< 2 Tarihi 18 >

1 Yanzu fa Yehoshafat ya wadace ƙwarai yana kuma da girma, ya kuma haɗa kansa da Ahab ta wurin aure.
Jehoshaphat became very wealthy and was greatly honored. But then he arranged for one of his family to marry someone from the family of King Ahab [of Israel].
2 Bayan’yan shekaru sai ya gangara don yă ziyarci Ahab a Samariya. Ahab kuwa ya yanka tumaki da shanu masu yawa dominsa da kuma mutanen da suke tare da shi, ya kuma lallashe shi yă yaƙi Ramot Gileyad.
Several years later, he went down [from Jerusalem] to Samaria to visit Ahab. Ahab welcomed him and the people who had come with him by slaughtering many sheep and cattle [for a feast].
3 Ahab sarkin Isra’ila ya tambayi Yehoshafat sarkin Yahuda ya ce, “Za ka tafi tare da ni mu yaƙi Ramot Gileyad?” Yehoshafat ya amsa ya ce, “Ni kamar kai ne, kuma mutanena kamar naka ne; za mu tafi tare da kai a yaƙin.”
Then he asked Jehoshaphat, “Will you [and your army] go with my army to attack Ramoth [city] in [the] Gilead [region]?” Jehoshaphat replied, “My soldiers and I will go to the battle when you tell us to go.”
4 Amma Yehoshafat ya kuma ce wa sarkin Isra’ila, “Da fari mu nemi bishewar Ubangiji.”
Then he added, “But we should ask Yahweh first, to find out what he wants us to do.”
5 Saboda haka sarkin Isra’ila ya tattara annabawa duka, mutane ɗari huɗu, ya kuma tambaye su, “Mu tafi yaƙi a kan Ramot Gileyad ko kada mu tafi?” Suka amsa “Tafi, gama Allah zai ba da shi cikin hannun sarki.”
So the king of Israel gathered all his 400 prophets and asked them, “Should we go to attack the people of Ramoth [city], or should we not do that?” They replied, “Yes, go [and attack them] because God will enable your army to defeat them.”
6 Amma Yehoshafat ya yi tambaya ya ce, “Babu wani annabin Ubangiji a nan da za mu tambaya?”
But Jehoshaphat asked, “Is there no prophet of Yahweh here whom we can ask?”
7 Sarki Isra’ila ya amsa wa Yehoshafat, “Akwai guda har yanzu mai suna Mikahiya ɗan Imla, za mu iya nemi nufin Ubangiji daga gare shi, sai dai ba na sonsa domin bai taɓa yin annabci wani abu mai kyau game da ni ba, sai kullum masifa.” Yehoshafat ya amsa ya ce, “Kada sarki yă faɗa haka.”
The king of Israel replied, “There is still one man here, whom we can ask to find out what Yahweh wants, his name is Micaiah, the son of Imlah. But I hate him because he never says anything good about me. He always predicts [that] bad [things will happen to me].” Jehoshaphat replied, “King Ahab, you should not say that!”
8 Saboda haka sarkin Isra’ila ya kira ɗaya daga cikin ma’aikatansa ya ce, “A kawo Mikahiya ɗan Imla nan da nan.”
So the king of Israel told one of his officials to summon Micaiah immediately.
9 Saye da rigunan sarakuna, sarki Isra’ila da Yehoshafat sarkin Yahuda suna zaune a kan kujerunsu na mulki a masussuka ta ƙofar shigar Samariya, tare da dukan annabawa suna ta annabci a gabansu.
The king of Israel and the king of Judah were sitting there on their thrones, wearing their royal robes. They were at the place where people threshed grain, near the gate of Samaria [city]. All of [Ahab’s] prophets were standing in front of them, predicting what was going to happen.
10 To, fa, Zedekiya ɗan Kena’ana ya yi ƙahonin ƙarfe, ya kuma furta, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Da waɗannan za ka sassoki Arameyawa sai sun hallaka.’”
[One of them whose name was] Zedekiah, the son of Kenaanah, had made from iron something that resembled the horns of a bull. He proclaimed to Ahab, “This is what Yahweh says: ‘With horns [like these], your [army] will keep attacking the army of Syria [like a bull attacks another animal], until you completely destroy them.’”
11 Dukan sauran annabawan suka yi irin annabcin nan. Suka ce, “A haura zuwa Ramot Gileyad a yi nasara, gama Ubangiji zai ba da shi cikin hannun sarki.”
