< 2 Tarihi 16 >
1 A shekara ta talatin da shida ta mulkin Asa, Ba’asha sarkin Isra’ila ya haura don yă yaƙi Yahuda da Rama mai katanga, don kuma yă hana wani daga fita ko shiga yankin Asa sarkin Yahuda.
Léta třidcátého šestého kralování Azova vytáhl Báza král Izraelský proti Judovi, a stavěl Ráma, aby nedal vyjíti ani jíti k Azovi králi Judskému.
2 Sai Asa ya ɗauki azurfa da zinariya daga ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma na fadansa ya aika wa Ben-Hadad sarkin Aram, wanda yake mulki a Damaskus.
Tedy vzav Aza stříbro i zlato z pokladů domu Hospodinova i domu královského, poslal k Benadadovi králi Syrskému, kterýž bydlil v Damašku, řka:
3 Ya ce, “Bari yarjejjeniya ta kasance tsakani na da kai kamar yadda ya kasance tsakanin mahaifina da mahaifinka. Dubi ina aika maka azurfa da zinariya. Yanzu ka yanke yarjejjeniya da Ba’asha sarkin Isra’ila domin yă janye daga gare ni.”
Smlouva jest mezi mnou a mezi tebou, mezi otcem mým a mezi otcem tvým. Aj, posílámť teď stříbro a zlato, jdi, zruš smlouvu svou s Bázou králem Izraelským, ať odtrhne ode mne.
4 Ben-Hadad ya yarda da Sarki Asa ya kuma aika da manyan hafsoshin mayaƙansa a kan garuruwan Isra’ila. Suka ci Iyon, Dan, Abel-Mayim da kuma dukan biranen ajiya na Naftali.
I uposlechl Benadad krále Azy, a poslal knížata s vojsky svými proti městům Izraelským. I dobyli Jon a Dan, též Abelmaim i všech měst Neftalímových, v nichž měli sklady.
5 Da Ba’asha ya ji wannan, ya daina ginin Rama ya yashe aikinsa.
To když uslyšel Báza, přestal stavěti Ráma, a zanechal díla svého.
6 Sa’an nan Sarki Asa ya kawo dukan mutanen Yahuda, suka kuma kwashe duwatsu da katako daga Rama waɗanda Ba’asha yake amfani da su. Da su ne Asa ya gina Geba da Mizfa.
V tom Aza král pojal všecken lid Judský, a pobrali kamení z Ráma i dříví, z něhož stavěl Báza, a vystavěl z něho Gabaa a Masfa.
7 A lokacin Hanani mai duba ya zo wurin Asa sarkin Yahuda ya ce masa, “Don ka dogara ga sarkin Aram, ba kuwa ga Ubangiji Allahnka ba ne mayaƙan sarkin Aram sun kuɓuce daga hannunka.
V ten pak čas přišel Chanani prorok k Azovi králi Judskému, a řekl jemu: Že jsi zpolehl na krále Syrského, a nezpolehl jsi na Hospodina Boha svého, proto ušlo vojsko krále Syrského z ruky tvé.
8 Ai, Kushawa da Libiyawa rundunar sojoji ne masu yawan gaske, suna kuma da kekunan yaƙi da mahayan dawakai masu yawa ƙwarai. Amma duk da haka, saboda ka dogara ga Ubangiji, ya kuwa ba da su cikin hannunka.
Zdaliž jsou Chussimští a Lubimští neměli vojsk velmi velikých, s vozy a jezdci náramně mnohými? A když jsi zpolehl na Hospodina, vydal je v ruku tvou.
9 Gama gaban Ubangiji yana ko’ina a duniya don yă ƙarfafa waɗanda zukatansu suke binsa cikin aminci. Ka yi wauta, daga yanzu nan gaba za ka yi ta yaƙi.”
Oči zajisté Hospodinovy spatřují všecku zemi, aby dokazoval síly své při těch, kteříž jsou k němu srdce upřímého. Bláznivě jsi učinil v té věci, protož od toho času budou proti tobě války.
10 Sai Asa ya yi fushi sosai da mai duban saboda wannan; ya yi fushi ƙwarai har ya sa aka jefa shi a kurkuku. A lokaci guda kuma Asa ya fara gwada wa mutane azaba.
Tedy rozhněvav se Aza na proroka, dal ho do vězení; nebo se byl rozhněval na něj pro tu věc. A utiskal Aza některé z lidu toho času.
11 Ayyukan mulkin Asa, daga farko zuwa ƙarshe, suna a rubuce a littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
O jiných pak věcech Azových, prvních i posledních, zapsáno jest v knize o králích Judských a Izraelských.
12 A shekara ta talatin da tara ta mulkinsa, Asa ya kamu da wata cuta a ƙafarsa. Ko da yake cutar ta yi tsanani, duk d haka ma a cikin ciwonsa bai nemi taimako daga Ubangiji ba, sai dai daga likitoci.
Potom léta třidcátého devátého kralování svého nemocen byl Aza na nohy své těžkou nemocí, a však v nemoci své nehledal Boha, ale lékařů.
13 Sa’an nan a shekara ta arba’in da ɗaya ta mulkinsa, Asa ya mutu ya kuma huta tare da kakanninsa.
A tak usnul Aza s otci svými, a umřel léta čtyřidcátého prvního kralování svého.
14 Suka binne shi a kabarin da ya fafe wa kansa a Birnin Dawuda. Suka sa shi a makara wadda aka rufe da kayan yaji da kuma turare dabam-dabam da aka niƙa, suka kuma ƙuna babbar wuta don girmama shi.
A pochovali jej v hrobě jeho, kterýž byl vytesal sobě v městě Davidově, a položili ho na lůžku, kteréž byl naplnil vonnými věcmi a mastmi dílem apatykářským připravenými. I pálili to jemu ohněm velmi velikým.