< 2 Tarihi 18 >

1 Yanzu fa Yehoshafat ya wadace ƙwarai yana kuma da girma, ya kuma haɗa kansa da Ahab ta wurin aure.
And Jehoshaphat had riches and honor in abundance, and he intermarried with Achab.
2 Bayan’yan shekaru sai ya gangara don yă ziyarci Ahab a Samariya. Ahab kuwa ya yanka tumaki da shanu masu yawa dominsa da kuma mutanen da suke tare da shi, ya kuma lallashe shi yă yaƙi Ramot Gileyad.
And he went down after [some] years to Achab to Samaria. And Achab killed for him sheep and oxen in abundance, and for the people that were with him, and persuaded him to go up to Ramoth-gil'ad.
3 Ahab sarkin Isra’ila ya tambayi Yehoshafat sarkin Yahuda ya ce, “Za ka tafi tare da ni mu yaƙi Ramot Gileyad?” Yehoshafat ya amsa ya ce, “Ni kamar kai ne, kuma mutanena kamar naka ne; za mu tafi tare da kai a yaƙin.”
Then said Achab the king of Israel unto Jehoshaphat the king of Judah, Wilt thou go with me against Ramoth-gil'ad! And he said to him, I [will be] like thee, and my people [shall be] as thy people; and we will be with thee in the battle.
4 Amma Yehoshafat ya kuma ce wa sarkin Isra’ila, “Da fari mu nemi bishewar Ubangiji.”
And Jehoshaphat said unto the king of Israel, Inquire, I pray thee, today [first] of the word of the Lord.
5 Saboda haka sarkin Isra’ila ya tattara annabawa duka, mutane ɗari huɗu, ya kuma tambaye su, “Mu tafi yaƙi a kan Ramot Gileyad ko kada mu tafi?” Suka amsa “Tafi, gama Allah zai ba da shi cikin hannun sarki.”
Then did the king of Israel assemble the prophets, four hundred men, and said unto them, Shall we go to Ramoth-gil'ad to battle, or shall I forbear? And they said, Go up, and God will deliver [it] into the hand of the king.
6 Amma Yehoshafat ya yi tambaya ya ce, “Babu wani annabin Ubangiji a nan da za mu tambaya?”
And Jehoshaphat said, Is there not here a prophet of the Eternal besides, that we might inquire of him?
7 Sarki Isra’ila ya amsa wa Yehoshafat, “Akwai guda har yanzu mai suna Mikahiya ɗan Imla, za mu iya nemi nufin Ubangiji daga gare shi, sai dai ba na sonsa domin bai taɓa yin annabci wani abu mai kyau game da ni ba, sai kullum masifa.” Yehoshafat ya amsa ya ce, “Kada sarki yă faɗa haka.”
And the king of Israel said unto Jehoshaphat, There is yet one man, by whom we may inquire of the Lord; but I hate him; for he never prophesieth any good concerning me, but at all times evil: it is Michayhu the son of Yimla. And Jehoshaphat said, Let not the king say so.
8 Saboda haka sarkin Isra’ila ya kira ɗaya daga cikin ma’aikatansa ya ce, “A kawo Mikahiya ɗan Imla nan da nan.”
Then called the king of Israel a certain court-officer, and said, “Hasten hither Michayhu the son of Yimla.”
9 Saye da rigunan sarakuna, sarki Isra’ila da Yehoshafat sarkin Yahuda suna zaune a kan kujerunsu na mulki a masussuka ta ƙofar shigar Samariya, tare da dukan annabawa suna ta annabci a gabansu.
And the king of Israel and Jehoshaphat the king of Judah were sitting each on his throne, dressed in their royal garments, and they were sitting in a threshing-floor at the entrance of the gate of Samaria: and all the prophets prophesied before them.
10 To, fa, Zedekiya ɗan Kena’ana ya yi ƙahonin ƙarfe, ya kuma furta, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Da waɗannan za ka sassoki Arameyawa sai sun hallaka.’”
And Zedekiah the son of Kena'anah had made himself horns of iron; and he said, Thus hath said the Lord, With these shalt thou push the Syrians until thou have made an end of them.
11 Dukan sauran annabawan suka yi irin annabcin nan. Suka ce, “A haura zuwa Ramot Gileyad a yi nasara, gama Ubangiji zai ba da shi cikin hannun sarki.”
