< 2 Tarihi 16 >
1 A shekara ta talatin da shida ta mulkin Asa, Ba’asha sarkin Isra’ila ya haura don yă yaƙi Yahuda da Rama mai katanga, don kuma yă hana wani daga fita ko shiga yankin Asa sarkin Yahuda.
Yahuda Kralı Asa'nın krallığının otuz altıncı yılında İsrail Kralı Baaşa Yahuda'ya saldırmaya hazırlanıyordu. Asa'nın topraklarına giriş çıkışı engellemek amacıyla, Rama Kenti'ni güçlendirmeye başladı.
2 Sai Asa ya ɗauki azurfa da zinariya daga ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma na fadansa ya aika wa Ben-Hadad sarkin Aram, wanda yake mulki a Damaskus.
Bunun üzerine Asa, RAB'bin Tapınağı'nın ve sarayın hazinelerindeki altın ve gümüşü çıkararak şu haberle birlikte Şam'da oturan Aram Kralı Ben-Hadat'a gönderdi:
3 Ya ce, “Bari yarjejjeniya ta kasance tsakani na da kai kamar yadda ya kasance tsakanin mahaifina da mahaifinka. Dubi ina aika maka azurfa da zinariya. Yanzu ka yanke yarjejjeniya da Ba’asha sarkin Isra’ila domin yă janye daga gare ni.”
“Babamla baban arasında olduğu gibi seninle benim aramızda da bir antlaşma olsun. Sana gönderdiğim bu altınlara, gümüşlere karşılık, sen de İsrail Kralı Baaşa ile yaptığın antlaşmayı boz, topraklarımdan askerlerini çeksin.”
4 Ben-Hadad ya yarda da Sarki Asa ya kuma aika da manyan hafsoshin mayaƙansa a kan garuruwan Isra’ila. Suka ci Iyon, Dan, Abel-Mayim da kuma dukan biranen ajiya na Naftali.
Kral Asa'nın önerisini kabul eden Ben-Hadat, ordu komutanlarını İsrail kentlerinin üzerine gönderdi. İyon'u, Dan'ı, Avel-Mayim'i, Naftali'nin bütün ambarlı kentlerini ele geçirdiler.
5 Da Ba’asha ya ji wannan, ya daina ginin Rama ya yashe aikinsa.
Baaşa bunu duyunca Rama'nın yapımını durdurup işe son verdi.
6 Sa’an nan Sarki Asa ya kawo dukan mutanen Yahuda, suka kuma kwashe duwatsu da katako daga Rama waɗanda Ba’asha yake amfani da su. Da su ne Asa ya gina Geba da Mizfa.
Kral Asa bütün Yahudalılar'ı çağırttı; Baaşa'nın Rama'nın yapımında kullandığı taşlarla keresteleri alıp götürdüler. Asa bunlarla Geva ve Mispa kentlerini onardı.
7 A lokacin Hanani mai duba ya zo wurin Asa sarkin Yahuda ya ce masa, “Don ka dogara ga sarkin Aram, ba kuwa ga Ubangiji Allahnka ba ne mayaƙan sarkin Aram sun kuɓuce daga hannunka.
O sırada Bilici Hanani Yahuda Kralı Asa'ya gelip şöyle dedi: “Tanrın RAB'be güveneceğine Aram Kralı'na güvendin. Bu yüzden Aram Kralı'nın ordusu elinden kurtuldu.
8 Ai, Kushawa da Libiyawa rundunar sojoji ne masu yawan gaske, suna kuma da kekunan yaƙi da mahayan dawakai masu yawa ƙwarai. Amma duk da haka, saboda ka dogara ga Ubangiji, ya kuwa ba da su cikin hannunka.
Kûşlular'la Luvlular, çok sayıda savaş arabaları, atlılarıyla büyük bir ordu değil miydiler? Ama sen RAB'be güvendin, O da onları eline teslim etti.
9 Gama gaban Ubangiji yana ko’ina a duniya don yă ƙarfafa waɗanda zukatansu suke binsa cikin aminci. Ka yi wauta, daga yanzu nan gaba za ka yi ta yaƙi.”
RAB'bin gözleri bütün yürekleriyle kendisine bağlı olanlara güç vermek için her yeri görür. Akılsızca davrandın. Bundan böyle hep savaş içinde olacaksın.”
10 Sai Asa ya yi fushi sosai da mai duban saboda wannan; ya yi fushi ƙwarai har ya sa aka jefa shi a kurkuku. A lokaci guda kuma Asa ya fara gwada wa mutane azaba.
Asa biliciye öfkelenip onu cezaevine attırdı. Çünkü söyledikleri onu kızdırmıştı. Halktan bazı kişilere de baskı yaptı.
11 Ayyukan mulkin Asa, daga farko zuwa ƙarshe, suna a rubuce a littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
Asa'nın yaptığı işler, başından sonuna dek, Yahuda ve İsrail krallarının tarihinde yazılıdır.
12 A shekara ta talatin da tara ta mulkinsa, Asa ya kamu da wata cuta a ƙafarsa. Ko da yake cutar ta yi tsanani, duk d haka ma a cikin ciwonsa bai nemi taimako daga Ubangiji ba, sai dai daga likitoci.
Asa, krallığının otuz dokuzuncu yılında ayaklarından hastalandı. Durumu çok ağırdı. Hastalığında RAB'be yöneleceğine hekimlere başvurdu.
13 Sa’an nan a shekara ta arba’in da ɗaya ta mulkinsa, Asa ya mutu ya kuma huta tare da kakanninsa.
Asa krallığının kırk birinci yılında ölüp atalarına kavuştu.
14 Suka binne shi a kabarin da ya fafe wa kansa a Birnin Dawuda. Suka sa shi a makara wadda aka rufe da kayan yaji da kuma turare dabam-dabam da aka niƙa, suka kuma ƙuna babbar wuta don girmama shi.
Onu özel olarak hazırlanmış, güzel kokulu çeşit çeşit baharat dolu bir sedyeye yatırarak Davut Kenti'nde kendisi için yaptırdığı mezara gömdüler. Onuruna çok büyük bir ateş yaktılar.