< 2 Tarihi 16 >
1 A shekara ta talatin da shida ta mulkin Asa, Ba’asha sarkin Isra’ila ya haura don yă yaƙi Yahuda da Rama mai katanga, don kuma yă hana wani daga fita ko shiga yankin Asa sarkin Yahuda.
In the six-and-thirtieth year of the reign of Assa, came up Ba'sha the king of Israel against Judah, and built Kamah, in order not to suffer any one to go out or come in to Assa the king of Judah.
2 Sai Asa ya ɗauki azurfa da zinariya daga ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma na fadansa ya aika wa Ben-Hadad sarkin Aram, wanda yake mulki a Damaskus.
Then did Assa bring out silver and gold out of the treasuries of the house of the Lord and of the king's house, and sent [them] to Ben-hadad the king of Syria, who dwelt at Damascus, saying,
3 Ya ce, “Bari yarjejjeniya ta kasance tsakani na da kai kamar yadda ya kasance tsakanin mahaifina da mahaifinka. Dubi ina aika maka azurfa da zinariya. Yanzu ka yanke yarjejjeniya da Ba’asha sarkin Isra’ila domin yă janye daga gare ni.”
A covenant is between me and thee, as between my father and thy father: behold, I have sent unto thee silver and gold; go, break thy covenant with Ba'sha the king of Israel, that he may withdraw from me.
4 Ben-Hadad ya yarda da Sarki Asa ya kuma aika da manyan hafsoshin mayaƙansa a kan garuruwan Isra’ila. Suka ci Iyon, Dan, Abel-Mayim da kuma dukan biranen ajiya na Naftali.
And Ben-hadad hearkened unto king Assa, and sent the captains of the armies that he had against the cities of Israel, and they smote 'Iyon, and Dan, and Abel-mayim, and all the treasure-cities of Naphtali.
5 Da Ba’asha ya ji wannan, ya daina ginin Rama ya yashe aikinsa.
And it came to pass, when Ba'sha heard this, that he left off the building of Ramah, and stopped his work.
6 Sa’an nan Sarki Asa ya kawo dukan mutanen Yahuda, suka kuma kwashe duwatsu da katako daga Rama waɗanda Ba’asha yake amfani da su. Da su ne Asa ya gina Geba da Mizfa.
And king Assa took then all Judah; and they carried away the stones of Ramah, and its timber, wherewith Ba'sha had built; and he built therewith Geba' and Mizpah.
7 A lokacin Hanani mai duba ya zo wurin Asa sarkin Yahuda ya ce masa, “Don ka dogara ga sarkin Aram, ba kuwa ga Ubangiji Allahnka ba ne mayaƙan sarkin Aram sun kuɓuce daga hannunka.
And at that time came Chanani the seer to Assa the king of Judah, and said unto him, Because thou hast relied on the king of Syria, and hast not relied on the Lord thy God: therefore is the army of the king of Syria escaped out of thy hands.
8 Ai, Kushawa da Libiyawa rundunar sojoji ne masu yawan gaske, suna kuma da kekunan yaƙi da mahayan dawakai masu yawa ƙwarai. Amma duk da haka, saboda ka dogara ga Ubangiji, ya kuwa ba da su cikin hannunka.
Were not the Ethiopians and the Lubim a numerous army, with chariots and horsemen in great abundance? yet, because thou didst rely on the Lord, he gave them up into thy hand.
9 Gama gaban Ubangiji yana ko’ina a duniya don yă ƙarfafa waɗanda zukatansu suke binsa cikin aminci. Ka yi wauta, daga yanzu nan gaba za ka yi ta yaƙi.”
For as regardeth the Lord, his eyes roam throughout the whole earth, to hold strongly with those whose heart is entire toward him: thou hast done foolishly for this reason; because from this time forth there will be wars with thee.
10 Sai Asa ya yi fushi sosai da mai duban saboda wannan; ya yi fushi ƙwarai har ya sa aka jefa shi a kurkuku. A lokaci guda kuma Asa ya fara gwada wa mutane azaba.
Then became Assa incensed toward the seer, and put him in a prison-house; for he was in a rage with him because of this. And Assa oppressed some of the people at the same time.
11 Ayyukan mulkin Asa, daga farko zuwa ƙarshe, suna a rubuce a littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
And, behold, the acts of Assa, the first and the last, lo, they are written in the book of the kings of Judah and Israel.
12 A shekara ta talatin da tara ta mulkinsa, Asa ya kamu da wata cuta a ƙafarsa. Ko da yake cutar ta yi tsanani, duk d haka ma a cikin ciwonsa bai nemi taimako daga Ubangiji ba, sai dai daga likitoci.
And Assa became sick in the thirty-and-ninth year of his reign in his feet, his disease being exceedingly severe: yet even in his disease he sought not to the Lord, but [applied] to the physicians.
13 Sa’an nan a shekara ta arba’in da ɗaya ta mulkinsa, Asa ya mutu ya kuma huta tare da kakanninsa.
And Assa slept with his fathers, and died in the one-and-fortieth year of his reign.
14 Suka binne shi a kabarin da ya fafe wa kansa a Birnin Dawuda. Suka sa shi a makara wadda aka rufe da kayan yaji da kuma turare dabam-dabam da aka niƙa, suka kuma ƙuna babbar wuta don girmama shi.
And they buried him in his own sepulchres, which he had dug for himself in the city of David, and they laid him in the couch which was filled with sweet odors and divers kinds of spices mixed by the apothecary's art; and they made for him a burning uncommonly great.