< 2 Tarihi 16 >
1 A shekara ta talatin da shida ta mulkin Asa, Ba’asha sarkin Isra’ila ya haura don yă yaƙi Yahuda da Rama mai katanga, don kuma yă hana wani daga fita ko shiga yankin Asa sarkin Yahuda.
Mais à l’année trente-sixième de son règne, Baasa, roi d’Israël, monta en Juda, et environna d’un mur Rama, afin que nul du royaume d’Asa ne pût sûrement sortir et entrer.
2 Sai Asa ya ɗauki azurfa da zinariya daga ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma na fadansa ya aika wa Ben-Hadad sarkin Aram, wanda yake mulki a Damaskus.
Asa prit donc de l’argent et de l’or des trésors de la maison du Seigneur, et des trésors du roi, et envoya à Bénadad, roi de Syrie, qui habitait à Damas, disant:
3 Ya ce, “Bari yarjejjeniya ta kasance tsakani na da kai kamar yadda ya kasance tsakanin mahaifina da mahaifinka. Dubi ina aika maka azurfa da zinariya. Yanzu ka yanke yarjejjeniya da Ba’asha sarkin Isra’ila domin yă janye daga gare ni.”
Il y a une alliance entre moi et vous; mon père aussi et le vôtre ont entretenu la concorde; c’est pourquoi je vous ai envoyé de l’argent et de l’or, afin que, rompant l’alliance que vous avez faite avec Baasa, roi d’Israël, vous l’obligiez à s’éloigner de moi.
4 Ben-Hadad ya yarda da Sarki Asa ya kuma aika da manyan hafsoshin mayaƙansa a kan garuruwan Isra’ila. Suka ci Iyon, Dan, Abel-Mayim da kuma dukan biranen ajiya na Naftali.
Cette nouvelle reçue, Bénadad envoya les princes de ses armées contre les villes d’Israël, lesquels frappèrent Ahion, et Dan, et Abelmaïm, et toutes les villes de Nephthali murées.
5 Da Ba’asha ya ji wannan, ya daina ginin Rama ya yashe aikinsa.
Lorsque Baasa l’eut appris, il cessa de bâtir Rama, et interrompit son ouvrage.
6 Sa’an nan Sarki Asa ya kawo dukan mutanen Yahuda, suka kuma kwashe duwatsu da katako daga Rama waɗanda Ba’asha yake amfani da su. Da su ne Asa ya gina Geba da Mizfa.
Or le roi Asa prit tout Juda avec lui, et ils enlevèrent les pierres de Rama et les bois qu’avaient préparés Baasa pour bâtir, et il en bâtit Gabaa et Maspha.
7 A lokacin Hanani mai duba ya zo wurin Asa sarkin Yahuda ya ce masa, “Don ka dogara ga sarkin Aram, ba kuwa ga Ubangiji Allahnka ba ne mayaƙan sarkin Aram sun kuɓuce daga hannunka.
En ce temps-là, Hanani, le prophète, vint vers Asa, roi de Juda, et lui dit: Parce que vous avez eu confiance dans le roi de Syrie, et non dans le Seigneur votre Dieu, c’est pourquoi l’armée du roi de Syrie s’est échappée de votre main.
8 Ai, Kushawa da Libiyawa rundunar sojoji ne masu yawan gaske, suna kuma da kekunan yaƙi da mahayan dawakai masu yawa ƙwarai. Amma duk da haka, saboda ka dogara ga Ubangiji, ya kuwa ba da su cikin hannunka.
Est-ce que les Ethiopiens et les Libyens n’étaient pas beaucoup plus nombreux en quadriges, en cavaliers et en une multitude considérable? Et comme vous aviez cru au Seigneur, il les livra en votre main.
9 Gama gaban Ubangiji yana ko’ina a duniya don yă ƙarfafa waɗanda zukatansu suke binsa cikin aminci. Ka yi wauta, daga yanzu nan gaba za ka yi ta yaƙi.”
Car les yeux du Seigneur contemplent toute la terre, et ils donnent de la force à ceux qui d’un cœur parfait croient en lui. Vous avez donc agi follement, et à cause de cela dès à présent des guerres s’élèveront contre vous.
10 Sai Asa ya yi fushi sosai da mai duban saboda wannan; ya yi fushi ƙwarai har ya sa aka jefa shi a kurkuku. A lokaci guda kuma Asa ya fara gwada wa mutane azaba.
Mais Asa, irrité contre le Voyant, commanda qu’il fût mis dans les chaînes; car il avait été très indigné de ses paroles; et il tua en ce temps-là un grand nombre de personnes d’entre le peuple.
11 Ayyukan mulkin Asa, daga farko zuwa ƙarshe, suna a rubuce a littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
Or les actions d’Asa, les premières et les dernières, sont écrites dans le Livre des rois de Juda et d’Israël.
12 A shekara ta talatin da tara ta mulkinsa, Asa ya kamu da wata cuta a ƙafarsa. Ko da yake cutar ta yi tsanani, duk d haka ma a cikin ciwonsa bai nemi taimako daga Ubangiji ba, sai dai daga likitoci.
Asa fut aussi malade, la trente-neuvième année de son règne, d’une douleur aux pieds très violente, et dans son infirmité il ne chercha point le Seigneur; mais il se confia davantage en l’art des médecins.
13 Sa’an nan a shekara ta arba’in da ɗaya ta mulkinsa, Asa ya mutu ya kuma huta tare da kakanninsa.
Et il dormit avec ses pères; et il mourut l’an quarante et unième de son règne.
14 Suka binne shi a kabarin da ya fafe wa kansa a Birnin Dawuda. Suka sa shi a makara wadda aka rufe da kayan yaji da kuma turare dabam-dabam da aka niƙa, suka kuma ƙuna babbar wuta don girmama shi.
Et on l’ensevelit dans son sépulcre qu’il s’était creusé dans la cité de David; et on le mit sur son lit rempli d’aromates et d’essences de femme de mauvaise vie, composées selon l’art des parfumeurs, et on les brûla sur lui en très grand appareil.