< 2 Tarihi 15 >

1 Sai Ruhun Allah ya sauko a kan Azariya ɗan Oded.
Tada duh Božji dođe na Odedova sina Azarju.
2 Ya fita ya je ya sadu da Asa ya kuma faɗa masa, “Ka saurare ni, Asa da kuma dukan Yahuda da Benyamin. Ubangiji yana tare da ku sa’ad da kuke tare da shi. In kuka neme shi, za ku same shi, amma in kuka yashe shi, zai yashe ku.
On je izišao pred Asu i rekao mu: “Čujte me, Asa i sve Judino i Benjaminovo pleme! Jahve je s vama jer ste vi s njime; i ako ga budete tražili, naći ćete ga; ako li ga ostavite, i on će ostaviti vas.
3 Tun da daɗewa Isra’ila ba su da Allah na gaskiya, babu firist da zai koyar, kuma babu doka.
Dugo su Izraelci bili bez pravoga Boga i bez svećenika-učitelja i bez Zakona.
4 Amma cikin wahalarsu suka juya ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, suka kuma neme shi, suka kuwa same shi.
Kad su se u nevolji obratili Jahvi, Bogu Izraelovu, i stali ga tražiti, našli su ga.
5 A waɗancan kwanaki akwai hatsari a yin tafiye-tafiye, gama dukan mazaunan ƙasashe suna cikin babbar damuwa.
U ona vremena nitko nije mogao na miru ni izlaziti ni dolaziti, jer su veliki nemiri vladali među svim zemaljskim stanovnicima.
6 Wata ƙasa takan murƙushe wata, wani birni kuma yakan murƙushe wani, domin Allah ya wahalshe su da kowace irin damuwa.
Udarao je narod na narod, grad na grad, jer ih je Jahve smeo svakojakom nevoljom.
7 Amma game da ku, ku ƙarfafa kada ku fid da zuciya, gama za a ba ku ladan aikinku.”
Ali vi budite hrabri i neka vam ne klonu ruke, jer ima nagrada za vaša djela.”
8 Sa’ad da Asa ya ji waɗannan kalmomin da annabcin Azariya ɗan Oded annabi ya faɗa, sai ya sami ƙarfi hali. Ya kawar da gumaka masu banƙyama daga dukan ƙasar Yahuda da Benyamin da kuma daga garuruwan da ya ci da yaƙi a ƙasar tudu ta Efraim. Ya gyaggyara bagaden Ubangiji da yake a gaban shirayin haikalin Ubangiji.
Čuvši te riječi i proročku besjedu proroka Odeda, Asa se ohrabri i ukloni idolske gadove iz cijele Judine i Benjaminove zemlje i iz gradova koje je bio osvojio u Efrajimovoj gori. Obnovio je i Jahvin žrtvenik koji je bio pred Jahvinim trijemom.
9 Sa’an nan ya tattara dukan Yahuda da Benyamin da kuma mutane daga Efraim, Manasse da Simeyon waɗanda suke zaune a cikinsu, gama jama’a mai girma ta zo wurinsa daga Isra’ila sa’ad da suka ga cewa Ubangiji Allahnsa yana tare da shi.
Onda je skupio sve Judino i Benjaminovo pleme i došljake koji su bili kod njih od Efrajimova, Manašeova i Šimunova plemena, jer ih je mnogo prebjeglo k njemu od Izraelaca kad su vidjeli da je s njim Jahve, njegov Bog.
10 Suka taru a Urushalima a wata na uku na shekara ta goma sha biyar ta mulkin Asa.
I skupili su se u Jeruzalemu trećega mjeseca petnaeste godine Asina kraljevanja.
11 A lokacin suka miƙa hadaya bijimai ɗari bakwai da tumaki da kuma awaki dubu bakwai ga Ubangiji daga ganimar da suka dawo da ita.
Onoga su dana prinijeli Jahvi žrtve od plijena koji su dognali, sedam stotina goveda i sedam tisuća sitne stoke.
12 Suka yi alkawari don su nemi Ubangiji Allah na kakanninsu, da dukan zuciyarsu da kuma dukan ransu.
Zavjetovaše se da će tražiti Jahvu, Boga svojih otaca, svim srcem i svom dušom.
13 Aka kashe dukan waɗanda ba su nemi Ubangiji, Allah na Isra’ila ba, ko ƙarami ko babba, namiji ko ta mace.
A tko god ne bi tražio Jahvu, Izraelova Boga, da se pogubi, bio malen ili velik, čovjek ili žena.
14 Suka yi rantsuwa ga Ubangiji da babbar murya, da ihu da garayu da ƙahoni.
Zakleli su se Jahvi iza glasa i uz gromki poklik, uz trube i rogove.
15 Dukan Yahuda suka yi farin ciki game da rantsuwar domin sun yi rantsuwar gabagadi. Suka nemi Allah da gaske, suka kuma same shi. Saboda haka Ubangiji ya ba su hutu a kowane gefe.
Svi su se Judejci radovali zbog te zakletve jer su se iz svega srca zakleli i od sve su ga svoje volje tražili i našli ga. Jahve im je dao mir odasvud uokolo.
16 Sarki Asa ya tuɓe mahaifiyar mahaifiyarsa daga matsayinta na mahaifiyar sarauniya, domin ta gina ginshiƙin banƙyama na Ashera. Asa ya rurrushe shi, ya farfasa shi ya kuma ƙone shi a Kwarin Kidron.
I svoju mater Maaku ukloni kralj Asa s vlasti jer je bila načinila gada Ašeri. Asa je sasjekao njezina gada, satro ga i spalio u potoku Kidronu.
17 Ko da yake bai kawar da masujadan kan tudu daga Isra’ila ba, zuciyar Asa ta cika da bin Ubangiji dukan kwanakinsa.
Ali uzvišice nisu bile uklonjene iz Izraela. Ipak je Asino srce bilo privrženo Jahvi svega njegova života.
18 Ya kawo azurfa da zinariya da kayayyaki a haikalin Allah waɗanda shi da mahaifinsa suka keɓe.
Unio je u Dom Božji posvećene darove svoga oca i svoje: srebro i zlato i posuđe.
19 Ba a ƙara yin yaƙi ba sai a shekara ta talatin da biyar ta mulkin Asa.
Nije bilo rata sve do trideset i pete godine Asina kraljevanja.

< 2 Tarihi 15 >