de moi pour communiquer avec toi?
24 Mikahiya ya amsa ya ce, “Za ka gane a ranar da ka je ka ɓuya a can cikin ɗaki.”
Et Michée dit: Voici tu le verras le jour même où tu iras de chambre en chambre pour te cacher.
25 Sa’an nan sarkin Isra’ila ya umarta, “Ɗauki Mikahiya ku aika da shi zuwa ga Amon mai mulkin birni da kuma ga Yowash ɗan sarki,
Et le roi d'Israël dit: Arrêtez Michée et le menez à Amon, préfet de la ville, et à Joas, fils du roi,
26 ku ce ga abin da sarki ya ce, ‘Ku jefa wannan mutum a kurkuku kada kuma ku ba shi wani abu sai dai burodi da ruwa har sai na dawo lafiya.’”
et dites: Ainsi parle le roi: Mettez cet homme en prison, et nourrissez-le de pain et d'eau de rigueur, jusqu'à ce que je revienne sain et sauf.
27 Mikahiya ya furta ya ce, “Idan har ka dawo lafiya, to, Ubangiji bai yi magana ta wurina ba.” Ya kuma ƙara da cewa, “Dukanku mutane, ku lura da maganata!”
Et Michée dit: Si tu reviens sain et sauf, l'Éternel n'a pas parlé par moi. Et il dit: Entendez, vous tous les peuples!
28 Saboda haka sarkin Isra’ila da Yehoshafat sarkin Yahuda suka haura zuwa Ramot Gileyad.
Et le roi d'Israël avec Josaphat, roi de Juda, marcha contre Ramoth en Galaad.
29 Sarkin Isra’ila ya ce wa Yehoshafat, “Zan ɓad da kama in shiga yaƙin, amma ka sa kayanka na sarauta.” Saboda haka sarkin Isra’ila ya ɓad da kama ya shiga cikin yaƙin.
Et le roi d'Israël dit à Josaphat: Je me travestirai pour aller au combat, mais toi, revêts-toi de ton costume. Le roi d'Israël se travestit donc, et ils vinrent au combat.
30 To, fa, sarkin Aram ya umarce shugabannin keken yaƙinsa ya ce, “Kada ku yaƙi kowa, ƙarami ko babba, sai dai sarkin Isra’ila.”
Et le roi de Syrie avait donné cet ordre aux commandants de ses chars: N'attaquez personne, ni petit, ni grand, sinon le roi d'Israël seul.
31 Sa’ad da shugabannin kekunan yaƙi suka ga Yehoshafat, sai suka yi tsammani, “Wannan ne sarkin Isra’ila.” Saboda haka suka juya don su yaƙe shi, amma Yehoshafat ya yi ihu, Ubangiji kuma ya taimake shi. Allah ya janye su daga gare shi,
Et lorsque les commandants des chars virent Josaphat, ils se dirent: C'est le roi d'Israël! et ils appuyèrent de son côté pour l'attaquer. Alors Josaphat fit un cri, et l'Éternel le secourut, et Dieu les écarta de lui;
32 gama sa’ad da shugabannin keken yaƙi suka ga cewa ba shi ne sarkin Isra’ila ba, sai suka daina binsa.
et lorsque les commandants des chars virent que ce n'était pas le roi d'Israël, ils revinrent de sa poursuite.
33 Amma wani ya harba kibiya haka kawai, sai kibiyar ta sami sarki Ahab na Isra’ila a kafaɗa tsakanin rigar yaƙinsa na ƙarfe da ƙarfen ƙirjinsa. Sai sarki ya ce wa mai tuƙan keken yaƙi, “Juya ka fitar da ni daga wurin yaƙin. An ji mini rauni.”
Cependant un homme banda son arc tout innocemment, et atteignit le roi d'Israël entre les pendants de la cuirasse et la cotte d'armes. Et celui-ci dit à son cocher: Tourne et mène-moi hors de la mêlée, car je suis blessé.
34 Duk yini yaƙi ya yi ta cin gaba, sarkin Isra’ila kuwa ya jingina kansa a cikin keken yaƙinsa yana duban Arameyawa har yamma. Sa’an nan a fāɗuwar rana sai ya mutu.
Et la bataille était intense pendant cette journée, et le roi d'Israël resta debout sur son char en vue des Syriens jusqu'au soir, et il mourut au moment du coucher du soleil.

< 2 Tarihi 18 >