< 2 Tarihi 15 >

1 Sai Ruhun Allah ya sauko a kan Azariya ɗan Oded.
Guds Ånd kom over Azarja, Odeds Søn,
2 Ya fita ya je ya sadu da Asa ya kuma faɗa masa, “Ka saurare ni, Asa da kuma dukan Yahuda da Benyamin. Ubangiji yana tare da ku sa’ad da kuke tare da shi. In kuka neme shi, za ku same shi, amma in kuka yashe shi, zai yashe ku.
og han trådte frem for Asa og sagde til ham: "Hør mig, Asa og hele Juda og Benjamin! HERREN er med eder, når I er med ham; og hvis I søger ham, lader han sig finde af eder, men forlader I ham, forlader han også eder!
3 Tun da daɗewa Isra’ila ba su da Allah na gaskiya, babu firist da zai koyar, kuma babu doka.
I lange Tider var Israel uden sand Gud, uden Præster til at vejlede og uden Lov,
4 Amma cikin wahalarsu suka juya ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, suka kuma neme shi, suka kuwa same shi.
men i sin Trængsel omvendte det sig til HERREN, Israels Gud, og søgte ham, og han lod sig finde at dem.
5 A waɗancan kwanaki akwai hatsari a yin tafiye-tafiye, gama dukan mazaunan ƙasashe suna cikin babbar damuwa.
I de Tider kunde ingen gå ud og ind i Fred, thi der var vild Rædsel over alle Landes Indbyggere;
6 Wata ƙasa takan murƙushe wata, wani birni kuma yakan murƙushe wani, domin Allah ya wahalshe su da kowace irin damuwa.
Folk knustes mod Folk, By mod By, thi Gud bragte dem i vild Rædsel med alle mulige Trængsler.
7 Amma game da ku, ku ƙarfafa kada ku fid da zuciya, gama za a ba ku ladan aikinku.”
Men I, vær frimodige og lad ikke Hænderne synke, thi der er Løn for eders Gerning."
8 Sa’ad da Asa ya ji waɗannan kalmomin da annabcin Azariya ɗan Oded annabi ya faɗa, sai ya sami ƙarfi hali. Ya kawar da gumaka masu banƙyama daga dukan ƙasar Yahuda da Benyamin da kuma daga garuruwan da ya ci da yaƙi a ƙasar tudu ta Efraim. Ya gyaggyara bagaden Ubangiji da yake a gaban shirayin haikalin Ubangiji.
Da Asa hørte de Ord og den Profeti, tog han Mod til sig og fjernede de væmmelige Guder fra hele Judas og Benjamins Land og fra de Byer, han havde indtaget i Efraims Bjerge; oghan byggede påny HERRENs Alter foran HERRENs Forhal.
9 Sa’an nan ya tattara dukan Yahuda da Benyamin da kuma mutane daga Efraim, Manasse da Simeyon waɗanda suke zaune a cikinsu, gama jama’a mai girma ta zo wurinsa daga Isra’ila sa’ad da suka ga cewa Ubangiji Allahnsa yana tare da shi.
Så samlede han hele Juda og Benjamin og de Folk fra Efraim, Manasse og Simeon, der boede som fremmede hos dem; thi en Mængde Israeliter var gået over til ham, da de så, at HERREN hans Gud var med ham.
10 Suka taru a Urushalima a wata na uku na shekara ta goma sha biyar ta mulkin Asa.
De samledes i Jerusalem i den tredje Måned i Asas femtende Regeringsår
11 A lokacin suka miƙa hadaya bijimai ɗari bakwai da tumaki da kuma awaki dubu bakwai ga Ubangiji daga ganimar da suka dawo da ita.
og ofrede den Dag HERREN Ofre af Byttet, de havde medbragt, 700 Stykker Hornkvæg og 7000 Stykker Småkvæg.
12 Suka yi alkawari don su nemi Ubangiji Allah na kakanninsu, da dukan zuciyarsu da kuma dukan ransu.
Derpå sluttede de en Pagt om at søge HERREN, deres Fædres Gud, af hele deres Hjerte og hele deres Sjæl;
13 Aka kashe dukan waɗanda ba su nemi Ubangiji, Allah na Isra’ila ba, ko ƙarami ko babba, namiji ko ta mace.
og enhver, der ikke søgte HERREN, Israels Gud, skulde lide Døden, være sig lille eller stor, Mand eller Kvinde.
14 Suka yi rantsuwa ga Ubangiji da babbar murya, da ihu da garayu da ƙahoni.
Det tilsvor de HERREN med høj Røst under Jubel og til Trompeters og Horns Klang,
15 Dukan Yahuda suka yi farin ciki game da rantsuwar domin sun yi rantsuwar gabagadi. Suka nemi Allah da gaske, suka kuma same shi. Saboda haka Ubangiji ya ba su hutu a kowane gefe.
Og hele Juda glædede sig over den Ed, thi de svor af hele deres Hjerte og søgte ham af hele deres Vilje; og han lod sig finde af dem og lod dem få Ro til alle Sider.
16 Sarki Asa ya tuɓe mahaifiyar mahaifiyarsa daga matsayinta na mahaifiyar sarauniya, domin ta gina ginshiƙin banƙyama na Ashera. Asa ya rurrushe shi, ya farfasa shi ya kuma ƙone shi a Kwarin Kidron.
Kong Asa fratog endog sin Moder Ma'aka Værdigheden som Herskerinde, fordi hun havde ladet lave et Skændselsbillede til Ære for Asjera; Asa lod hendes Skændselsbillede nedbryde, sønderknuse og brænde i Kedrons Dal.
17 Ko da yake bai kawar da masujadan kan tudu daga Isra’ila ba, zuciyar Asa ta cika da bin Ubangiji dukan kwanakinsa.
Vel forsvandt Offerhøjene ikke af Israel, men alligevel var Asas Hjerte helt med HERREN, så længe han levede.
18 Ya kawo azurfa da zinariya da kayayyaki a haikalin Allah waɗanda shi da mahaifinsa suka keɓe.
Og han bragte sin Faders og sine egne Helliggaver ind i Guds Hus, Sølv, Guld og forskellige Kar.
19 Ba a ƙara yin yaƙi ba sai a shekara ta talatin da biyar ta mulkin Asa.
Der var ikke Krige føer efter Asas fem og tredivte Regeringsår.

< 2 Tarihi 15 >