< 2 Tarihi 15 >

1 Sai Ruhun Allah ya sauko a kan Azariya ɗan Oded.
And as for 'Azaryahu the son of 'Oded—on him came the spirit of God;
2 Ya fita ya je ya sadu da Asa ya kuma faɗa masa, “Ka saurare ni, Asa da kuma dukan Yahuda da Benyamin. Ubangiji yana tare da ku sa’ad da kuke tare da shi. In kuka neme shi, za ku same shi, amma in kuka yashe shi, zai yashe ku.
And he went out to meet Assa, and said unto him, Hear me, O Assa, and all Judah and Benjamin, The Lord is with you, while ye remain with him; and if ye seek him, he will let himself be found by you; but if ye forsake him, he will forsake you.
3 Tun da daɗewa Isra’ila ba su da Allah na gaskiya, babu firist da zai koyar, kuma babu doka.
And many days [had elapsed] for Israel, [they being] without the true God, and without a teaching priest, and without law.
4 Amma cikin wahalarsu suka juya ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, suka kuma neme shi, suka kuwa same shi.
But they returned when they were in distress unto the Lord, the God of Israel, and they sought him, and he let himself be found by them.
5 A waɗancan kwanaki akwai hatsari a yin tafiye-tafiye, gama dukan mazaunan ƙasashe suna cikin babbar damuwa.
And in those times there was no peace to him that went out, and to him that came in; but there were great confusions among all the inhabitants of the countries.
6 Wata ƙasa takan murƙushe wata, wani birni kuma yakan murƙushe wani, domin Allah ya wahalshe su da kowace irin damuwa.
And nation was dashed to pieces against nation, and city against city; for God did confound them with all kind of distress.
7 Amma game da ku, ku ƙarfafa kada ku fid da zuciya, gama za a ba ku ladan aikinku.”
But as for you, be ye strong, and let not your hands be weak; for there is a reward for your doing.
8 Sa’ad da Asa ya ji waɗannan kalmomin da annabcin Azariya ɗan Oded annabi ya faɗa, sai ya sami ƙarfi hali. Ya kawar da gumaka masu banƙyama daga dukan ƙasar Yahuda da Benyamin da kuma daga garuruwan da ya ci da yaƙi a ƙasar tudu ta Efraim. Ya gyaggyara bagaden Ubangiji da yake a gaban shirayin haikalin Ubangiji.
And when Assa heard these words, and the prophecy of 'Oded the prophet, he was strengthened, and he put away the abominable idols out of all the land of Judah and Benjamin, and out of the cities which he had captured from the mountain of Ephraim; and he renewed the altar of the Lord, that was before the porch of the Lord.
9 Sa’an nan ya tattara dukan Yahuda da Benyamin da kuma mutane daga Efraim, Manasse da Simeyon waɗanda suke zaune a cikinsu, gama jama’a mai girma ta zo wurinsa daga Isra’ila sa’ad da suka ga cewa Ubangiji Allahnsa yana tare da shi.
And he assembled all Judah and Benjamin, and those that sojourned with them out of Ephraim and Menasseh, and out of Simeon; for they had joined him out of Israel in abundance, when they saw that the Lord his God was with him.
10 Suka taru a Urushalima a wata na uku na shekara ta goma sha biyar ta mulkin Asa.
And so they assembled themselves at Jerusalem in the third month, in the fifteenth year of the reign of Assa.
11 A lokacin suka miƙa hadaya bijimai ɗari bakwai da tumaki da kuma awaki dubu bakwai ga Ubangiji daga ganimar da suka dawo da ita.
And they sacrificed unto the Lord on the same day, of the booty which they had brought, seven hundred oxen and seven thousand sheep.
12 Suka yi alkawari don su nemi Ubangiji Allah na kakanninsu, da dukan zuciyarsu da kuma dukan ransu.
And they entered into the covenant to seek the Lord the God of their fathers with all their heart and with all their soul;
13 Aka kashe dukan waɗanda ba su nemi Ubangiji, Allah na Isra’ila ba, ko ƙarami ko babba, namiji ko ta mace.
So that whosoever would not seek the Lord the God of Israel should be put to death, from the small even up to the great, whether it be man or woman.
14 Suka yi rantsuwa ga Ubangiji da babbar murya, da ihu da garayu da ƙahoni.
And they swore unto the Lord with a loud voice, and with [joyful] shouting, and with trumpets, and with cornets.
15 Dukan Yahuda suka yi farin ciki game da rantsuwar domin sun yi rantsuwar gabagadi. Suka nemi Allah da gaske, suka kuma same shi. Saboda haka Ubangiji ya ba su hutu a kowane gefe.
And all Judah rejoiced because of the oath; for with all their heart had they sworn, and with their whole desire did they seek him, and he let himself be found by them: and the Lord gave them rest on every side.
16 Sarki Asa ya tuɓe mahaifiyar mahaifiyarsa daga matsayinta na mahaifiyar sarauniya, domin ta gina ginshiƙin banƙyama na Ashera. Asa ya rurrushe shi, ya farfasa shi ya kuma ƙone shi a Kwarin Kidron.
And also concerning Ma'achah the mother of king Assa, he removed her from being queen, because she had made a scandalous image for the grove; and Assa cut down her scandalous image, and had it ground up, and burnt it by the brook Kidron.
17 Ko da yake bai kawar da masujadan kan tudu daga Isra’ila ba, zuciyar Asa ta cika da bin Ubangiji dukan kwanakinsa.
But the high-places were not removed out of Israel; nevertheless the heart of Assa was entire all his days.
18 Ya kawo azurfa da zinariya da kayayyaki a haikalin Allah waɗanda shi da mahaifinsa suka keɓe.
And be brought the things which his father had sanctified, and his own sanctified things, into the house of God, —silver, and gold, and vessels.
19 Ba a ƙara yin yaƙi ba sai a shekara ta talatin da biyar ta mulkin Asa.
And there was no war until the five-and-thirtieth year of the reign of Assa.

< 2 Tarihi 15 >