And all the prophets prophesied so, saying, Go up against Ramoth-gil'ad, and prosper, and the Lord will deliver it into the king's hand.
12 Ɗan saƙon da ya tafi don yă kawo Mikahiya kuwa ya ce masa, “Duba, kowannen a cikin annabawa ya yi faɗin nasara wa sarki. Don haka kai ma ka yi maganar da za tă gamshi sarki kamar yadda suka yi.”
And the messenger that went to call Michayhu spoke to him, saying, Behold, the words of the prophets are with one voice good for the king: so do let thy word, I pray thee, be like [that of] any one of them, and speak something good.
13 Amma Mikahiya ya ce, “Na rantse da ran Ubangiji, zan faɗa masa kawai abin da Allahna ya faɗa.”
And Michayhu said, As the Lord liveth, truly what my God may say, that will I speak.
14 Da suka iso, sarki ya tambaye shi, “Mika, mu tafi mu yaƙi Ramot Gileyad, ko kada mu tafi?” Ya amsa, “Kai masa yaƙi za ka kuwa yi nasara, gama za a ba da su a hannunka.”
And when he was come to the king, the king said unto him, Michah, shall we go to Ramoth-gil'ad to battle, or shall I forbear? And he said, Go ye up, and prosper, and may they be delivered into your hand.
15 Sarki ya ce masa, “Sau nawa zan sa ka rantse don ka faɗa gaskiya a cikin sunan Ubangiji?”
And the king said to him, How many times yet must I adjure thee that thou shalt not speak to me any thing but the truth in the name of the Lord?
16 Sa’an nan Mikahiya ya amsa, “Na ga dukan Isra’ila sun warwatsu a kan tuddai kamar tumakin da ba su da makiyaya, kuma Ubangiji ya ce, ‘Waɗannan mutane ba su da maigida. Bari kowanne yă tafi gida cikin salama.’”
Then said he, I saw all Israel scattered over the mountains, as flocks that have not a shepherd: and the Lord said, These have no master; let them return every man to his house in peace.
17 Sarkin Isra’ila ya ce wa Yehoshafat, “Ban faɗa maka cewa bai taɓa yin annabci wani abu mai kyau game da ni, in ba masifa ba?”
And the king of Israel said to Jehoshaphat, Did I not say unto thee that he would not prophesy concerning me any good, but [only] for evil?
18 Mikahiya ya ci gaba, “Saboda haka sai ka ji maganar Ubangiji. Na ga Ubangiji yana zama a kan kursiyinsa tare da dukan rundunar sama tsaye a damansa da hagunsa.
And he said, Therefore hear ye the word of the Lord: I saw the Lord sitting on his throne, and all the host of heaven standing on his right and his left.
19 Ubangiji kuwa ya ce, ‘Wa zai ruɗe Ahab sarki Isra’ila zuwa yaƙi da Ramot Gileyad da kuma zuwa mutuwarsa a can?’ “Wani ya ba da wata shawara, wani kuma wata dabam.
And the Lord said, Who will persuade Achab the king of Israel, that he may go up and fall at Ramoth-gil'ad? And one said—one saying after this manner, and another saying after that manner.
20 A ƙarshe, wani ruhu ya zo gaba, ya tsaya a gaban Ubangiji ya ce, ‘Zan ruɗe shi.’ “Ubangiji ya yi tambaya, ‘Ta wace hanya?’
Then came there forth a spirit, and placed himself before the Lord, and said, I will persuade him. And the Lord said unto him, Wherewith?
21 “Ya ce, ‘Zan tafi in zama ruhun ƙarya a bakunan dukan annabawansa.’ “Ubangiji ya ce, ‘Za ka yi nasara a ruɗinsa. Ka tafi, ka yi haka.’
And he said, I will go forth, and I will become a lying spirit in the mouth of all his prophets. And he said, Thou wilt persuade him, and also prevail: go forth, and do so.
22 “To yanzu, Ubangiji ya sa ruhun ruɗu a bakunan waɗannan annabawanka. Ubangiji ya ƙayyade masifa dominka.”
And now, behold, the Lord hath put a lying spirit in the mouth of these thy prophets: but the Lord hath spoken evil concerning thee.
23 Sai Zedekiya ɗan Kena’ana ya haura ya mari Mikahiya a fuska. Ya ce, “Ta wace hanya ce ruhun Ubangiji ya fita daga gare ni ya zo ya yi magana da kai?”
