< 2 Tarihi 16 >

1 A shekara ta talatin da shida ta mulkin Asa, Ba’asha sarkin Isra’ila ya haura don yă yaƙi Yahuda da Rama mai katanga, don kuma yă hana wani daga fita ko shiga yankin Asa sarkin Yahuda.
Forsothe in the sixe and thrittithe yeer of his rewme Baasa, the kyng of Israel, stiede in to Juda, and cumpasside Rama with a wal, that no man of the rewme of Asa myyte go out ether entre sikirli.
2 Sai Asa ya ɗauki azurfa da zinariya daga ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma na fadansa ya aika wa Ben-Hadad sarkin Aram, wanda yake mulki a Damaskus.
Sotheli Asa brouyte forth gold and siluer fro the tresours of the hows of the Lord, and fro the kyngis tresouris; and sente to Benadab, kyng of Sirie, that dwellide in Damask,
3 Ya ce, “Bari yarjejjeniya ta kasance tsakani na da kai kamar yadda ya kasance tsakanin mahaifina da mahaifinka. Dubi ina aika maka azurfa da zinariya. Yanzu ka yanke yarjejjeniya da Ba’asha sarkin Isra’ila domin yă janye daga gare ni.”
and seide, Boond of pees is bitwixe me and thee, and my fadir and thi fadir hadden acordyng; wherfor Y sente to thee siluer and gold, that whanne thou hast broke the boond of pees, which thou hast with Baasa, king of Israel, thou make hym to go awei fro me.
4 Ben-Hadad ya yarda da Sarki Asa ya kuma aika da manyan hafsoshin mayaƙansa a kan garuruwan Isra’ila. Suka ci Iyon, Dan, Abel-Mayim da kuma dukan biranen ajiya na Naftali.
And whanne this was foundun, Benadab sente princes of hise oostis to the citees of Israel, whiche smytiden Ahion, and Dan, and Abelmaym, and alle the wallid citees of Neptalym.
5 Da Ba’asha ya ji wannan, ya daina ginin Rama ya yashe aikinsa.
And whanne Baasa hadde herd this, he ceesside to bilde Rama, and left his werk.
6 Sa’an nan Sarki Asa ya kawo dukan mutanen Yahuda, suka kuma kwashe duwatsu da katako daga Rama waɗanda Ba’asha yake amfani da su. Da su ne Asa ya gina Geba da Mizfa.
Forsothe kyng Asa took al Juda, and thei token fro Rama the stonys and trees, whiche Baasa hadde maad redi to bildyng; and he bildide of tho Gabaa, and Maspha.
7 A lokacin Hanani mai duba ya zo wurin Asa sarkin Yahuda ya ce masa, “Don ka dogara ga sarkin Aram, ba kuwa ga Ubangiji Allahnka ba ne mayaƙan sarkin Aram sun kuɓuce daga hannunka.
In that tyme Anany, the profete, cam to Asa, kyng of Juda, and seide to hym, For thou haddist trist in the kyng of Sirie, and not in `thi Lord God, herfor the oost of `the kyng of Sirie aschapide fro thin hond.
8 Ai, Kushawa da Libiyawa rundunar sojoji ne masu yawan gaske, suna kuma da kekunan yaƙi da mahayan dawakai masu yawa ƙwarai. Amma duk da haka, saboda ka dogara ga Ubangiji, ya kuwa ba da su cikin hannunka.
Whether `Ethiopiens and Libiens weren not many mo in charis, and knyytis, and ful greet multitude; whiche whanne thou haddist bileuyd to the Lord, he bitook in to thin hondis?
9 Gama gaban Ubangiji yana ko’ina a duniya don yă ƙarfafa waɗanda zukatansu suke binsa cikin aminci. Ka yi wauta, daga yanzu nan gaba za ka yi ta yaƙi.”
For the iyen of the Lord biholden al the erthe, and yyuen strengthe to hem, that with perfit herte bileuen in to hym. Therfor thou hast do folili, and for this, yhe, in present tyme batels schulen rise ayens thee.
10 Sai Asa ya yi fushi sosai da mai duban saboda wannan; ya yi fushi ƙwarai har ya sa aka jefa shi a kurkuku. A lokaci guda kuma Asa ya fara gwada wa mutane azaba.
And Asa was wrooth ayens the prophete, and comaundide hym to be sent in to stockis. Forsothe the Lord hadde indignacioun greetli on this thing, and killide ful many of the puple in that tyme.
11 Ayyukan mulkin Asa, daga farko zuwa ƙarshe, suna a rubuce a littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
Sotheli the firste and the laste werkis of Asa ben writun in the book of kyngis of Juda and of Israel.
12 A shekara ta talatin da tara ta mulkinsa, Asa ya kamu da wata cuta a ƙafarsa. Ko da yake cutar ta yi tsanani, duk d haka ma a cikin ciwonsa bai nemi taimako daga Ubangiji ba, sai dai daga likitoci.
Forsothe Asa was sijk ful gretli in the akynge of feet, in the nyne and thrittithe yeer of his rewme; and nether in his sikenesse he souyte the Lord, but tristide more in the craft of lechis.
13 Sa’an nan a shekara ta arba’in da ɗaya ta mulkinsa, Asa ya mutu ya kuma huta tare da kakanninsa.
And Asa slepte with hise fadris, and he was deed in the oon and fourtithe yeer of his rewme.
14 Suka binne shi a kabarin da ya fafe wa kansa a Birnin Dawuda. Suka sa shi a makara wadda aka rufe da kayan yaji da kuma turare dabam-dabam da aka niƙa, suka kuma ƙuna babbar wuta don girmama shi.
And thei birieden him in his sepulcre, which he hadde maad to hym silf in the cytee of Dauid; and thei puttiden hym on his bed ful of swete smellynge spices and oynementis of hooris, that weren `maad togidere bi the craft of oynement makeris, and thei brenten on hym with ful greet cost.

< 2 Tarihi 16 >