All the other prophets [of Ahab] agreed. They said, “Yes! If you attack Ramoth [city] in [the] Gilead [region], you will be successful, because Yahweh will enable you to defeat them.”
12 Ɗan saƙon da ya tafi don yă kawo Mikahiya kuwa ya ce masa, “Duba, kowannen a cikin annabawa ya yi faɗin nasara wa sarki. Don haka kai ma ka yi maganar da za tă gamshi sarki kamar yadda suka yi.”
The messenger who went to summon Micaiah said to him, “Listen to me! All the other prophets are unitedly predicting that the king will be successful [in the battle]. So be sure to agree with them and say that the king’s army will be successful!”
13 Amma Mikahiya ya ce, “Na rantse da ran Ubangiji, zan faɗa masa kawai abin da Allahna ya faɗa.”
But Micaiah said, “As surely as Yahweh lives, I will tell the king only what Yahweh tells me to say.”
14 Da suka iso, sarki ya tambaye shi, “Mika, mu tafi mu yaƙi Ramot Gileyad, ko kada mu tafi?” Ya amsa, “Kai masa yaƙi za ka kuwa yi nasara, gama za a ba da su a hannunka.”
When Micaiah arrived, the king [of Israel] asked him, “Should we go to attack Ramoth, or not?” Micaiah replied, “Sure, go! Yahweh will enable your army to defeat them!”
15 Sarki ya ce masa, “Sau nawa zan sa ka rantse don ka faɗa gaskiya a cikin sunan Ubangiji?”
But King Ahab [realized that Micaiah was lying, so he] said to Micaiah, “I have told you many times that you must always tell only the truth when you say what Yahweh [has revealed to you]!”
16 Sa’an nan Mikahiya ya amsa, “Na ga dukan Isra’ila sun warwatsu a kan tuddai kamar tumakin da ba su da makiyaya, kuma Ubangiji ya ce, ‘Waɗannan mutane ba su da maigida. Bari kowanne yă tafi gida cikin salama.’”
Then Micaiah replied, “[The truth is that in a vision] I saw all the troops of Israel scattered on the mountains. They seemed to be like sheep that did not have a shepherd. And Yahweh said, ‘Their master has been killed. So tell them all to go home peacefully.’”
17 Sarkin Isra’ila ya ce wa Yehoshafat, “Ban faɗa maka cewa bai taɓa yin annabci wani abu mai kyau game da ni, in ba masifa ba?”
Ahab said to Jehoshaphat, “I told you that he never predicts that anything good will happen to me! He [always] predicts that bad things will happen to me.”
18 Mikahiya ya ci gaba, “Saboda haka sai ka ji maganar Ubangiji. Na ga Ubangiji yana zama a kan kursiyinsa tare da dukan rundunar sama tsaye a damansa da hagunsa.
But Micaiah continued, saying, “Listen to what Yahweh showed to me! [In a vision] I saw Yahweh sitting on his throne, with all the armies of heaven [standing around him], on his right side and on his left side.
19 Ubangiji kuwa ya ce, ‘Wa zai ruɗe Ahab sarki Isra’ila zuwa yaƙi da Ramot Gileyad da kuma zuwa mutuwarsa a can?’ “Wani ya ba da wata shawara, wani kuma wata dabam.
And Yahweh said, ‘Who can persuade Ahab, the king of Israel, to go to fight against the people of Ramoth, in order that he may be killed there?’ “Some suggested one thing, and others suggested something else.
20 A ƙarshe, wani ruhu ya zo gaba, ya tsaya a gaban Ubangiji ya ce, ‘Zan ruɗe shi.’ “Ubangiji ya yi tambaya, ‘Ta wace hanya?’
“Finally one spirit, [having received a message from Satan], came to Yahweh and said, ‘I can do it!’ “Yahweh asked him, ‘How will you do it?’
21 “Ya ce, ‘Zan tafi in zama ruhun ƙarya a bakunan dukan annabawansa.’ “Ubangiji ya ce, ‘Za ka yi nasara a ruɗinsa. Ka tafi, ka yi haka.’
“The spirit replied, ‘I will go and inspire all of Ahab’s prophets to tell lies.’ Yahweh said, ‘You will be successful; go and do it!’
22 “To yanzu, Ubangiji ya sa ruhun ruɗu a bakunan waɗannan annabawanka. Ubangiji ya ƙayyade masifa dominka.”
“So now [I tell you that] Yahweh has caused your prophets to lie to you. Yahweh has decided that something terrible will happen to you.”