And Zedekiah the son of Kena'anah went near, and struck Michayhu on the cheek, and said, Which is the way the Spirit of the Lord passed away from me to speak with thee?
24 Mikahiya ya amsa ya ce, “Za ka gane a ranar da ka je ka ɓuya a can cikin ɗaki.”
And Michayhu said, Behold, thou shalt see it on that day when thou shalt go into the innermost chamber to hide thyself.
25 Sa’an nan sarkin Isra’ila ya umarta, “Ɗauki Mikahiya ku aika da shi zuwa ga Amon mai mulkin birni da kuma ga Yowash ɗan sarki,
And the king of Israel said, Take ye Michayhu, and carry him back unto Amon the governor of the city, and to Joash the king's son;
26 ku ce ga abin da sarki ya ce, ‘Ku jefa wannan mutum a kurkuku kada kuma ku ba shi wani abu sai dai burodi da ruwa har sai na dawo lafiya.’”
And say ye, Thus hath said the king, Put this man in the prison, and feed him with sparing bread and with sparing water, until I return in peace.
27 Mikahiya ya furta ya ce, “Idan har ka dawo lafiya, to, Ubangiji bai yi magana ta wurina ba.” Ya kuma ƙara da cewa, “Dukanku mutane, ku lura da maganata!”
And Michayhu said, If thou return at all in peace, then hath the Lord not spoken through me. And he said, Hear it, O all ye nations!
28 Saboda haka sarkin Isra’ila da Yehoshafat sarkin Yahuda suka haura zuwa Ramot Gileyad.
And the king of Israel went up with Jehoshaphat the king of Judah to Ramoth-gil'ad.
29 Sarkin Isra’ila ya ce wa Yehoshafat, “Zan ɓad da kama in shiga yaƙin, amma ka sa kayanka na sarauta.” Saboda haka sarkin Isra’ila ya ɓad da kama ya shiga cikin yaƙin.
And the king of Israel said unto Jehoshaphat, I will disguise myself, and enter into the battle; but do thou put on thy royal garments. And the king of Israel disguised himself, and they went into the battle.
30 To, fa, sarkin Aram ya umarce shugabannin keken yaƙinsa ya ce, “Kada ku yaƙi kowa, ƙarami ko babba, sai dai sarkin Isra’ila.”
And the king of Syria had commanded the captains of the chariots that he had, saying, Fight ye not with the small or with the great, save only with the king of Israel alone.
31 Sa’ad da shugabannin kekunan yaƙi suka ga Yehoshafat, sai suka yi tsammani, “Wannan ne sarkin Isra’ila.” Saboda haka suka juya don su yaƙe shi, amma Yehoshafat ya yi ihu, Ubangiji kuma ya taimake shi. Allah ya janye su daga gare shi,
And it came to pass, when the captains of the chariots saw Jehoshaphat, that they said, This is the king of Israel. And they encompassed him to fight; and Jehoshaphat cried out, and the Lord helped him; and God induced them to go away from him.
32 gama sa’ad da shugabannin keken yaƙi suka ga cewa ba shi ne sarkin Isra’ila ba, sai suka daina binsa.
And it came to pass, when the captains of the chariots perceived that it was not the king of Israel, that they turned back from following him.
33 Amma wani ya harba kibiya haka kawai, sai kibiyar ta sami sarki Ahab na Isra’ila a kafaɗa tsakanin rigar yaƙinsa na ƙarfe da ƙarfen ƙirjinsa. Sai sarki ya ce wa mai tuƙan keken yaƙi, “Juya ka fitar da ni daga wurin yaƙin. An ji mini rauni.”
But a certain man drew his bow at a venture, and struck the king of Israel between the joints and the armor: wherefore he said to the chariot-driver, Turn about, and carry me out of the camp; for I am wounded.
34 Duk yini yaƙi ya yi ta cin gaba, sarkin Isra’ila kuwa ya jingina kansa a cikin keken yaƙinsa yana duban Arameyawa har yamma. Sa’an nan a fāɗuwar rana sai ya mutu.
And the battle increased on that day: and the king of Israel stayed [himself] up in the chariot against the Syrians until the evening, and he died at the time of the sun's going down.

< 2 Tarihi 18 >