< 2 Tarihi 14 >

1 Abiya kuwa ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda. Asa ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki, a zamaninsa kuma ƙasar ta zauna lafiya na shekara goma.
So Abijah slept with his fathers, and they buried him in the city of David, and Asa his son reigned in his stead, —in his days, the land rested ten years.
2 Asa ya yi abin da yake da kyau da kuma daidai a gaban Ubangiji Allahnsa.
And Asa did that which was good and that which was right, in the eyes of Yahweh his God;
3 Ya kawar da baƙin bagade da masujadai bisa tudu, ya farfashe keɓaɓɓun duwatsu, ya kuma sassare ginshiƙan Ashera.
and took away the foreign altars, and the high places, —and brake in pieces the pillars, and cut in twain the Sacred Stems;
4 Ya umarci Yahuda su nemi Ubangiji Allah na kakanninsu, su kuma yi biyayya da dokoki da kuma umarnansa.
and bade Judah seek Yahweh, God of their fathers, -and execute the law, and the commandment;
5 Ya kawar da masujadan kan tudu da bagadan turare a kowane gari a Yahuda, masarautar kuwa ta zauna lafiya a ƙarƙashinsa.
and removed from all the cities of Judah, the high places, and the sun-images, —and the kingdom became quiet before him.
6 Ya gina biranen katanga na Yahuda, da yake ƙasar tana zaman lafiya. Babu wanda yake yaƙi da shi a waɗannan shekaru, gama Ubangiji ya ba shi hutu.
And he built cities of defence, in Judah, —for the land had quiet, nor was there near him any war, in these years, because Yahweh had given him rest.
7 Ya ce wa Yahuda, “Bari mu gina waɗannan garuruwa mu sa katanga kewaye da su, da hasumiyoyi, ƙofofi da ƙyamare. Ƙasar har yanzu tamu ce domin mun nemi Ubangiji Allahnmu, mun neme shi ya kuwa ba mu hutu a kowane gefe.” Saboda haka suka gina suka kuma yi nasara.
Therefore said he to Judah, Let us build these cities, and let us surround them with walls and towers, doors and bars, while the land is yet before us, for we have sought Yahweh our God, we have sought him, and he hath given us rest on every side. So they built, and prospered.
8 Asa ya kasance da mayaƙa dubu ɗari uku daga Yahuda, kintsatse da manyan garkuwoyi da māsu, da kuma mayaƙa dubu ɗari biyu da dubu tamanin daga Benyamin, riƙe da ƙananan garkuwoyi da kuma baka. Dukan waɗannan jarumawa ne ƙwarai.
And it came to pass that, Asa, had a force bearing shield and spear, out of Judah, three hundred thousand, and, out of Benjamin, such as bare a buckler and trode a bow, two hundred and eighty thousand, —all these, were heroes of valour.
9 Zera mutumin Kush ya taka ya fita don yă yaƙe su da babban runduna da kuma kekunan yaƙi ɗari uku, ya kuma zo har Maresha.
Then came out against them Zerah the Ethiopian, with a force of a thousand thousand, and three hundred chariots, —and he came as far as Mareshah.
10 Asa ya fita don yă ƙara da shi, suka ja dāgā yaƙi a Kwarin Zefata kusa da Maresha.
And Asa went out to meet him, —and they set in array for battle, in the valley of Zaphonah, at Mareshah.
11 Sai Asa ya kira ga Ubangiji Allahnsa ya ce, “Ubangiji, babu wani kamar ka da zai taimaki marar ƙarfi a kan mai ƙarfi. Ka taimake mu, ya Ubangiji Allahnmu, gama mun dogara a gare ka, kuma a cikin sunanka muka fito don mu yaƙi wannan babbar runduna. Ya Ubangiji, kai ne Allahnmu; kada ka bar mutum yă yi nasara a kanka.”
Then Asa cried out unto Yahweh his God, and said, O Yahweh, it is, nothing with thee, to help whether with many or with such as have no strength. Help us, O Yahweh our God, for, on thee, do we lean, and, in thy name, have we come against this multitude, —O Yahweh! our God, thou art, let not, weak man, have power against thee.
12 Ubangiji fa ya bugi mutanen Kush a gaban Asa da Yahuda. Mutanen Kush suka gudu,
So Yahweh smote the Ethiopians, before Asa, and before Judah, —and the Ethiopians fled.
13 Asa kuwa da mayaƙansa suka bi su har Gerar. Mutanen Kush suka mutu a ranan nan har ba a iya ƙidaya, aka buge su a gaban Ubangiji da rundunansa. Mutanen Yahuda suka kwashi ganima sosai.
And Asa and the people that were with him pursued as far as to Gerar, and the Ethiopians fell, so that there was no way for them to recover, for they were routed before Yahweh, and before him host, —and they carried away exceeding much spoil.
14 Suka hallaka dukan ƙauyukan kewaye da Gerar, gama tsoron Ubangiji ya kama su. Suka kwashi ganima na dukan ƙauyukan nan, da yake akwai ganima sosai a can.
And they smote all the cities round shout Gerar, for the dread of Yahweh was upon them, —and they plundered all the cities, for, great plunder, was there in them.
15 Suka kuma yaƙi sansanin makiyaya suka kwashe tumaki da awaki da raƙuma. Suka koma Urushalima.
Moreover also, the tents of the cattle, they smote, —and carried off sheep in abundance, and camels, and returned to Jerusalem.

< 2 Tarihi 14 >