23 Sai Zedekiya ɗan Kena’ana ya haura ya mari Mikahiya a fuska. Ya ce, “Ta wace hanya ce ruhun Ubangiji ya fita daga gare ni ya zo ya yi magana da kai?”
Then Zedekiah son of Kenaanah walked over to Micaiah and slapped him on his face. He said, “Do you think that Yahweh’s Spirit left me in order to speak to you?”
24 Mikahiya ya amsa ya ce, “Za ka gane a ranar da ka je ka ɓuya a can cikin ɗaki.”
Micaiah replied, “You will find out for yourself [to which of us Yahweh’s Spirit has truly spoken] on the day when you go into a room of some house to hide [from the Syrian soldiers]!”
25 Sa’an nan sarkin Isra’ila ya umarta, “Ɗauki Mikahiya ku aika da shi zuwa ga Amon mai mulkin birni da kuma ga Yowash ɗan sarki,
King Ahab commanded [his soldiers], “Seize Micaiah and take him to Amon, the governor of this city, and to my son Joash.
26 ku ce ga abin da sarki ya ce, ‘Ku jefa wannan mutum a kurkuku kada kuma ku ba shi wani abu sai dai burodi da ruwa har sai na dawo lafiya.’”
Tell them that I have commanded that they should put this man in prison and give him only bread and water. Do not give him anything else to eat until I return safely [from the battle]!”
27 Mikahiya ya furta ya ce, “Idan har ka dawo lafiya, to, Ubangiji bai yi magana ta wurina ba.” Ya kuma ƙara da cewa, “Dukanku mutane, ku lura da maganata!”
Micaiah replied, “If you return safely, [it will be clear that] it was not Yahweh who told me what to say to you!” Then he said [to all those who were standing there], “Do not forget what I have said [to King Ahab]!”
28 Saboda haka sarkin Isra’ila da Yehoshafat sarkin Yahuda suka haura zuwa Ramot Gileyad.
So the king of Israel and the king of Judah [led their armies] to Ramoth, in [the] Gilead [region].
29 Sarkin Isra’ila ya ce wa Yehoshafat, “Zan ɓad da kama in shiga yaƙin, amma ka sa kayanka na sarauta.” Saboda haka sarkin Isra’ila ya ɓad da kama ya shiga cikin yaƙin.
King Ahab said to Jehoshaphat, “I will put on different clothes, [in order that no one will recognize that I am the king.] But you should wear your royal robe.” So the king of Israel disguised himself, and they both went into the battle.
30 To, fa, sarkin Aram ya umarce shugabannin keken yaƙinsa ya ce, “Kada ku yaƙi kowa, ƙarami ko babba, sai dai sarkin Isra’ila.”
The King of Syria told his soldiers who were driving the chariots, “Attack only the king of Israel!”
31 Sa’ad da shugabannin kekunan yaƙi suka ga Yehoshafat, sai suka yi tsammani, “Wannan ne sarkin Isra’ila.” Saboda haka suka juya don su yaƙe shi, amma Yehoshafat ya yi ihu, Ubangiji kuma ya taimake shi. Allah ya janye su daga gare shi,
So when the soldiers who were driving the Syrian chariots saw Jehoshaphat [wearing the royal robes], they thought “He must be the king of Israel!”
32 gama sa’ad da shugabannin keken yaƙi suka ga cewa ba shi ne sarkin Isra’ila ba, sai suka daina binsa.
So they turned to attack him. But when Jehoshaphat cried out, Yahweh helped him, and they realized that he was not the king of Israel. And God caused them to stop pursuing him.
33 Amma wani ya harba kibiya haka kawai, sai kibiyar ta sami sarki Ahab na Isra’ila a kafaɗa tsakanin rigar yaƙinsa na ƙarfe da ƙarfen ƙirjinsa. Sai sarki ya ce wa mai tuƙan keken yaƙi, “Juya ka fitar da ni daga wurin yaƙin. An ji mini rauni.”
But one [Syrian] soldier shot an arrow at Ahab, without knowing that it was Ahab. The arrow struck Ahab between the places where the parts of his armor joined together. Ahab told the driver of his chariot, “Turn the chariot around and take me out of here! I have been [severely] wounded!”
34 Duk yini yaƙi ya yi ta cin gaba, sarkin Isra’ila kuwa ya jingina kansa a cikin keken yaƙinsa yana duban Arameyawa har yamma. Sa’an nan a fāɗuwar rana sai ya mutu.
The battle continued all that day. Ahab was sitting propped up in his chariot, facing the Syrian soldiers. And late in the afternoon, when the sun was setting, he died.

< 2 Tarihi 18 >